Sashe 6
Kyalkyalin Kauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Bayan sallan magrib gabaki dayansu mazan suka shigo gida duka yaran zuwa sukayi gaidasu banda Yasmeen da tana sallan magrib ta bingile da bacci danta bala’in gaji, anatse Baba yakalli Farida dake zaune kusada Ammi akan tabarma yace “ina Yasmeen”? Dan ita kadaine bata tsakar gidan, ahankali Farida tace “tayi bacci Baba” bai damu da abincin da aka kawomusu da zasu fara ci ba tashi yayi ahankali yakalli Yayanshi yace “ina zuwa Baffa ku faracin abincin” idan da sabo kowa na gidan yasaba da yanda Baba yake da yaran gidan ma gabaki daya bawai nashi kadaiba gyadamai kai kawai Baffa yayi, direct dakin yaran yawuce wanda shine atsakiya dakinsu wanda yakenan ciki da falo da bayin wanka da dakin Baffa shima ciki da falo da bayin wanka sai akama yara matan dakinsu awajen babban daki guda daya, da sallama chan kasa yadaga labule yashiga dakin, kwance yaga Yasmeen din akasa tai shane shane tana bacci ga hijabin datai salla dashi agefe babu hula akanta sai kitson kanta dakenan all back dayay tsufa amman gashin baki sidik sai uban tsawo tana shakan bacci, ahankali ya tsugunna akanta hannunshi yakai yadaura asaman kan goshinta jin jikinta ba zafi yasa ahankali yakai hannunshi yabugi kafadarta yace “Yasmeen Yasmeen” cikin bacci murya chan ciki tace “uhn Baba” dan shiru yayi yana kallonta saikuma ahankali yatashi gadonsu katon gaske dan su uku ke kwana adakin, wani zubin kuma Nana nazuwa tace ita wajen Anty Yasmeen zata kwana ba wajen Ammi ba sai su zama su hudu, hijabinta dake wajen Baba yadauka ya kakkabe gadon sannan yadawo yaduka yadagata ahankali yace “tashi kihau gado” cikin bacci yadagata tamike tsaye kana ganin yanda take kasan ta bala’in gaji dan har layi layi take kaman zata fadi da taimakonshi yasata akan gadon tana lumshe idanu cike da bacci sannan yakashe wutan dakin dayake kunne yawuce yafito tsakar gida daga Yaya har Hajjo kowa yabishi da kallo anamai harara ciki ciki itadai Ammi ko kallonshi batayiba dan sosai yau yabata mata rai, zama yayi wajen yayinshi yasa hannu suka cigaba da cin tuwon duk wanda zai shigo gidan saisun bashi sha’awa sabida yanda family suke three brothers da iyalansu suna zaune agidan da iyayensu suka bar musu da iyalansu zaman lafiya kuma kansu ahade.
Saida suka cinye tuwon sannan yakalli Yayan nashi anatse yace “Yaya gobe za’amini karin girma awajen aiki zan koma Commissioner of Police CP” duka gidan hatta Ammi saida takalleshi cikeda farin ciki yaran sukahau cewa “Baba Allah ya sanya alheri” murmushi yamusu yace “Ameen” su Yaya da Hajjo ma sukace “Allah sanya Alheri Allah tayaka riko” anatse yace “Ameen nagode” murmushi Baffa yayi yace “Alhamdulillah Alhamdulillah shi daman duk wanda yarike Allah haka Allah ke daukaka shi, mutane na yawan cewa ai duk Dan sandan da baya karban cin hanci baya kaiwa ko’ina, ko akasuwa idan ana hiran nan nakan cemusu uhm’uh kada suce haka, inada kani da tunda yashiga aikin yan sanda yau kimanin shekaru kusan sha takwas kenan daidai da cin hancin naira biyar baitaba karba ba kuma ahankali ahankali anata karamai girma gashi yau za’a nadaka CP maiyafi haka? Nan gaba saidai muji an maidaka IG gabaki dayama” Baffa yadanyi shiru tareda daukan ruwa ya kurba sannan anatse yace “a kullum ina fadamaka kowani matsayi kasamu arayuwan nan kayi amfani dashi wajen magance matsalolin al’umma gabaki daya, wajen yaki da rashin gaskiya da kafa gaskiya, wajen taiwakama addinin musulunci, wajen tsare hakkin dan adam da saman da zaman lafiya adoron kasa, ta hanyar kawo karshe sata, kidnapping, shaye shaye, fyade, kisan kai da sauransu, Allah ubangiji yabaka sa’a yakuma tayaka ruko sannan kasani wannan position din amana ce, karkaci amanan sabon seat din nan kaji Ibrahim” anatse Baba yace “naji Baffa nagode sosai” dafashi kanninshi mai binshi yayi Baba Karami wanda shine mijin Hajjo yace “Allah yatayaka riko Yaya” murmushi yayi yace “Ameen” tashi Baffa yayi yace “to kumu tashi mutafi masallaci, kukuma matan sai kuyi naku sallan” dan juyawa Baba yayi yakalli Ammi dake kallonshi cikeda farin ciki dauke kai tayi dasauri ganin sun hada ido dan haushin shi takeji wani kalan murmushi yayi yabi su Baffa suka wuce mosque batare dayace mata komiba.
As usual daman gidan ana sallan isha’i kowa ke shigewa daki dan yara anje school angaji, weekends ne dama yaran gidan basu cika bacci da wuri ba dan ranan baaje boko ba, Ammi na idar da salla tadauki Nanah datai bacci asaman gadonta tafito waje tashigo dakin su Yasmeen tagansu duka sun kwanta dudda ba bacci Sa’a da Farida keyi ba amman Yasmeen tadade da bacci, kwantar da Nana tayi tareda su tana kallon Yasmeen tace “kin gaji ba dole kiyi bacci ba cikin dare kya tashi kiyi ishan kukuma baraku kashe wutan bane” dasauri Sa’a dakejan lullubi tace “Ammi dan Allah kikasha mana” dan hararansu tayi sannan takashe musu tajawo musu kofan tafito tashiga nata dakin, maida kofan falon tayi tarufe sanan tashiga uwar dakinsu, dan matsakaicin bayinsu da wanda kadai ake aciki ta shiga ta watsa ruwa sannan tafito ta shirya cikin kayan bacci ta fesa yan turarukanta ta kwanta.
Saida suka cinye tuwon sannan yakalli Yayan nashi anatse yace “Yaya gobe za’amini karin girma awajen aiki zan koma Commissioner of Police CP” duka gidan hatta Ammi saida takalleshi cikeda farin ciki yaran sukahau cewa “Baba Allah ya sanya alheri” murmushi yamusu yace “Ameen” su Yaya da Hajjo ma sukace “Allah sanya Alheri Allah tayaka riko” anatse yace “Ameen nagode” murmushi Baffa yayi yace “Alhamdulillah Alhamdulillah shi daman duk wanda yarike Allah haka Allah ke daukaka shi, mutane na yawan cewa ai duk Dan sandan da baya karban cin hanci baya kaiwa ko’ina, ko akasuwa idan ana hiran nan nakan cemusu uhm’uh kada suce haka, inada kani da tunda yashiga aikin yan sanda yau kimanin shekaru kusan sha takwas kenan daidai da cin hancin naira biyar baitaba karba ba kuma ahankali ahankali anata karamai girma gashi yau za’a nadaka CP maiyafi haka? Nan gaba saidai muji an maidaka IG gabaki dayama” Baffa yadanyi shiru tareda daukan ruwa ya kurba sannan anatse yace “a kullum ina fadamaka kowani matsayi kasamu arayuwan nan kayi amfani dashi wajen magance matsalolin al’umma gabaki daya, wajen yaki da rashin gaskiya da kafa gaskiya, wajen taiwakama addinin musulunci, wajen tsare hakkin dan adam da saman da zaman lafiya adoron kasa, ta hanyar kawo karshe sata, kidnapping, shaye shaye, fyade, kisan kai da sauransu, Allah ubangiji yabaka sa’a yakuma tayaka ruko sannan kasani wannan position din amana ce, karkaci amanan sabon seat din nan kaji Ibrahim” anatse Baba yace “naji Baffa nagode sosai” dafashi kanninshi mai binshi yayi Baba Karami wanda shine mijin Hajjo yace “Allah yatayaka riko Yaya” murmushi yayi yace “Ameen” tashi Baffa yayi yace “to kumu tashi mutafi masallaci, kukuma matan sai kuyi naku sallan” dan juyawa Baba yayi yakalli Ammi dake kallonshi cikeda farin ciki dauke kai tayi dasauri ganin sun hada ido dan haushin shi takeji wani kalan murmushi yayi yabi su Baffa suka wuce mosque batare dayace mata komiba.
As usual daman gidan ana sallan isha’i kowa ke shigewa daki dan yara anje school angaji, weekends ne dama yaran gidan basu cika bacci da wuri ba dan ranan baaje boko ba, Ammi na idar da salla tadauki Nanah datai bacci asaman gadonta tafito waje tashigo dakin su Yasmeen tagansu duka sun kwanta dudda ba bacci Sa’a da Farida keyi ba amman Yasmeen tadade da bacci, kwantar da Nana tayi tareda su tana kallon Yasmeen tace “kin gaji ba dole kiyi bacci ba cikin dare kya tashi kiyi ishan kukuma baraku kashe wutan bane” dasauri Sa’a dakejan lullubi tace “Ammi dan Allah kikasha mana” dan hararansu tayi sannan takashe musu tajawo musu kofan tafito tashiga nata dakin, maida kofan falon tayi tarufe sanan tashiga uwar dakinsu, dan matsakaicin bayinsu da wanda kadai ake aciki ta shiga ta watsa ruwa sannan tafito ta shirya cikin kayan bacci ta fesa yan turarukanta ta kwanta.