← Book details Feeryal Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 52 OF 52

Sashe 52

Feeryal Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

Atsaye ta tadda Miemie abakin gat d'in Aunty, Miemie ta ce
"Wow kefa kullun kamar kara miki kyau akeyi, muje ko,
mtss hmm ga matar can Umma Karima nafito ina magana wa isa driver ya d'auko mota yakaimu anguwa,
shine ta fito wai yazo yajemata aika kamar batada driver da zaije mata aika ne,
zomuje drivern Ammah yakaimu."

Feeryal ta ce
"Kibari kawai naje na karb'o keyn motan Ammie'na sai nayi deriving namu,
sai dai amma zaki dinga nunamin hanya tunda bansaniba."
Miemie ta ce
"Too lallai ma Feeryal kin iya tuki ne?
ko so kike kije ki zubar damu a hanya."
Feeryal tayi murmushi sannan ta ce
"Na iya mana ni nake janmu na kaimu unguwa da Aunty Maryam."
ta juya tana kokarin komawa ciki,
sukaji horn a bayansu.
Miemie ta waiga tana fad'in
"Lah ya ajmal ne, muyake ma horn zomuje."
tajawo hannunta suka isa wajen motar.
Ajmal ya zuge gilashin motar ya dube su yana cewa "Miemie Feeryal inazuwa haka?."
Miemie tace
"Zamuje gyaran gashine Ya Ajmal."
Ajmal yace
"Kushiga muje na saukeku dama fita zanyi."
kafin yarufe baki Miemie tabude gaba tace
"Feeryal shiga muwuce."

Feeryal ta danyi jim tana dago kanta sai suka hada ido da Ajmal.
da sauri ta kawar da kai a hankali ta shige motar, Miemie kuma tashiga baya suka tafi.

Sunatafe Miemie tanata zuba surutu Feeryal kuwa nashiru dama ba gwanace wajen iya surutu ba.
jifa-jifa Ajmal yake dan satan kallonta,
harsuka isa wurin gyaran gashin,
Feeryal batace kalaba.
suna sauka a motar Ajmal yad'an leko ya ce
"Karfe nawa zaku gama?."
Miemie ta ce
"Bamu sani ba yai, sai yadda ta yiwu "
ya ce "Okay to idan kun gama ku kirani."
yaja motar yatafi.
suma suka wuce shagon gyaran gyashin.

Suna gamawa Miemie takirashi yazo yamayar dasu gida.
suna sauka amotar Feeryal ta dubeshi ta ce
Mungode."
yadan jijjiga kai tareda sakin murmushi yajuya da motansa zuwa site dinsu.
suma su Feeryal kowa tayi shashinsu bayan Miemie ta ce mata zata shigo anjima.

Feeryal nashiga ta tadda Aunty a parkour,
Aunty ta ce
"Har kun dawo."
ta ce Eh.
cikin sauri tawuce d'akin ta dan tana alla-alla taje tacire bra'n dake jikinta domin ba karamin takurata ya yi ba.
tana shiga tacire abayan dake jikinta ta dau towel ta d'aura tawuce bandaki.
tana shiga takunce towel ta ajiye,
tana kokarin zare bra'n,
sai ta d'an tsaya ta kasa kunne tayi shiru.
sai kuma da sauri ta janyo towel dinta ta d'aura, tafice da gudu tayi parlour.

ganin bata ga Aunty a parlour ba shige bedroom d'in ta.
Aunty dake kokarin shi ga bathroom ta ja ta tsaya ta ce
"Ke lafiyar ki meye na gudun har kin gama wankan?."
ta ce
"Ammie kamar kukan mage naji a bayin."
Aunty ta rike hab'a ta ce
"Kamane ina, bakiji ba dan shiririta kika fito."
cikin shagwab'a ta ce
"Ni kam Ammie tsoro nake ji bazan iya wankan a can ba."
Aunty ta dawo da baya tana fad'in
"To zo ki shiga kiyi wankan ki fito sai na shiga."
ta zauna bakin gado ita kuma Feeryal ta tura kofar bayin ta sa kanta ciki.
wani irin burki taja ya yin da tsikar jikinta ya wani irin tashi yarrr,
jikinta gaba d'aya ya d'auki b'ari
kar-kar-kar.........!

To masu karatu a nan na kawo karshen littafi na d'aya wanda tundaga farkonsa har karshensa Free ne.
idan ki-kana bukatar ci gaban labarin ka-ki biya naira 500 kacal domin samun cigaban sa.
tura ta wannan asusun
3170524141 Rashida Salihu first bank.
ko ki tuntub'e ni ta Whatsapp number ta
08034690723.

Idan har kina bibiyan litattafaina irin su
HAMDAH KARSASHI ALFARMA BAZAWARA CE'ITA
da da dai sauransu.
ina mai miki albishir da cewa
labarin FEERYAL ya kwan gabansu.
labari ne mai d'auke da sarkakiya cakwakiya murd'ad'd'iya.
ku dai ku biyo ni na warware muku zare da abawa.

Mommyn Twins ce Rasheedat S Director nake.
har kullum da ko yaushe ina godiya gareku masoyana.
Chapter 52 · 0% Book details