Sashe 10
Feeryal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani zabgegen maciji tagani sakankanin kafafuwanta, a kanannad'e acure guri guda ya fasa kai.
takuma yin baya a muguwar razane,
da karfi ta furta "Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un!."
cikin tsananin kad'uwa.
tana furta kalmar innalillahi da sauri macijin ya shiga ware jikinsa yana bi ta kan kafafun Feeryal da ke zaune tana wasa da shi, yanufi kofa yana isa dai-dai bakin kofa ta nime shi ko sama ko kasa ya b'ace mata bat bata kuma ganinsa ba,
bata kuma san ta in da ya bi ba dan kofar a rufe take.
Rasashi ke da wuya tasoma jin wani kara mai cike da amon sauti na dukar can cikin kunnuwanta.
da karfi ta rumtse ido tare da kai hannu cikin kunnenta da take ji kamar dodon kunnuwan nata zasu zazzago su fito waje.
ji tayi ana fad'in
"Ke kad'ai bazaki iya bata kariya ba dole sai da taimakon muuuu!."
kuma toshe kunnuwanta tayi da karfi tana juyi had'e da tangad'i har sai da ta zube kasa.
a dai-dai lokacin da taji kamar an fisge mata dodon kunne, nan da nan wani uban zufa ya shiga keto mata.
a hankali kuma taji yanayin ya d'auke cak cikin second 1 tadawo dai-dai.
Da sauri ta mike zaune tashi ja da baya tana bin Feeryal da kallon tsaro.
ita ko yarinyar baki ta b'are tana mika mata hanu alamun ta d'auke ta.
Cikin rawar murya Aunty tashiga fad'in
"Ban tab'a cutar da ke ba, ban d'auko ki dan na cutar da ke ba,
sai dan na taimake ki, ki dubi girman Allah kada ki cutar da ni,
zan mai da ke in da na d'auko ki,
nayi zaton ke d'in jinsin mu ne shiyasa na d'auko ki, ban d'auko ki dan na cutar da ke ba!."
Gaba d'aya Aunty ta birkice ta ko ta ina a jikinta b'ari yake, tsoro mai tsanani ya baibaye ta.
ta kasa iya mikewa kan jafafunta sai ja da baya take a zaune.
Jin karar bud'e kofa ta waigo da sauri a bala'in razane, dan tagama zaton macijin ne ya dawo.
ganin Daddy ne ya shigo da sauri ta mike a guje tayi gurin shi,
ta fad'a jikin shi ta kankameshi da karfi tana fad'in
"Daddy maciji na ganshi da ido na! dan Allah ka d'auke ta ka mai da ita in da muka d'auko ta,
wlh nahakura zanci cigaba da zama a haka gara na tabbata a matsayin juya, na hakura bana son d'a zanyi rayuwa ta ni kad'ai a haka!."
Da sauri yadad'a rukota sosai ganin yadda gaba d'aya ta fita hayyacin ta.
ya janyo ta suka karaso cikin parlour, ya zauna kan kujera tare da zaunar da ita a gefen sa.
"Fad'imatu."
ya kira sunan ta yana kallon fuskarta.
ido ta zuba masa sai kuma ta girgiza kanta kamar wacce ke son dawowa hayyacin ta.
ta yunkura zata mike da sauri ya ruko ta yakuma duban ta da kyau ya ce
"Ki dawo hayyacin ki."
wani nannauyan numfashi ta sauke da sauri ta waiga gefe da gefen ta sai kuma ta maida duban ta gareshi.
"Fad'imatu." yakuma kiran sunan ta
murya a raunace.
kai ta girgiza ta ce
"Daddy."
"Numfashi ya fesar sannan yakuma rukota da kyau ya ce
"A ina kika ga macijin Fad'imatu? akaf fad'in gidan nan da kewayen sa, ba macijiba ko kwaro in har mai cutar wa ne bai isa ya matso yankin gidan nan ba, ta ko wane kusurwa;
tazarar taku dubu ne ta ko wata kusurwa sakanin mu da duk wani nau'in kwaro mai cutar wa,
ko ta sama ko ta kasa,
sam maciji bazai iya shigowa gidan nan ba, a zagaye gidan nan yake da maganin su,
idan kuwa sukayi gigin shiga to kuwa zasu mutu tun kan su karaso,
koda ta cikin karkashin k'asa ne kuwa."
"Daddy na ganshi da ido na fa babba ne sosai agaban Feeryal tana wasa da shi, kuma naji ana magana da karfi kamar za'a fasa min kunne,
ni dai a maida ita kawai wlh na hakura."
shiru ya yi yana kallonta a kasan ransa yake fad'in
"Anya ba aljanu ne ke son shafarta ba?."
kwana biyu gaba d'aya yaga yanayin ta ya sauya, abin da bazai faruba tarika cewa ya faru.
kai ya jinjina sannan ya ce
"Gizo ne kawai."
da sauri ta ce "A'a Daddy wannan kam ba gizo bane nagani da ido na da gaske ne."
"D'azu bakya hayyacin ki Fad'imatu akwai abin da ke shirin faruwa da ke, yakamata a dakile faruwar hakan,
ina zuwa."
Yafad'a yana mikewa ya nufi bedroom yafito d'auke da Alkur'ani mai girma ya dawo in da take, ya bud'e ya mika mata.
ya ce "Kirika karantawa ina zuwa, bari naje na dawo, dan shi yafi komai kariya."
Ya isa ya d'auki Feeryal data fara kuka ya ajeta a gefenta.
yana cewa
"Ta gaji da zamane ko tana jin yunwa."
ido ta bita da shi harga Allah tsoro take bata yanzu.
Cikin hanzari yafita, Daddy yakai awa d'aya zuwa d'aya da rabi kafin ya dawo.
a bedroom ya same su dan ta sami kwarin gwuiwa da taimakon karanta Alkur'anin da tayi, har ta ji karfin zuciya ta d'auke ta ta je tamata wanka, tana gama shiryata kuwa tayi bacci.
Daddy ya mika mata kullin laidar daya shigo da shi.
ta karb'i laidar tana d'an jujjuyashi a hannunta sai kuma ta kunce laidar.
da mamaki take kallon kulli-kullin magunguna.
da fuskar tambaya ta dube shi,
sai kuma taga ya d'au abin saka kuraren wuta ya jona shi gijin wuta,
yana fad'in
"Hayaki ne da wanka na karb'o miki, zo maza kiyi hayakin anjima in zaki kwanta kiyi wankan maganin sai ki kara yin hayakin."
"Hayaki da wanka kuma? asabo da me ni fa lafiya ta kalau."
kai ya girgiza ganin ba tasowar zatayi ba ya janyo hanunta.
"Aljanu na son shafarki kice lafiyan ki lau, ina kuwa batun lafiya anan."
"Daddy kada ka rika yarda da wad'annan masu magungunan karyar fa."
"Zauna dan Allah."
ya yi maganar yana zaunar da ita.
da kansa ya bud'e yahakin ya saka yakuma rufeta da hijabinta kamar yadda aka ce masa.
sai da ya tabbatar hayakin ya ratsata sosai tana ta sauke tari da atishawa kafin ya bud'e ta.
yana fad'in
"Sai dai su kare a haka amma bazasu tab'a samin damar shigar jikin ki ba."
ita dai ido ta bisa da shi.
Da daddare kafin ta kwanta sai da ya tabbatar da tayi wankan maganin da hayaki.
duk da bataso ba.
Washegari da safe Aunty ta fito zata nufi kichin, tana bud'e kofar bedroom taga wani katon zomo fari soll,
idanunsa manya masu matukar razanarwa. yana zaune a dai-dai tsakiyar bakin kofa,
ya d'aga kunnuwansa sama yana juya idanun nasa da sam basuyi kama da idanun zomo ba.
wani irin juyi ta yi da farfe ta maida kofar ta rufe.
Tana waigowa kirjin ta ne yawani irin tsinkewa hango sa da tayi kan gadon Feeryal, wacce ke bacci yanzu kafin ta fita sai da ta gyara mata kwanci,
sai ga shi ta ganta zaune suna wasa da zomon da ta gani a bakin kofa,
yanzu-yanzu da ko second 1 baiyi ba
wani uban kara ta sake sakanakon had'a ido da shi da idanunsa masu matukar ban tsoro.
ta yanke jiki ta zube kasa.
Da sauri had'e da gudu Daddy dake cikin bathroom yafito, ya yi kanta cikin hanzari yana jijjigata da kiran sunan ta.
gani bata ko motsi da sauri yaje ya d'au gorar ruwa yazo ya yayyafa mata.
numfashi mai karfi ta sauke ta zabura zata mike, da sauri ya ruko ta.
"Fad'imatu mene ne ki natsu."
hannu ta shiga nunawa in da Feeryal ta ke
"Yana can yana can akwai wani abakin kofa."
ya waiga in da take nuna masa baiga komai ba, sai Feeryal da ke zaune.
ya ce
"Babu komai fa ni ban ga komai ba, bakiyi hayakin nan ba yau, muje maza kiyi."
ya d'agota suka karasa cikin d'akin.
Ranar haka Aunty ta wuni sukuku lamarin nason fin karfinta★★
Tekun Matip acan cikin fadar sarkin aljanu Matip,
dake karkashin teku cikin wani katon kasurgumin kogo mai matukar girma.
duniya ce guda a gurin.
matakan tsaro ne jiga-jigai masu matukar had'ari.
kifaffen masarautar da aka kifeshi tun tsawon shekaru d'ari biyu da hamsin da suka shud'e.
shine yakuma dawowa daram.
shugaba sarkin aljanu Matip yake cigaba da mulkarsa.
bayan tsawon shekarun da ya yi a tsare a kuma garkame sakamakon faruwar wani lamari.
Manya-manyan jiga-jigan dodanni aljanu majiya karfi masu tsuffar ban tsoro ne ke tsaron kofar masarautar, tasama da kasa.
Acikin fada sarki aljani Matip ne zaune a kan karagarsa na alfarma da aka yi sa da gundarin zinari.
ya yin da fadawa ke zagaye da shi.
Sarki aljani Matip ya dubi wazirinsa Kutub sannan ya yi gyaran murya, ya ce
"Akirawo Tarmuzu yanzun nan."
waziri Kutub ya dukar da kai ya ce
"Angama ya shugaba na."
wani kambu dake rike da shi ya murza cikin second 1 wani aljani ya bayyana a gaban sarki Matip. yazube gaban sa yana fad'in
"Na amsa kira ya shugaba na."
Sarki Matip ya dubesa sannan ya ce
"Tarmuzu Kudakata haka ku dai na bayyana ta ko wata tsuffa kuna razanin uwar gijiyarta,
zata rasa samin kula yadda ya kamata idan hakan ta faru kuma bazan yafe muku ba!."
"Tuba muke ya shugaba na a gafarce mu."
aljani Matip ya girgiza kai sannan ya d'aga masa hanu, nan take yab'ace..
Kimanin sati biyu kenan Aunty bata cikin walwalar ta, sai baya-baya take da Feeryal burin ta dai surabu lafiya.
kullum dai Daddy na karfafata da bata kwarin gwuiwa, yana ta so yaga ta cire kokonto kan Feeryal d'in, duk da shima yanzu lamarin yafara jefashi cikin nazari.
sun shefe tsawon sati gudannan bata kuma ganin wani abin tare da Feeryal ba.
sai dai wani lokacin idan ta barta ita kad'ai takanzo ta same ta tana ta wasa kamar tana yi da wani, haka nan zata d'auke ta, dan tayi alkawarin cigaba da kulawa da ita, amma cikin takasantsan burin ta dai surabu lafiya..★★
takuma yin baya a muguwar razane,
da karfi ta furta "Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un!."
cikin tsananin kad'uwa.
tana furta kalmar innalillahi da sauri macijin ya shiga ware jikinsa yana bi ta kan kafafun Feeryal da ke zaune tana wasa da shi, yanufi kofa yana isa dai-dai bakin kofa ta nime shi ko sama ko kasa ya b'ace mata bat bata kuma ganinsa ba,
bata kuma san ta in da ya bi ba dan kofar a rufe take.
Rasashi ke da wuya tasoma jin wani kara mai cike da amon sauti na dukar can cikin kunnuwanta.
da karfi ta rumtse ido tare da kai hannu cikin kunnenta da take ji kamar dodon kunnuwan nata zasu zazzago su fito waje.
ji tayi ana fad'in
"Ke kad'ai bazaki iya bata kariya ba dole sai da taimakon muuuu!."
kuma toshe kunnuwanta tayi da karfi tana juyi had'e da tangad'i har sai da ta zube kasa.
a dai-dai lokacin da taji kamar an fisge mata dodon kunne, nan da nan wani uban zufa ya shiga keto mata.
a hankali kuma taji yanayin ya d'auke cak cikin second 1 tadawo dai-dai.
Da sauri ta mike zaune tashi ja da baya tana bin Feeryal da kallon tsaro.
ita ko yarinyar baki ta b'are tana mika mata hanu alamun ta d'auke ta.
Cikin rawar murya Aunty tashiga fad'in
"Ban tab'a cutar da ke ba, ban d'auko ki dan na cutar da ke ba,
sai dan na taimake ki, ki dubi girman Allah kada ki cutar da ni,
zan mai da ke in da na d'auko ki,
nayi zaton ke d'in jinsin mu ne shiyasa na d'auko ki, ban d'auko ki dan na cutar da ke ba!."
Gaba d'aya Aunty ta birkice ta ko ta ina a jikinta b'ari yake, tsoro mai tsanani ya baibaye ta.
ta kasa iya mikewa kan jafafunta sai ja da baya take a zaune.
Jin karar bud'e kofa ta waigo da sauri a bala'in razane, dan tagama zaton macijin ne ya dawo.
ganin Daddy ne ya shigo da sauri ta mike a guje tayi gurin shi,
ta fad'a jikin shi ta kankameshi da karfi tana fad'in
"Daddy maciji na ganshi da ido na! dan Allah ka d'auke ta ka mai da ita in da muka d'auko ta,
wlh nahakura zanci cigaba da zama a haka gara na tabbata a matsayin juya, na hakura bana son d'a zanyi rayuwa ta ni kad'ai a haka!."
Da sauri yadad'a rukota sosai ganin yadda gaba d'aya ta fita hayyacin ta.
ya janyo ta suka karaso cikin parlour, ya zauna kan kujera tare da zaunar da ita a gefen sa.
"Fad'imatu."
ya kira sunan ta yana kallon fuskarta.
ido ta zuba masa sai kuma ta girgiza kanta kamar wacce ke son dawowa hayyacin ta.
ta yunkura zata mike da sauri ya ruko ta yakuma duban ta da kyau ya ce
"Ki dawo hayyacin ki."
wani nannauyan numfashi ta sauke da sauri ta waiga gefe da gefen ta sai kuma ta maida duban ta gareshi.
"Fad'imatu." yakuma kiran sunan ta
murya a raunace.
kai ta girgiza ta ce
"Daddy."
"Numfashi ya fesar sannan yakuma rukota da kyau ya ce
"A ina kika ga macijin Fad'imatu? akaf fad'in gidan nan da kewayen sa, ba macijiba ko kwaro in har mai cutar wa ne bai isa ya matso yankin gidan nan ba, ta ko wane kusurwa;
tazarar taku dubu ne ta ko wata kusurwa sakanin mu da duk wani nau'in kwaro mai cutar wa,
ko ta sama ko ta kasa,
sam maciji bazai iya shigowa gidan nan ba, a zagaye gidan nan yake da maganin su,
idan kuwa sukayi gigin shiga to kuwa zasu mutu tun kan su karaso,
koda ta cikin karkashin k'asa ne kuwa."
"Daddy na ganshi da ido na fa babba ne sosai agaban Feeryal tana wasa da shi, kuma naji ana magana da karfi kamar za'a fasa min kunne,
ni dai a maida ita kawai wlh na hakura."
shiru ya yi yana kallonta a kasan ransa yake fad'in
"Anya ba aljanu ne ke son shafarta ba?."
kwana biyu gaba d'aya yaga yanayin ta ya sauya, abin da bazai faruba tarika cewa ya faru.
kai ya jinjina sannan ya ce
"Gizo ne kawai."
da sauri ta ce "A'a Daddy wannan kam ba gizo bane nagani da ido na da gaske ne."
"D'azu bakya hayyacin ki Fad'imatu akwai abin da ke shirin faruwa da ke, yakamata a dakile faruwar hakan,
ina zuwa."
Yafad'a yana mikewa ya nufi bedroom yafito d'auke da Alkur'ani mai girma ya dawo in da take, ya bud'e ya mika mata.
ya ce "Kirika karantawa ina zuwa, bari naje na dawo, dan shi yafi komai kariya."
Ya isa ya d'auki Feeryal data fara kuka ya ajeta a gefenta.
yana cewa
"Ta gaji da zamane ko tana jin yunwa."
ido ta bita da shi harga Allah tsoro take bata yanzu.
Cikin hanzari yafita, Daddy yakai awa d'aya zuwa d'aya da rabi kafin ya dawo.
a bedroom ya same su dan ta sami kwarin gwuiwa da taimakon karanta Alkur'anin da tayi, har ta ji karfin zuciya ta d'auke ta ta je tamata wanka, tana gama shiryata kuwa tayi bacci.
Daddy ya mika mata kullin laidar daya shigo da shi.
ta karb'i laidar tana d'an jujjuyashi a hannunta sai kuma ta kunce laidar.
da mamaki take kallon kulli-kullin magunguna.
da fuskar tambaya ta dube shi,
sai kuma taga ya d'au abin saka kuraren wuta ya jona shi gijin wuta,
yana fad'in
"Hayaki ne da wanka na karb'o miki, zo maza kiyi hayakin anjima in zaki kwanta kiyi wankan maganin sai ki kara yin hayakin."
"Hayaki da wanka kuma? asabo da me ni fa lafiya ta kalau."
kai ya girgiza ganin ba tasowar zatayi ba ya janyo hanunta.
"Aljanu na son shafarki kice lafiyan ki lau, ina kuwa batun lafiya anan."
"Daddy kada ka rika yarda da wad'annan masu magungunan karyar fa."
"Zauna dan Allah."
ya yi maganar yana zaunar da ita.
da kansa ya bud'e yahakin ya saka yakuma rufeta da hijabinta kamar yadda aka ce masa.
sai da ya tabbatar hayakin ya ratsata sosai tana ta sauke tari da atishawa kafin ya bud'e ta.
yana fad'in
"Sai dai su kare a haka amma bazasu tab'a samin damar shigar jikin ki ba."
ita dai ido ta bisa da shi.
Da daddare kafin ta kwanta sai da ya tabbatar da tayi wankan maganin da hayaki.
duk da bataso ba.
Washegari da safe Aunty ta fito zata nufi kichin, tana bud'e kofar bedroom taga wani katon zomo fari soll,
idanunsa manya masu matukar razanarwa. yana zaune a dai-dai tsakiyar bakin kofa,
ya d'aga kunnuwansa sama yana juya idanun nasa da sam basuyi kama da idanun zomo ba.
wani irin juyi ta yi da farfe ta maida kofar ta rufe.
Tana waigowa kirjin ta ne yawani irin tsinkewa hango sa da tayi kan gadon Feeryal, wacce ke bacci yanzu kafin ta fita sai da ta gyara mata kwanci,
sai ga shi ta ganta zaune suna wasa da zomon da ta gani a bakin kofa,
yanzu-yanzu da ko second 1 baiyi ba
wani uban kara ta sake sakanakon had'a ido da shi da idanunsa masu matukar ban tsoro.
ta yanke jiki ta zube kasa.
Da sauri had'e da gudu Daddy dake cikin bathroom yafito, ya yi kanta cikin hanzari yana jijjigata da kiran sunan ta.
gani bata ko motsi da sauri yaje ya d'au gorar ruwa yazo ya yayyafa mata.
numfashi mai karfi ta sauke ta zabura zata mike, da sauri ya ruko ta.
"Fad'imatu mene ne ki natsu."
hannu ta shiga nunawa in da Feeryal ta ke
"Yana can yana can akwai wani abakin kofa."
ya waiga in da take nuna masa baiga komai ba, sai Feeryal da ke zaune.
ya ce
"Babu komai fa ni ban ga komai ba, bakiyi hayakin nan ba yau, muje maza kiyi."
ya d'agota suka karasa cikin d'akin.
Ranar haka Aunty ta wuni sukuku lamarin nason fin karfinta★★
Tekun Matip acan cikin fadar sarkin aljanu Matip,
dake karkashin teku cikin wani katon kasurgumin kogo mai matukar girma.
duniya ce guda a gurin.
matakan tsaro ne jiga-jigai masu matukar had'ari.
kifaffen masarautar da aka kifeshi tun tsawon shekaru d'ari biyu da hamsin da suka shud'e.
shine yakuma dawowa daram.
shugaba sarkin aljanu Matip yake cigaba da mulkarsa.
bayan tsawon shekarun da ya yi a tsare a kuma garkame sakamakon faruwar wani lamari.
Manya-manyan jiga-jigan dodanni aljanu majiya karfi masu tsuffar ban tsoro ne ke tsaron kofar masarautar, tasama da kasa.
Acikin fada sarki aljani Matip ne zaune a kan karagarsa na alfarma da aka yi sa da gundarin zinari.
ya yin da fadawa ke zagaye da shi.
Sarki aljani Matip ya dubi wazirinsa Kutub sannan ya yi gyaran murya, ya ce
"Akirawo Tarmuzu yanzun nan."
waziri Kutub ya dukar da kai ya ce
"Angama ya shugaba na."
wani kambu dake rike da shi ya murza cikin second 1 wani aljani ya bayyana a gaban sarki Matip. yazube gaban sa yana fad'in
"Na amsa kira ya shugaba na."
Sarki Matip ya dubesa sannan ya ce
"Tarmuzu Kudakata haka ku dai na bayyana ta ko wata tsuffa kuna razanin uwar gijiyarta,
zata rasa samin kula yadda ya kamata idan hakan ta faru kuma bazan yafe muku ba!."
"Tuba muke ya shugaba na a gafarce mu."
aljani Matip ya girgiza kai sannan ya d'aga masa hanu, nan take yab'ace..
Kimanin sati biyu kenan Aunty bata cikin walwalar ta, sai baya-baya take da Feeryal burin ta dai surabu lafiya.
kullum dai Daddy na karfafata da bata kwarin gwuiwa, yana ta so yaga ta cire kokonto kan Feeryal d'in, duk da shima yanzu lamarin yafara jefashi cikin nazari.
sun shefe tsawon sati gudannan bata kuma ganin wani abin tare da Feeryal ba.
sai dai wani lokacin idan ta barta ita kad'ai takanzo ta same ta tana ta wasa kamar tana yi da wani, haka nan zata d'auke ta, dan tayi alkawarin cigaba da kulawa da ita, amma cikin takasantsan burin ta dai surabu lafiya..★★