Sashe 3
Feeryal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ido Hajiya Karima ta gwalalo tare dare da fad'in
"Zancen banza kai yaushe akayi cikin da za'a yi haihuwar har kowa ya kasa sani, ai wannan sai dai taga haihuwa a tsuliyar wani badai a nata ba."
"Wlh Umma Karima naganta da idona tana bawa yaro nono."
kirji Hajiya Karima ta buga har suna had'a baki da Mommy wajen fad'in
"Yaushe tayi ciki har ta haihu bamu sani ba."
"Wlh ni dai na ganta dama Hajiya ce ta aike ni kiran Daddy tun jiya take ta kiransa a waya baya d'auka,
shine tace naje na kirawo mata shi dan tasan yana can makale wajen kinibabbiyar matar nan tasa, bari ma naje na sanar mata sabon labari."
tafice da gudu tanufi sashin Hajiya wato kakar su.
Tun daga bakin kofa take fad'in "Hajiya Hajiya Hajiya."
wata dattijuwar mata dake zaune a wani kayataccen parlour tana sanye da gilashi a idanunta, hutu da kwanciyar hankali sun bayyana a kijinta, wanda ya b'oye tsufarta, zaka iya mata kallon daya gaza shekarunta sabar hutu.
"Ke wani irin shashancin kira ne wannan, sai naci mutuncinki Farida, ina tun d'azu na aike ki sai yanzu kikaga damar dawowa ko."
cikin rad'a da iya gulma ta ce
"Hajiya wlh Aunty ta haihu Daddy yana can."
baki Hajiya ta karkace ta ce
"Ke Farida Fatima ce ta haihu cewa akayi miki haihuwar wasa ce, shekara nawa tana zaune sai dai taci taje ta juye a shadda, ko b'atan wata bata tab'a yi ba,
wannan da ita yafara aura nasan bazata tab'a barinsa ya kara aure ba, da ni da ganin jikokina ta gefen sa kuwa har abada, sai dai in cikin abinci tayi ta haifa a shadda, bari naje na ganewa idona."
"Wlh Hajiya kije kigani da gaske ne."
Hajiya ta mike tanufi kofa tana fad'in
"Yanzu ma kuwa, dan rashin daraja Fatima tafi masa ni, tun jiya baizo ya gaishe ni ba yana makale a gurin ta."
A b'angaren su Mommy kuwa bakaramin girgiza sukayi da jin lamarin ba, dukkanin su suka nufi sashin Aunty dan gane wa idon su abin da ke faruwa.
a kusan tare suka iso da Hajiya dan ita direban ta tasa ya kaita side d'in Aunty'n dan tafiyar tafi yi mata sauki.
suna shiga parlour'n kowa yatsaya cike da d'in bin mamakin ganin jaririya a hannun Aunty tana shayar da ita.
hankali tashe Mommy da Umma Karima suke kallon-kallo, kowa da irin abun da yake sakawa a ransa.
hajiya ta rafka wani uban salati tare da tafa hanu tana fad'in
"Ikon Allah Abubakar ina cikin gidan ayi haihuwa ban sani ba, kamar yadda bansan da cikin ba, Eh lallai ta wanke ta baka kasha, ka mance da uwar da ta haife ka."
Da sauri Daddy ya mike yana fad'in
"Sannu da zuwa Hajiya yanzu nake shirin zuwa gaishe ki, bismilla ga guri zauna."
hannu ta d'aga masa tana fad'in
"Ba zama ne ya kawo ni ba, na ce yaushe ta haihu ban sani ba!."
kai ya sunkuyar kana ya d'ago ya dubi mahaifiyar tasa kana ya ce..........!
Mommyn Twins ce
🌺🌺 *FEERYAL* 🌺🌺
*NA*
*RASHEEDAT S DIRECTOR*
( _Book 1_)
*~Free page~*
*_Littafin na kud'i ne 500 account no 3170524141 Rashida Salihu first bank ka-ki tura shaidar biya ta WhatsApp number ta 08034690723_*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'SâœðŸ?*
*🇦SSOCIATIONðŸ¤ðŸ»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇ðŸ»
https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association
*____________________________________*
Bismillahirrahmanurrahim
🅿�2
"Da ma Hajiya zanzo muyi magana, amma tun da har kinzo ki zauna kiji yadda akayi zata haihu ne baki sani ba."
"Ba gashi kuwa sai zuwa nayi naga d'a a hannu ba, ai baka d'auke ni da mahimmanci ba, narasa me ke damunka Abubakar akan Fatima duk ka susuce kazama wani iri, tun jiya nake kiran ka a waya sabo da kuna nakudar munafurci kaki d'aga wayar ma, bare har kazo in da nake,
Allah yasa kafin ta haihu dubunta sun haihu,
ko wani munafurcin ne na b'oye cikin da haihuwar oho."
wani irin mummunar fad'uwar gaba Umma Karima ta ji.
yanzu bawai haihuwar ce ke firgitata ba, duk da tabbacin da take da shi kan cewa bazata tab'a haihuwa ba har abada, ga kuma akasin hakan ta gani.
fatan ta d'aya kada a ce namiji ta haifa.
a b'angaren Mommy ma haka abun yake.
mita ta shiga yi tana dad'a ingiza Hajiya
"Yanzu har rashin muhimmancin mu yakai ta haihu a cikin gidan nan bamu saniba, idan an b'oye ciki sai a b'o haihuwa, haba Alhaji me ka mai da mu haka."
Hajiya ta cab'i zancen da fad'in
"Marasa mutunci mana haka ya mai da kowa, to ka zauna da matarka kucigaba da munafurcin ku, kada ka sake kazo in da nake."
Ta juya tana kokarin fita da sauri ya tare ta
"Hajiya kiyi hakuri ki saurare ni,
bafa haihuwa Fatima tayi ba, sai kuma tayi ciki har ta haihu ki gaza sani, abun da ake fatan samu idan aka samu ai kowa sai ya sani,
bana gida ba har da na waje, kowa za'a sanar masa yataya mu farinci,
jiya a hanyarmu ta dawowa muka tsinci jaririyar a cikin ruwa, da alama had'ari iyayen ta sukayi tana bukatar taimako,
shine muka d'auke ta, likita ya shaida mana bazata iya rayuwa ba sai da nonon uwa shiyasa aka samarwa Fad'imatu ruwan nono domin ta ceto rayuwar ta."
Wani irin zabura dukkanin su sukayi.
Hajiya ta bigi kirji ta tuma tsalle ta zube kasa ta saka hannu a ka tana fad'in
"Wayyo Allah Abubakar da Fatima zasu kashe ni, tsintar ta kukayi kuma a cikin ruwa, anya Abubakar
kanka d'aya kuwa ko aljanu sun shafe ka ne,
ku tsinci 'yar kuma acikin ruwa ma har ka lamunci matarka ta shayar da ita,
sabo da karasa 'ya'ya ne ko me?
idan ita juya ce bata haihuwa ai kai da 'ya'yan ka ta ganka tafe da kafafun su,
duk basu ishekaba har sai kanimi kari da 'ya'yan aljanu."
Tamaso ta leka fuskar Feeryal dake rungume a hannun Aunty, data rungume ta tsam kamar za'a kwatar mata ita.
Hajiya takuma zabura tare da mustsuke idonta tana fad'in
"Lahaula maganin baki wasayyahuuuuu ya tsaya a kanki Fatima!
Abubakar d'iyar aljanu kuka d'auko kuka kawo mana gida,
wlh ko shakka babu wannan d'iyar aljanu ce, tun da nake ban tab'a ganin mutum irin wannan ba,
ko a fina-finan masu jajayen kunnuwan da nake gani ana haskosu a TV,
dubi kalarta dubi kalar kwayar idanun ta, sam basuyi kalar na mutane ba,
kwayar ido kamar na magen mayu wlh ba mutum bace;
maza-maza kuyi gaggawar d'aukar 'yar su ku mayar musu in da kuka d'auko musu ita,
tun kafin bala'i ya sauka a gidan nan,
dan bazamu iya da fad'an aljanu ba,
dan babu kaura cikin dangin mu,
wani bala'in kuke son d'auko mana, zaku d'auko aljanar ruwa ku kawo mana ita gida."
Mommy da Umma Karima har suna rige-rigen zuwa leka fuskar yarinyar, bakaramin firgici suka shiga da ganin halittar 'yar ba,
'ya'yansu ma kowa sai da yaje yagano fuskar ta.
Mommy tashiga zabga salati da tafa hannu tana fad'in
"Wlh aljana ce Hajiya dakur'ani bazamu zauna da aljanar ruwa a gidan nan ba, ko a fita da ita ko mu mufita da 'ya'yan mu, dan ambaliyar ruwa bazataci da mu ba ehe."
Umma Karima ta karkata baki cike da rashin mutunci tana aikawa Aunty kallon banza ta ce
"An dai yi asara rashin haihuwa nason bud'a miki kai shine har zaki d'auko aljana ki kawo mana ita cikin gida,
to wlh ba a gidan nan ba, idan haihuwar abin banza ne ki haifa mana,
sai kinje kin d'auko aljanar ruwa kin kawo mana damuwa."
Rumtse ido Aunty tayi tana jin yanda maganganun su ke mata yawo cikin kwakwalwa.
da sauri Daddy yataro Hajiya ganin yadda take shiga bata nan take fita ba.
ya ce
"Hajiya kiyi hakuri amma ba aljana ba ce mutum ce, ina kyautata zaton watakila badaga yankin kasarmu take ba,
shi yasa kamanninta ya bambanta amma mutum ce ita irin mu."
"Inji uban wa tun da kake katab'a gani mutum kyakkyawa irin wannan?
kana kallon aljana kiri-kiri kace mutum,
dama ance aljanun ruwa kyawawa ne gashinan kiri-kiri ina gani kace ba haka ba,
kai Ajimi kirawo min Sulaiman da Tukur yau zan bar gidan nan dan bazan zauna da aljana ba."
Ajeemal ya juya yana jan kwafa, sam baya son fitinar kakar nan tasu.
Hajiya ta cigaba da fad'a har tana kumfar baki, su Mommy na tayata.
batare da b'ata lokaci ba Alhaji Sulaiman da Alhaji Tukur suka amsa kiran mahaifiyar tasu.
Hajiya na ganin su takawo kuka ta saka tana sharb'e hanci da fad'in
"Zamata yakare a gidan nan Abubakar ya zab'a ko ni ko aljanar ruwa da matarsa."
da sauri suka karaso in da take sukashiga bata hakuri, Alhaji Sulaiman ya ce
"Hajiya dan Allah kiyi hakuri zo muje sashin ki muyi magana."
da kyar suka janye ta zuwa sashin nata.
Numfashi Daddy ya sauke ganin fitarsu kana ya maida dubansa kan Mommy da Umma Karima ya ce
"Duk wacce bazata iya zamaba ta kama gabanta."
yana kaiwa nan yajuya yabi bayan su Hajiya.
Mugun kallo suka wasawa Aunty Umma Karima ta ce
"Bokanki yafad'a miki karya sai dai ke kibar gidan nan ba dai mu masu 'ya'ya ba."
Mommy kuwa kwafa tayi tare da kuma wasa mata harara tajuya takad'a keyar 'ya'yan ta tana fad'in
"Maza kubar nan kada aljana tashiga jikinku."
Murmushin takaici Aunty tayi tare da bin bayansu da kallo, tana mai dad'a rungume Feeryal ajikinta.
A can sashin Hajiya kuwa sosai ta tubure ita ala dole sai dai Daddy ya zab'i ko ita ko aljanar ruwa,
dan bazata zauna da aljana a gida d'aya ba, bare ta shafe ta ta shafi jikokinta.
da kyar suka shawo kanta da alkawarin za'a mai da yarinyar inda aka d'auko ta.
Ko da suka fito daga sashin nata Alhaji Sulaiman wato Abbieh da Alhaji Tukur Dad suka dubi d'an uwan nasu.
Dad ya ce
"Yaya ina ganin a d'auki yarinyar nan a mayar da ita in da aka sameta ina ganin shine kad'ai samin masalaha,
Hajiya tayi fushi sosai."
"Zancen banza kai yaushe akayi cikin da za'a yi haihuwar har kowa ya kasa sani, ai wannan sai dai taga haihuwa a tsuliyar wani badai a nata ba."
"Wlh Umma Karima naganta da idona tana bawa yaro nono."
kirji Hajiya Karima ta buga har suna had'a baki da Mommy wajen fad'in
"Yaushe tayi ciki har ta haihu bamu sani ba."
"Wlh ni dai na ganta dama Hajiya ce ta aike ni kiran Daddy tun jiya take ta kiransa a waya baya d'auka,
shine tace naje na kirawo mata shi dan tasan yana can makale wajen kinibabbiyar matar nan tasa, bari ma naje na sanar mata sabon labari."
tafice da gudu tanufi sashin Hajiya wato kakar su.
Tun daga bakin kofa take fad'in "Hajiya Hajiya Hajiya."
wata dattijuwar mata dake zaune a wani kayataccen parlour tana sanye da gilashi a idanunta, hutu da kwanciyar hankali sun bayyana a kijinta, wanda ya b'oye tsufarta, zaka iya mata kallon daya gaza shekarunta sabar hutu.
"Ke wani irin shashancin kira ne wannan, sai naci mutuncinki Farida, ina tun d'azu na aike ki sai yanzu kikaga damar dawowa ko."
cikin rad'a da iya gulma ta ce
"Hajiya wlh Aunty ta haihu Daddy yana can."
baki Hajiya ta karkace ta ce
"Ke Farida Fatima ce ta haihu cewa akayi miki haihuwar wasa ce, shekara nawa tana zaune sai dai taci taje ta juye a shadda, ko b'atan wata bata tab'a yi ba,
wannan da ita yafara aura nasan bazata tab'a barinsa ya kara aure ba, da ni da ganin jikokina ta gefen sa kuwa har abada, sai dai in cikin abinci tayi ta haifa a shadda, bari naje na ganewa idona."
"Wlh Hajiya kije kigani da gaske ne."
Hajiya ta mike tanufi kofa tana fad'in
"Yanzu ma kuwa, dan rashin daraja Fatima tafi masa ni, tun jiya baizo ya gaishe ni ba yana makale a gurin ta."
A b'angaren su Mommy kuwa bakaramin girgiza sukayi da jin lamarin ba, dukkanin su suka nufi sashin Aunty dan gane wa idon su abin da ke faruwa.
a kusan tare suka iso da Hajiya dan ita direban ta tasa ya kaita side d'in Aunty'n dan tafiyar tafi yi mata sauki.
suna shiga parlour'n kowa yatsaya cike da d'in bin mamakin ganin jaririya a hannun Aunty tana shayar da ita.
hankali tashe Mommy da Umma Karima suke kallon-kallo, kowa da irin abun da yake sakawa a ransa.
hajiya ta rafka wani uban salati tare da tafa hanu tana fad'in
"Ikon Allah Abubakar ina cikin gidan ayi haihuwa ban sani ba, kamar yadda bansan da cikin ba, Eh lallai ta wanke ta baka kasha, ka mance da uwar da ta haife ka."
Da sauri Daddy ya mike yana fad'in
"Sannu da zuwa Hajiya yanzu nake shirin zuwa gaishe ki, bismilla ga guri zauna."
hannu ta d'aga masa tana fad'in
"Ba zama ne ya kawo ni ba, na ce yaushe ta haihu ban sani ba!."
kai ya sunkuyar kana ya d'ago ya dubi mahaifiyar tasa kana ya ce..........!
Mommyn Twins ce
🌺🌺 *FEERYAL* 🌺🌺
*NA*
*RASHEEDAT S DIRECTOR*
( _Book 1_)
*~Free page~*
*_Littafin na kud'i ne 500 account no 3170524141 Rashida Salihu first bank ka-ki tura shaidar biya ta WhatsApp number ta 08034690723_*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'SâœðŸ?*
*🇦SSOCIATIONðŸ¤ðŸ»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇ðŸ»
https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association
*____________________________________*
Bismillahirrahmanurrahim
🅿�2
"Da ma Hajiya zanzo muyi magana, amma tun da har kinzo ki zauna kiji yadda akayi zata haihu ne baki sani ba."
"Ba gashi kuwa sai zuwa nayi naga d'a a hannu ba, ai baka d'auke ni da mahimmanci ba, narasa me ke damunka Abubakar akan Fatima duk ka susuce kazama wani iri, tun jiya nake kiran ka a waya sabo da kuna nakudar munafurci kaki d'aga wayar ma, bare har kazo in da nake,
Allah yasa kafin ta haihu dubunta sun haihu,
ko wani munafurcin ne na b'oye cikin da haihuwar oho."
wani irin mummunar fad'uwar gaba Umma Karima ta ji.
yanzu bawai haihuwar ce ke firgitata ba, duk da tabbacin da take da shi kan cewa bazata tab'a haihuwa ba har abada, ga kuma akasin hakan ta gani.
fatan ta d'aya kada a ce namiji ta haifa.
a b'angaren Mommy ma haka abun yake.
mita ta shiga yi tana dad'a ingiza Hajiya
"Yanzu har rashin muhimmancin mu yakai ta haihu a cikin gidan nan bamu saniba, idan an b'oye ciki sai a b'o haihuwa, haba Alhaji me ka mai da mu haka."
Hajiya ta cab'i zancen da fad'in
"Marasa mutunci mana haka ya mai da kowa, to ka zauna da matarka kucigaba da munafurcin ku, kada ka sake kazo in da nake."
Ta juya tana kokarin fita da sauri ya tare ta
"Hajiya kiyi hakuri ki saurare ni,
bafa haihuwa Fatima tayi ba, sai kuma tayi ciki har ta haihu ki gaza sani, abun da ake fatan samu idan aka samu ai kowa sai ya sani,
bana gida ba har da na waje, kowa za'a sanar masa yataya mu farinci,
jiya a hanyarmu ta dawowa muka tsinci jaririyar a cikin ruwa, da alama had'ari iyayen ta sukayi tana bukatar taimako,
shine muka d'auke ta, likita ya shaida mana bazata iya rayuwa ba sai da nonon uwa shiyasa aka samarwa Fad'imatu ruwan nono domin ta ceto rayuwar ta."
Wani irin zabura dukkanin su sukayi.
Hajiya ta bigi kirji ta tuma tsalle ta zube kasa ta saka hannu a ka tana fad'in
"Wayyo Allah Abubakar da Fatima zasu kashe ni, tsintar ta kukayi kuma a cikin ruwa, anya Abubakar
kanka d'aya kuwa ko aljanu sun shafe ka ne,
ku tsinci 'yar kuma acikin ruwa ma har ka lamunci matarka ta shayar da ita,
sabo da karasa 'ya'ya ne ko me?
idan ita juya ce bata haihuwa ai kai da 'ya'yan ka ta ganka tafe da kafafun su,
duk basu ishekaba har sai kanimi kari da 'ya'yan aljanu."
Tamaso ta leka fuskar Feeryal dake rungume a hannun Aunty, data rungume ta tsam kamar za'a kwatar mata ita.
Hajiya takuma zabura tare da mustsuke idonta tana fad'in
"Lahaula maganin baki wasayyahuuuuu ya tsaya a kanki Fatima!
Abubakar d'iyar aljanu kuka d'auko kuka kawo mana gida,
wlh ko shakka babu wannan d'iyar aljanu ce, tun da nake ban tab'a ganin mutum irin wannan ba,
ko a fina-finan masu jajayen kunnuwan da nake gani ana haskosu a TV,
dubi kalarta dubi kalar kwayar idanun ta, sam basuyi kalar na mutane ba,
kwayar ido kamar na magen mayu wlh ba mutum bace;
maza-maza kuyi gaggawar d'aukar 'yar su ku mayar musu in da kuka d'auko musu ita,
tun kafin bala'i ya sauka a gidan nan,
dan bazamu iya da fad'an aljanu ba,
dan babu kaura cikin dangin mu,
wani bala'in kuke son d'auko mana, zaku d'auko aljanar ruwa ku kawo mana ita gida."
Mommy da Umma Karima har suna rige-rigen zuwa leka fuskar yarinyar, bakaramin firgici suka shiga da ganin halittar 'yar ba,
'ya'yansu ma kowa sai da yaje yagano fuskar ta.
Mommy tashiga zabga salati da tafa hannu tana fad'in
"Wlh aljana ce Hajiya dakur'ani bazamu zauna da aljanar ruwa a gidan nan ba, ko a fita da ita ko mu mufita da 'ya'yan mu, dan ambaliyar ruwa bazataci da mu ba ehe."
Umma Karima ta karkata baki cike da rashin mutunci tana aikawa Aunty kallon banza ta ce
"An dai yi asara rashin haihuwa nason bud'a miki kai shine har zaki d'auko aljana ki kawo mana ita cikin gida,
to wlh ba a gidan nan ba, idan haihuwar abin banza ne ki haifa mana,
sai kinje kin d'auko aljanar ruwa kin kawo mana damuwa."
Rumtse ido Aunty tayi tana jin yanda maganganun su ke mata yawo cikin kwakwalwa.
da sauri Daddy yataro Hajiya ganin yadda take shiga bata nan take fita ba.
ya ce
"Hajiya kiyi hakuri amma ba aljana ba ce mutum ce, ina kyautata zaton watakila badaga yankin kasarmu take ba,
shi yasa kamanninta ya bambanta amma mutum ce ita irin mu."
"Inji uban wa tun da kake katab'a gani mutum kyakkyawa irin wannan?
kana kallon aljana kiri-kiri kace mutum,
dama ance aljanun ruwa kyawawa ne gashinan kiri-kiri ina gani kace ba haka ba,
kai Ajimi kirawo min Sulaiman da Tukur yau zan bar gidan nan dan bazan zauna da aljana ba."
Ajeemal ya juya yana jan kwafa, sam baya son fitinar kakar nan tasu.
Hajiya ta cigaba da fad'a har tana kumfar baki, su Mommy na tayata.
batare da b'ata lokaci ba Alhaji Sulaiman da Alhaji Tukur suka amsa kiran mahaifiyar tasu.
Hajiya na ganin su takawo kuka ta saka tana sharb'e hanci da fad'in
"Zamata yakare a gidan nan Abubakar ya zab'a ko ni ko aljanar ruwa da matarsa."
da sauri suka karaso in da take sukashiga bata hakuri, Alhaji Sulaiman ya ce
"Hajiya dan Allah kiyi hakuri zo muje sashin ki muyi magana."
da kyar suka janye ta zuwa sashin nata.
Numfashi Daddy ya sauke ganin fitarsu kana ya maida dubansa kan Mommy da Umma Karima ya ce
"Duk wacce bazata iya zamaba ta kama gabanta."
yana kaiwa nan yajuya yabi bayan su Hajiya.
Mugun kallo suka wasawa Aunty Umma Karima ta ce
"Bokanki yafad'a miki karya sai dai ke kibar gidan nan ba dai mu masu 'ya'ya ba."
Mommy kuwa kwafa tayi tare da kuma wasa mata harara tajuya takad'a keyar 'ya'yan ta tana fad'in
"Maza kubar nan kada aljana tashiga jikinku."
Murmushin takaici Aunty tayi tare da bin bayansu da kallo, tana mai dad'a rungume Feeryal ajikinta.
A can sashin Hajiya kuwa sosai ta tubure ita ala dole sai dai Daddy ya zab'i ko ita ko aljanar ruwa,
dan bazata zauna da aljana a gida d'aya ba, bare ta shafe ta ta shafi jikokinta.
da kyar suka shawo kanta da alkawarin za'a mai da yarinyar inda aka d'auko ta.
Ko da suka fito daga sashin nata Alhaji Sulaiman wato Abbieh da Alhaji Tukur Dad suka dubi d'an uwan nasu.
Dad ya ce
"Yaya ina ganin a d'auki yarinyar nan a mayar da ita in da aka sameta ina ganin shine kad'ai samin masalaha,
Hajiya tayi fushi sosai."