← Book details Jiddatulkhair Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 89 OF 205

Sashe 89

Jiddatulkhair Complete Hausa Novel · about 6 min read

tace xata ci ya siya mata a eatry din da suka je sannan suka dawo gida, ta tafi bangaren Aunty shi kuma ya tafi dakinsa, bude kofar yayi ya tadda jiddah yanda ya barta, ya kulle kofar ya shiga bandaki yayi wanka ya fito ya sauya kayan jikinsa xuwa pajamas sannan ya kwanta.... Tun magrib Aunty ke ta neman Jiddah bayan wanke wanke ya taru amma bata ganta ba, har dakinsu Seeyama ta shiga ta tambayesu suka ce bata shigo ba, cikin dubara ta shiga bangaren Ummi nan ma bata ganta ba, kaf sai da ta xaga duk gidan har da leka kofar gida amma bata ga alamarta ba, wani abu ya dauke hankalinta ta ci gaba da harkar gabanta, sai wajen goma da wani abu ta farga har lkcn fa bata ga Jiddah ba, ta sake xagaye gidan ta koma dakinsu Seeyama da bangaren Ummi duk babu alamarta, mamaki ne ya cikata, to ko Abuturrab ya tafi da ita ne daxu da ya xo?? Wayarsa ta shiga kira xuciyarta na tafarfasa, Abuturrab dake kwance har ya fara bacci vibration din wayarsa ya tadasa, bude ido yyi a hankali ya jawo wayar, ya daga ya kai kunne ganin Aunty ce ke kiransa, daga daya bangaren tace "Abuturrab kana gidan nan ne?" Bin dakin yyi da kallo, lkci daya yace "Aa ina tare da Ahmad" Aunty tace "Au haba??" Yace "Ehh a nan xan kwana, da wani abu ne?" Ta girgixa kai tace "Aa tunda baka nan sai da safe kawai" Daga haka ta katse wayar tayi wani murmushi, dama so take ta ta66atar da cewar ba shi ya dauketa ba, addu'a ta shiga yi a ranta na cewar Allah yasa karawa gaba jiddah tayi kawai... Abuturrab ya kalli kasan carpet din dakin ya ga jiddah kwance ta gaji da kukan bacci ya dauketa, har ya koma ya kwanta ya mike ya bude press dinsa ya fiddo da xanin gado ya rufa mata sannan ya kwanta saman gado ya kashe wutan dakin. Karfe takwas din safe, Abuturrab ya gama shiryawa saboda Ahmad dake jiransa, babu abinda ya ta6a na breakfast da aka kawo masa ya bar ma Jiddah da ke bacci ya fita ya kulle kofar ya tafi da makullin, babu wanda ya lura da shi har ya bar gidan. Karfe tara da rabi Ummi ta shigo dakinsu Ramlah da frnds dinta tana kallon Ramlah tace "Wai Jiddah fa??" Ramlah tace "Na xata ta bi Umma, ai bata kwana gidan nan ba" Ummi tace "Umma kuma? Umma ta xo gidan nan ne jiya?" Shiru Ramlah tayi, Ummi ta juya ta fita taje gun su siyama su ma same reply da Ramlah ta bata suka bata, nan taji hankalinta ya fara tashi, Aunty ta samu, Aunty tace "Jiddah kuma?? Ai ni ban ma san tana gidan nan ba" Ummi ta juya ta koma bangarenta ta kira yar uwarta, bayan Umma ta daga Ummi tace "Ramlah.... Jidderh ta koma gidanki ne??" daga daya bangaren Umma tace "Jiddah?? Aa bata gidana" Katse wayar Ummi tayi ta ajiye da mamaki, Abuturrab ne ya fado mata, to ko jiya ya tafi da ita ne?? Hankalinta ya d'an kwanta tuna hakan da tayi, dialing numbersa tayi bayan ya daga tace "Ka dau matarka ne?" Abuturrab dake tare da Ahmad da wasu frnds dinsu ya d'an yi shiru, kunya yake ji yace mata ai tana dakinsa, kuma baya son ya daga mata hankali, don yana ce mata bai dau Jiddah ba hankalinta xai tashi sosai, ya d'an yi kasa da murya yace "Ehh Ummi" Tace "Sae ka kai ta ina??" shiru yyi bai ce komai ba, Ummi tace "Na lura da kai baka da kirki, baka da kara, ba kuma ka da hankali, Kawai ka dau yarinya kayi tafiyar ka da ita without anyone's knowledge, duk ka bi ka daga min hankali, are this stupid? yarinyar da kake ikirarin ka aura ba da son ranka ba kamar yanda kake raina ma kanka hankali, Don wllh ba ni kake raina ma hankali ba, a sannu abinda ka kulla xai bayyana, did u think i am happy and relaxed with this ur marriage idan ba xuciyar musulunci ba?? duk ina lura da take taken ka a kan yarinyar nan kuma ko kaffara baxan yi ba da gangan kaje ka aureta ka xo nan kana raina ma ubanka hankali ba ni ba, to bari kaji, daga yau dama kada ka sake kawo ta gidan nan balle ka min rashin kunya yanda ka so, kaje can ka xauna da matarka a gidanku na yafe xuwanku wajena, duk da dama tun bayan da kaje kayi auren ka ba xuwa gidan uban naka kake ba, so just remain in ur house with ur so called wife" Tana kai wa nan ta katse wayarta, Abuturrab ya ajiye wayar ya jinginar da kansa da kujera yana tunanin abinda yasa yanxu kowa ke tunanin da gangan yaje ya auri Jiddah kawai pretending yake right from day one of the incident, to me yasa kowa ke ganin haka bayan shi ba da gangan ya aurota ba, mikewa yayi ya fita daga dakin, Ahmad ya bi sa da kallo.... Karfe sha biyu saura Abuturrab ya isa gida, face cap ne a kansa don bai son gaida kowa, kansa a kasa har ya nufi bangarensa ya ciro makulli ya bude kofar, Jiddah ta mike daga kwancen da take, ya shigo ya kulle kofar, ya xauna gefen gado ya dau wayarsa ya shiga kiran Siyama, tana dagawa yace ta xo dakinsa yana jiranta, ba a dau lkci ba Siyama ta xo, ya mike ya bude mata kofa, ta shigo ta gaishesa, duk da mamakin da ta yi ganin Jiddah a dakin amma bata nuna ba, sai murmushi kawai tayi mata, yana kallonta babu yabo bbu fallasa yace "Kaya xa ki dauko mata da Jilbab with ur Nikab now...." Siyama tace "Toh" sannan ta fita, sai ga ta babu bata lkci ta kawo ma Jiddah ankon da xa su saka ranan da Hijab da nikab, ajiye mata tayi gefen gado sannan ta fita, Jiddah ta tashi ta dau kayan ta shiga bandaki ta saka, bayan ta gama sakawa ta fito rike da nikab din tana kallonsa a hankali tace "Ban iya sakawa ba" Ya wani daure fuska yace "A haka xa ki saka, ko waye xai sa maki??" Kokarin sa wa ta shiga yi amma ta kasa, mikewa yayi ya fixge nikab din, ta runtse ido a tunaninta dukanta xai yi, ya shiga daura mata nikab din, bude ido tayi suka hada ido, da sauri ta rufe nata, har ya gama daura mata nikab din, yace "Fita ki jirani wajen motana" Ba musu ta nufi kofa ta bude ta fita, har ta isa tsakar gida kanta na kasa ta fita kofar gida gun motarsa, ya fito dakinsa ya kulle sannan ya fita shi ma....
Chapter 89 · 0% Book details