Sashe 21
Feeryal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Nan take waziri Kutub ya murza wata kambu, cikin dakika 1 aljani Tarmuzu ya bayyana, a gabansu ya zube bisa gwuiwowinsa yana fad'in
"Na amsa kira ya shugaba na."
sarki aljani Matip ya dube sa tare da cewa
"Daga yau aikin ku ya kare Chuchu da Chulu ne zasu cigaba daga inda kuka tsaya."
rusunar da kai ya yi yana cewa
"Mun d'auki tabbaci ya shugaba."
ya zaro wata kambun dake d'aure a hannunsa ya aje shi gaban shugaban nasu.
sannan ya mike ya koma cikin fadawan nan ya zauna.
sarki Matip ya dubi yara mata biyun nan dake gefen sa sannan ya ce
"Chuchu Chulu, kuje ku bayyana gare ta."
ai ko nan take suka b'ace.
Yau asabar babu makaranta, Feeryal tasha baccinta har wajen karfe goma kafin ta farka.
ta mike zaune tana mussuke idanunta tare da yin hamma.
fuska ta kwab'e zuwa yanzu tana jin yunwa.
cikin tsiririyar muryarta mai kama da na shagwab'a ta ce
"Ammie yunwa."
jin bataji motsin Ammien nata cikin d'akin ba, sai ta kuma ware idanunta sosai tana kokarin zamowa bakin gado.
Da d'an fuskar mamaki take kallon yara guda biyu tsaye cikin d'akin girmansu dai-dai da ita tsawonsu ma d'aya.
suma kuma ita suke kallo suna yi mata murmushi.
itama murmushin tayi musu, tana fad'in
"Laa ku suwaye ne ya sunan ku,
kunzo da Ammie'n ku ne, ina take tana gurin Ammie na, zaku kwana a gidan mu?."
ta joro musu tambayar tana washe baki.
Baki suka had'a wajen fad'in
"Mu kawayen ki ne, sunan mu Chuchu da Chulu,
bamuzo da Ammie'n mu ba mu kad'ai mukazo, idan kina so sai mu kwana a gidan ku idan kuma kince mu tafi zamu tafi, zakiyi wasa da mu?."
kai ta gyad'a tana cewa
"Har da Miemie ma zamuyi wasan, ku jirani Ammie na tayi min wanka nayi breakfast, zakuga Miemie ma tazo.
"Ke Feeryal da wa kike magana ko mafarki kike?."
cewar Aunty data sako kanta cikin d'akin, hab'a ta rike tana kallon Feeryal data rike kugu tana magana tana lankwasa gefe da gefe irin yaro yana jin dad'in abin da yake ko ya gani na burgewa.
"Ke Feeryal wai dama ba mafarki kike ba, da wa kika tsaya kina ta zuba uban zance haka, ko mirror kike wa magana?
ni da nake ta jiranki ki tashi kiyi wanka, taho maza muje kiyi wanka ki samu kiyi breakfast."
ta janyo hannunta suka nufi bayi.
Kafa tashiga bubbugawa tana fad'in
"Kar ku tafi ku jira ni bari Ammie na ta min wanka,
Ammie kiyi min da sauri zamuyi wasa ne."
Cak Aunty taja ta tsaya tare da waigowa tana bin cikin d'akin da kallo, bayan kayan dake cikin sa babu wani halitta mai numfashi ciki sai ita da Feeryal d'in.
"Ammie kiyi sauri ki min kinga sunzo da kayan wasa da yawa."
tayi maganar tana jijjiga hannun Aunty.
cikin yanayin soma shiga fargaba Aunty ta ce
"Feeryal babu kowa fa a nan sai ni da ke, a ina kika ga wasu har da kayan wasan?."
Baki ta cuno tana jan hannun Aunty ba tare da ta bata amsar tambayar ta ba, sai cewar da tayi.
"Ammie yi sauri kuma yunwa nake ji."
Aunty bata kuma kawo komai a ranta ba, sai tunanin shiririta ne kawai irin na yaro.
Tana gama mata wanka ita tariga Aunty fita a bayin, wanda kafin yau idan tayi mata wanka haka zata langwab'e sai ta d'auko ta ta fito da ita,
ta share mata jiki ta shafa mata mai takuma samata kaya.
dube-dube tashiga yi tana niman ta in da sabbin kawayen nata suke amma bata gansu cikin d'akin ba.
tana shirin fita parlour taje ta duba su ko suna can, Aunty ta fito ta ce
tazo ta sa mata kaya.
Aunty na gama shiryata tayi parlour da sauri, ganin basa nan ma sai ta b'ata fuska tare da cuno d'an karamin bakin ta gaba.
Aunty ta karaso in da take tana fad'in
"Zo muje dinning kiyi breakfast."
"Ammie sun tafi gidan su ne yau she zasu kuma zuwa?."
tayi maganar tana d'ago kanta sama tana duban Aunty.
"Wai su waye ne kam Feeryal?
babu fa wanda suka zo gidan nan, Miemie ma bata zo ba tukun, a ta ina kika gansu mebi mafarki kikayi, taho muje kici abinci."
ta janyo ta suka haura dinning.
Tana cikin yin breakfast d'in Miemie ta shigo da babyn wasan ta,
tana gamawa kuwa sukayi d'akin Feeryal d'in dan suyi wasa a can.
wannan d'akin sunan nata ne kawai amma bata kwana ciki da rana ne kad'ai yake da amfani da dare kuma guduwa take gun Ammie'n ta a can bedroom d'in Aunty take kwana.
Suna shiga bedroom d'in Feeryal ta waro ido tana fad'in
"Laaa dama nan kuka zo, shine baku jirani a bedroom d'in Ammie na nayi wanka ba,
ga Miemie tazo muyi wasa."
dariya duk sukayi mata.
d'aya daga cikin su ta ce
"Ai bazamu tafi ba tun da bamu sallame ki ba, idan kika ce mutafi sai mu tafi, mun jiraki a nan ne kizo muyi wasa."
Murmushi tayi tana jin dad'i tayi sabbin kawaye 'yan wasa.
ta dubi Miemie ta ce
"Miemie zauna muyi wasa da su a gwada girma da babyn mu da nasu wanne yafi girma."
Zama Miemie tayi bawai dan ta fahimci inda batun nata ya dosa ba, suka cigaba da wasa Feeryal tana yi tana magana da bada amsa ita kad'ai.
Miemie kam data gaji
ta mike ta d'au babynta ta kama hanyar fita daga d'akin tana fad'in
"Feeryal ni kam zanje garden nayi wasa ta a can ki zo mu je."
da sauri Feeryal ta mike tabi bayanta tana cewa
"Zo ki basu babyn shine zaki kwace a hannunsu, suna mata kitso."
Miemie kam tuni tayi waje daga d'akin dan bata fahimci abin da Feeryal d'in take nufi ba.
"Miemie ki tsaya ki basu aro ai idan suka gama wasan zasu baki."
tayi maganar tana rike babyn Miemie.
Aunty da ke zaune cikin parlour ta ce
" 'yan'matan Ammie rigima ko, ina naki babyn je ki d'auko mana, gobe zansa diraiba yakai Baba Rabi taje tayi miki shopping ta siyo miki wata tun da bakya son wancan d'in, babbama wanda tafi wannan;
zo abinki 'yammatan Ammie, zo mu zauna a nan."
Kafad'a ta make tare da cuno baki gaba ta ce
"Ammie kawaye na ne fa suke wasa da babyn ta shine ta kwace."
Ido Aunty ta zuba mata Miemie kam tayi waje abinta.
Gwuiwa a d'an sanyaye Aunty ta ce
"Wasu kawayen naki Feeryal?."
"Ba gasu can a d'aki ba shine Miemie ta hanasu abin wasa."
tayi narai-narai na ido zatayi kuka.
Aunty ta mike ta na fad'in
"Yaushe suka zo suna ta ina ko tare da Miemie suka zo."
kai ta girgiza tayi gaba Aunty ta bita a baya.
Daga bakin kofa Aunty ta tsaya tana raba ido cikin d'akin babu kowa, numfashi ta sauke ta ce
"Ina kawayen naki Feeryal ni banga kowa cikin d'akin nan ba."
"Ammie gasu nan baki gansu bane."
jiki a sanyaye Aunty ta girgiza kai tana fad'in
"Ban gansu ba Feeryal, ni banga kowa ba."
Juyowa tayi in da kayan wasan ta suke ta ce
"Ammie na wai bata ganku ba, ai bazata sa Baba Rabi ta siyo muku babban baby ba, Ammie ki ware idonki da yawa zaki gansu gasu nan."
ta yi nuni da hannunta.
sai kuma ta waro ido tana fad'in
"Ammie wai ke bakya ganin su inji wannan?."
takuma yin nuni da hannunta.
Zuwa yanzu jikin Aunty ya fara yin la'asar kai ta gyad'a
"Eh ni banga kowa ba, Feeryal ki dai na wasa babu kowa a nan taho mu tafi."
Aunty tayi waje da sauri zuciyar ta na d'an harbawa.
Daga inda take tsaye cikin parlour tana jiyo sautin maganar Feeryal, wanda yake nuni da tabbas akwai wanda ita take gani harkuma suke magana sakaninsu, wanda ita Aunty bata iya ji ko ganin su.........!
Mommyn Twince ce
🌺🌺 *FEERYAL* 🌺🌺
*NA*
*RASHEEDAT S DIRECTOR*
( _Book 1_)
*~Free page~*
*_Littafin na kud'i ne 500 account no 3170524141 Rashida Salihu first bank ka-ki tura shaidar biya ta WhatsApp number ta 08034690723_*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'SâœðŸ?*
*🇦SSOCIATIONðŸ¤ðŸ»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇ðŸ»
https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association
*____________________________________*
🅿�10
Kamar wasa Feeryal ta b'ata tsawon lokaci cikin d'aki, Aunty na zaune a parlour tana jiyo ta tana ta surutu can anjima kuma ta kwashe da dariya.
shiru Aunty tayi da tunani fal cikin ranta.
"Anya Feeryal bata sami matsala ba kuwa?."
tayi wa kanta da kanta tambayar.
me yake kuma shirin faruwa ne bayan lokaci mai tsayo da aka d'auka bata kara ganin wani sauyi tare da ita ba sai yanzu?.
wani b'ari na zuciyar ta ya shiga karanto mata.
"Kar dai ace sai da ta barki kika sakankance da ita kafin ta ke son nuna miki asalinta."
Da sauri tayi kokarin kawar da wad'annan tunanin ta mike ta nufi kichin, tana sawa ranta kawai wasa ce da shiririta irin na yaro.
ta sami Baba Rabi suka cigaba da aiki.
Wasa gaske Feeryal ta share awanni uku tana wasa.
lokaci zuwa lokaci Aunty take zuwa ta leka ko zataga 'yan wasan nata,
amma wayam bata ganin kowa.
yoghurt da cake kad'ai ta fitowa ta d'auka ta ce wa Aunty zasuje suci su sha da kawayenta.
ita dai Aunty to kawai ta bita da shi.
ganin batada niyyar barin abin da takeyi bare ma harta fito ta ni mi abinci, Aunty ta tako bakin kofar ta leko tana fad'in
"Feeryal ya isa haka wasan taso kizo kiyi wanka ki ci abinci lokacin wanka ya yi."
Fuska ta b'ata ta cuno baki gaba
"Ammie wasa fa mukeyi."
kai Aunty ta dafe
"Oh Allah
ki ce da kawayen naki suma suje suyi wanka, kuma kar su dawo,
sai gobe, maza taso kizo muje."
Feeryal ta juya tana kallon wani gefe sannan ta ce
"Kuma kuje ayi muku wanka nima Ammie na zatayi min."
murmushi ta sake sai kuma ta d'aga hannu tana bye-bye.
sai da ta daina ganin su kafin ta sauke hannunta.
"Na amsa kira ya shugaba na."
sarki aljani Matip ya dube sa tare da cewa
"Daga yau aikin ku ya kare Chuchu da Chulu ne zasu cigaba daga inda kuka tsaya."
rusunar da kai ya yi yana cewa
"Mun d'auki tabbaci ya shugaba."
ya zaro wata kambun dake d'aure a hannunsa ya aje shi gaban shugaban nasu.
sannan ya mike ya koma cikin fadawan nan ya zauna.
sarki Matip ya dubi yara mata biyun nan dake gefen sa sannan ya ce
"Chuchu Chulu, kuje ku bayyana gare ta."
ai ko nan take suka b'ace.
Yau asabar babu makaranta, Feeryal tasha baccinta har wajen karfe goma kafin ta farka.
ta mike zaune tana mussuke idanunta tare da yin hamma.
fuska ta kwab'e zuwa yanzu tana jin yunwa.
cikin tsiririyar muryarta mai kama da na shagwab'a ta ce
"Ammie yunwa."
jin bataji motsin Ammien nata cikin d'akin ba, sai ta kuma ware idanunta sosai tana kokarin zamowa bakin gado.
Da d'an fuskar mamaki take kallon yara guda biyu tsaye cikin d'akin girmansu dai-dai da ita tsawonsu ma d'aya.
suma kuma ita suke kallo suna yi mata murmushi.
itama murmushin tayi musu, tana fad'in
"Laa ku suwaye ne ya sunan ku,
kunzo da Ammie'n ku ne, ina take tana gurin Ammie na, zaku kwana a gidan mu?."
ta joro musu tambayar tana washe baki.
Baki suka had'a wajen fad'in
"Mu kawayen ki ne, sunan mu Chuchu da Chulu,
bamuzo da Ammie'n mu ba mu kad'ai mukazo, idan kina so sai mu kwana a gidan ku idan kuma kince mu tafi zamu tafi, zakiyi wasa da mu?."
kai ta gyad'a tana cewa
"Har da Miemie ma zamuyi wasan, ku jirani Ammie na tayi min wanka nayi breakfast, zakuga Miemie ma tazo.
"Ke Feeryal da wa kike magana ko mafarki kike?."
cewar Aunty data sako kanta cikin d'akin, hab'a ta rike tana kallon Feeryal data rike kugu tana magana tana lankwasa gefe da gefe irin yaro yana jin dad'in abin da yake ko ya gani na burgewa.
"Ke Feeryal wai dama ba mafarki kike ba, da wa kika tsaya kina ta zuba uban zance haka, ko mirror kike wa magana?
ni da nake ta jiranki ki tashi kiyi wanka, taho maza muje kiyi wanka ki samu kiyi breakfast."
ta janyo hannunta suka nufi bayi.
Kafa tashiga bubbugawa tana fad'in
"Kar ku tafi ku jira ni bari Ammie na ta min wanka,
Ammie kiyi min da sauri zamuyi wasa ne."
Cak Aunty taja ta tsaya tare da waigowa tana bin cikin d'akin da kallo, bayan kayan dake cikin sa babu wani halitta mai numfashi ciki sai ita da Feeryal d'in.
"Ammie kiyi sauri ki min kinga sunzo da kayan wasa da yawa."
tayi maganar tana jijjiga hannun Aunty.
cikin yanayin soma shiga fargaba Aunty ta ce
"Feeryal babu kowa fa a nan sai ni da ke, a ina kika ga wasu har da kayan wasan?."
Baki ta cuno tana jan hannun Aunty ba tare da ta bata amsar tambayar ta ba, sai cewar da tayi.
"Ammie yi sauri kuma yunwa nake ji."
Aunty bata kuma kawo komai a ranta ba, sai tunanin shiririta ne kawai irin na yaro.
Tana gama mata wanka ita tariga Aunty fita a bayin, wanda kafin yau idan tayi mata wanka haka zata langwab'e sai ta d'auko ta ta fito da ita,
ta share mata jiki ta shafa mata mai takuma samata kaya.
dube-dube tashiga yi tana niman ta in da sabbin kawayen nata suke amma bata gansu cikin d'akin ba.
tana shirin fita parlour taje ta duba su ko suna can, Aunty ta fito ta ce
tazo ta sa mata kaya.
Aunty na gama shiryata tayi parlour da sauri, ganin basa nan ma sai ta b'ata fuska tare da cuno d'an karamin bakin ta gaba.
Aunty ta karaso in da take tana fad'in
"Zo muje dinning kiyi breakfast."
"Ammie sun tafi gidan su ne yau she zasu kuma zuwa?."
tayi maganar tana d'ago kanta sama tana duban Aunty.
"Wai su waye ne kam Feeryal?
babu fa wanda suka zo gidan nan, Miemie ma bata zo ba tukun, a ta ina kika gansu mebi mafarki kikayi, taho muje kici abinci."
ta janyo ta suka haura dinning.
Tana cikin yin breakfast d'in Miemie ta shigo da babyn wasan ta,
tana gamawa kuwa sukayi d'akin Feeryal d'in dan suyi wasa a can.
wannan d'akin sunan nata ne kawai amma bata kwana ciki da rana ne kad'ai yake da amfani da dare kuma guduwa take gun Ammie'n ta a can bedroom d'in Aunty take kwana.
Suna shiga bedroom d'in Feeryal ta waro ido tana fad'in
"Laaa dama nan kuka zo, shine baku jirani a bedroom d'in Ammie na nayi wanka ba,
ga Miemie tazo muyi wasa."
dariya duk sukayi mata.
d'aya daga cikin su ta ce
"Ai bazamu tafi ba tun da bamu sallame ki ba, idan kika ce mutafi sai mu tafi, mun jiraki a nan ne kizo muyi wasa."
Murmushi tayi tana jin dad'i tayi sabbin kawaye 'yan wasa.
ta dubi Miemie ta ce
"Miemie zauna muyi wasa da su a gwada girma da babyn mu da nasu wanne yafi girma."
Zama Miemie tayi bawai dan ta fahimci inda batun nata ya dosa ba, suka cigaba da wasa Feeryal tana yi tana magana da bada amsa ita kad'ai.
Miemie kam data gaji
ta mike ta d'au babynta ta kama hanyar fita daga d'akin tana fad'in
"Feeryal ni kam zanje garden nayi wasa ta a can ki zo mu je."
da sauri Feeryal ta mike tabi bayanta tana cewa
"Zo ki basu babyn shine zaki kwace a hannunsu, suna mata kitso."
Miemie kam tuni tayi waje daga d'akin dan bata fahimci abin da Feeryal d'in take nufi ba.
"Miemie ki tsaya ki basu aro ai idan suka gama wasan zasu baki."
tayi maganar tana rike babyn Miemie.
Aunty da ke zaune cikin parlour ta ce
" 'yan'matan Ammie rigima ko, ina naki babyn je ki d'auko mana, gobe zansa diraiba yakai Baba Rabi taje tayi miki shopping ta siyo miki wata tun da bakya son wancan d'in, babbama wanda tafi wannan;
zo abinki 'yammatan Ammie, zo mu zauna a nan."
Kafad'a ta make tare da cuno baki gaba ta ce
"Ammie kawaye na ne fa suke wasa da babyn ta shine ta kwace."
Ido Aunty ta zuba mata Miemie kam tayi waje abinta.
Gwuiwa a d'an sanyaye Aunty ta ce
"Wasu kawayen naki Feeryal?."
"Ba gasu can a d'aki ba shine Miemie ta hanasu abin wasa."
tayi narai-narai na ido zatayi kuka.
Aunty ta mike ta na fad'in
"Yaushe suka zo suna ta ina ko tare da Miemie suka zo."
kai ta girgiza tayi gaba Aunty ta bita a baya.
Daga bakin kofa Aunty ta tsaya tana raba ido cikin d'akin babu kowa, numfashi ta sauke ta ce
"Ina kawayen naki Feeryal ni banga kowa cikin d'akin nan ba."
"Ammie gasu nan baki gansu bane."
jiki a sanyaye Aunty ta girgiza kai tana fad'in
"Ban gansu ba Feeryal, ni banga kowa ba."
Juyowa tayi in da kayan wasan ta suke ta ce
"Ammie na wai bata ganku ba, ai bazata sa Baba Rabi ta siyo muku babban baby ba, Ammie ki ware idonki da yawa zaki gansu gasu nan."
ta yi nuni da hannunta.
sai kuma ta waro ido tana fad'in
"Ammie wai ke bakya ganin su inji wannan?."
takuma yin nuni da hannunta.
Zuwa yanzu jikin Aunty ya fara yin la'asar kai ta gyad'a
"Eh ni banga kowa ba, Feeryal ki dai na wasa babu kowa a nan taho mu tafi."
Aunty tayi waje da sauri zuciyar ta na d'an harbawa.
Daga inda take tsaye cikin parlour tana jiyo sautin maganar Feeryal, wanda yake nuni da tabbas akwai wanda ita take gani harkuma suke magana sakaninsu, wanda ita Aunty bata iya ji ko ganin su.........!
Mommyn Twince ce
🌺🌺 *FEERYAL* 🌺🌺
*NA*
*RASHEEDAT S DIRECTOR*
( _Book 1_)
*~Free page~*
*_Littafin na kud'i ne 500 account no 3170524141 Rashida Salihu first bank ka-ki tura shaidar biya ta WhatsApp number ta 08034690723_*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'SâœðŸ?*
*🇦SSOCIATIONðŸ¤ðŸ»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇ðŸ»
https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association
*____________________________________*
🅿�10
Kamar wasa Feeryal ta b'ata tsawon lokaci cikin d'aki, Aunty na zaune a parlour tana jiyo ta tana ta surutu can anjima kuma ta kwashe da dariya.
shiru Aunty tayi da tunani fal cikin ranta.
"Anya Feeryal bata sami matsala ba kuwa?."
tayi wa kanta da kanta tambayar.
me yake kuma shirin faruwa ne bayan lokaci mai tsayo da aka d'auka bata kara ganin wani sauyi tare da ita ba sai yanzu?.
wani b'ari na zuciyar ta ya shiga karanto mata.
"Kar dai ace sai da ta barki kika sakankance da ita kafin ta ke son nuna miki asalinta."
Da sauri tayi kokarin kawar da wad'annan tunanin ta mike ta nufi kichin, tana sawa ranta kawai wasa ce da shiririta irin na yaro.
ta sami Baba Rabi suka cigaba da aiki.
Wasa gaske Feeryal ta share awanni uku tana wasa.
lokaci zuwa lokaci Aunty take zuwa ta leka ko zataga 'yan wasan nata,
amma wayam bata ganin kowa.
yoghurt da cake kad'ai ta fitowa ta d'auka ta ce wa Aunty zasuje suci su sha da kawayenta.
ita dai Aunty to kawai ta bita da shi.
ganin batada niyyar barin abin da takeyi bare ma harta fito ta ni mi abinci, Aunty ta tako bakin kofar ta leko tana fad'in
"Feeryal ya isa haka wasan taso kizo kiyi wanka ki ci abinci lokacin wanka ya yi."
Fuska ta b'ata ta cuno baki gaba
"Ammie wasa fa mukeyi."
kai Aunty ta dafe
"Oh Allah
ki ce da kawayen naki suma suje suyi wanka, kuma kar su dawo,
sai gobe, maza taso kizo muje."
Feeryal ta juya tana kallon wani gefe sannan ta ce
"Kuma kuje ayi muku wanka nima Ammie na zatayi min."
murmushi ta sake sai kuma ta d'aga hannu tana bye-bye.
sai da ta daina ganin su kafin ta sauke hannunta.