← Book details Feeryal Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 20 OF 52

Sashe 20

Feeryal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Zaraddin ya mike da sauri yazuba gwuiwowinsa a kasa ya had'e hannayen sa cikin karamar murya ya marairaice sosai yana fad'in
"Dan Allah dan girman Allah Daddy Dad kuyi hakuri wlh bazan kara ba, duk abin da kuka haneni bazan kara aikata shi ba, ku yafe min;
idan kuka kore ni ina zan je, bani da wanda suka fiku."
ya fashe da kuka wei-wei kunsan d'an kwaya da ladabin kule.
Daddy mai tausayi nan da nan tausayin sa ya cika shi da sauri ya ce
"Maso nan Zaraddin zo kusa dani."
ya rarrafo yazo gabansa.
Daddy ya sa hannu yana bubbuga kafad'ar sa.

"Ya isa haka Zaraddin, banyi maka hukunci dan bana son ka ba, sai ma dan kaunar da nake maka,
nafi kowa son naga kun gyaru kun zama mutanen kirki, da za'a rika kwatance da ku,
ba kaiba duk wanda ya aikata ba dai-dai ba acikin 'yan'uwan ka irin hukuncin da zan musu ke nan,
yarinyar nan amana ce a gare mu, nauyi ne a kanmu mutsare mata mutuncinta, sai inda karfin mu ya kare idan muka ga wani na shirin ci mata zarafi,
taya kuma za'ayi ace mu da hakkin hakan ke rataye a wuyan mu,
daga tsatson mu ne za'a sami mai son keta mata haddi,
kanwarku ce itama kada ku rika mata kallon wata daban, ku zamo mai bata kariya dan Allah;
wannan gargad'i ne kawai Zaraddin bazan iya nesanta ka gare mu ba wajibin mu ne baka tarbiyya dai-dai gwargwado,
Zaraddin na gamaka da Allah ka natsu ka daina biyewa abokan banza babu inda zasu kaika sai dai su kaika su baro,
nan da lokaci kad'an nake son d'agaku a kasarnan kuje ku karo karatu, kai da Ajeemal da Shamsuddin da Faisal, kai kad'ai nake da shakku a kanka,
dan Allah ka sawa rayuwar ka natsuwa."

Fad'a sosai Daddy ya yi masa Dad na taya shi.
daga bisani Dad yashiga bawa Daddy hakuri yakuma yi masa alkawarin in Allah ya yarda hakan bazata sake faruwa ba.
Daddy ya basu danar su tashi su tafi shi komai ya wuce a gurinsa.

Dad ya mike ya na fad'in
"Allah ya kara girma Yaya bango majinginar al'umma."
sannan ya dubi Zaraddin ya ce
"Sai ka tashi muje ai sha-sha-shan banza mara tunani."
Daddy ya katse shi
"Kul Tukur kar naji kayi masa wani abin."
kai Dad ya girgiza alamun ya d'auki umurnin yayan nasa.
kana ya kad'a keyar Zaraddin suka fita a daga side d'in Daddy, suka nufi side d'in Dad.

Suna shiga parlour da sauri Mom ta mike ta ruko Zaraddin tana dudduba jikin sa.
"Ya naga ka wani dishe, shi da ya ce min gidan masu kud'i ya kaika;
kana samin abinci mai kyau ma kuwa?
a wani irin makwanci kake kwanciya? badai da ruwan rijiya kake wanka ba dai? dubi fatarka duk kawani dishe haka."
Dad ya ce
"Daga zuwa kin tare shi da tambayoyi haka, ki barshi ya zauna mana, karya zan miki gashi ki tambaye shi wani irin gida na kaishi,
ko da bai kai nan ba amma ai gidan mai kud'i ne,
gidan aboki na Alhaji Uba na kaishi."

Baki Mom ta tab'e
"To ai ni banga wani alamun yaje gidan hutu ajikin sa ba, wlh aka sake gwada wa 'ya'yana gadara a gidan nan dole kaje ka siya mana gida mu koma dan bazan juri wulakanci ba,
wuce ka je kayi wanka ka huta,
zansa Ladi ta kai ma abinci yanzu."

Zaraddin ya juya yana wani tafiyar fankama, Dad ya ce
"Ka dai ji gargad'in dana maka idan ka sake
aka kuma samin matsala wlh sai na sab'a maka, bazaku rushe min mafarki na ba,
madadin ki gargad'e shi sabo da ya kiyaye gaba, kin tsaya wasu kananun magana,
gaba ya kamata ki hango da irin rayuwar daulan da zamu kasance ciki."
"Ai dai da b'acin rai bai aikata abu ba ayi masa sharri ace ya aikata."
"Inji wa kinfi kowa sanin halin d'anki yaushe ne naje na ye belunsu a hannun police, sunyi wa yarinya fyad'e."
"Eh ansan wancan amma ai na wannan aljana Feeryal d'in,
ai ba gaskiya ba ne, kage ne kawai."
"Ke dai kiyi shiru kawai ya dai kiyaye dan wlh yasa burina ya rushe ni da kaina zan damkashi hannun 'yan sanda."

Mita Mom ta ciga da yi ta d'au waya ta kira Ladi mai aikinta tana babban kicin su da duk ma'aikatan gidan, suna kokarin d'aura abincin rana.
Ladi na d'agawa Mom ta ce
Ki had'awa Zaraddin abinci mai rai da lafiya ki kai masa side d'in su."
"To hajiya."
cewar Ladi.

ko da Zaraddin ya shigo side d'in su, har ya d'aura hannu kan handle zai bud'e kofar bedroom d'insa,
sai kuma ya tsaya, yakai minti 10 a tsaye yana tunanin anya macijinnan ya fita kuwa, baya cikin d'akin nan?.

A hankali ya tura kofar ya shiga, ta bayan kofar ya sa hanu ya d'au wata doguwar karfe, kana a hankali yashiga takawa cikin d'aki, yana rarraba ido cikin d'akin.
lungu da sako ya dudduba baiga komai ba.
kasancewar ba wani tarkace bane cikin d'akin. daga
makeken bed and bedside sai wardrobe manne a bango guda TV fridge sai doguwar kujera.
har cikin bathroom ya duba babu komai.
ya dawo cikin d'akin gaban gado ya tsaya, a hankali ya kai hannu ya d'auki pant d'in Feeryal, daya gani tsakiyar gadon,
wan daya tub'e mata ranar.
da alama dai tun bayan korar sa da akayi babu wanda ya shigo d'akin,
ko ma'aikata masu gyaran side d'in su ma basu shigo bedroom d'in sa ba.

Ya d'ago pant d'in yana kare masa kallo, sai kuma da sauri ya mannashi a fuskarsa yana wani irin shinshinarsa, yana wani lullumshe ido.
Ajeemal da shigowar sa kenan zai wuce bedroom d'in sa, ya hango kofar Zaraddin a bud'e, ya karaso bakin kofar.
can ya hangosa tsaye da abin da yake yi.

Da mamaki Ajeemal ke kallon sa, har ya karaso cikin d'akin Zaraddin bai san ya shigo ba, ya shagala da abun da yake yi.
"Zaraddin."
Ajeemal yakira sunan sa.
da sauri ya ware idanunsa tare da cire pant d'in a fuskarsa ya yi baya da hanun sa ya b'oye shi ta bayan sa.

"Kace baka cire mata pant ba, ta ya akayi wannan yazo nan?."
Ajeemal ya yi maganar yana kamo hannunsa daya b'oye ta bayansa.
da karfi Zaraddin ya fisge hannusa yana hararar sa
"Sai kuma aka ce maka nata ne wannan d'in, to sayowa nayi."
kai Ajeemal ya girgiza sannan ya ce
"Sabo da ka koma mace shiyasa ka siyo pant dan ka rika sakawa ba, Zaraddin kabi a sannu dai."
"Anki a bi a sannun idan nabi da gudun ma me ya dame ka."
kafad'a Ajeemal ya d'aga
"Babu ruwa na life d'in ka ne, amma abun bakin cikin dole a danganta ka da mu."
"To ku san yadda zakuyi ku goge hakan mana."

"Rabu dashi Ajeemal zo mu tafi ga Faisal can a mota mu yake jira, badai ka mance 9:30 zamu shiga class ba."
cewar Shamsuddin yana karasowa bakin kofar bedroom d'in.
yaci gaba da fad'in
"Duk wanda ya yi na gari ai don kansa duniya ce ai gashi ga ita, ta ishe sa riga da wando,
ba sai ya siyo pant d'in sawa ba, zo mu tafi kar muyi latti."
Shamsuddin ya juya Ajeemal yabi bayansa.

Zaraddin yabi bayansu da harara tare da jan tsaki
"Mttss munafukan banza kawai."

Ya fito parlour ya samo laida ya kulle pant d'in ciki yaje ya jefa sa cikin dosbin.
kana ya koma bedroom d'in sa ya wuce bathroom domin yin wanka.

Tun da Aunty ta sami labarin dawowar Zaraddin takuma tsananta tsaro wa Feeryal.
ko da aka gama hutu suka koma makaranta, duk safiyar Allah idan lokacin tafiya makaranta ya yi ita ke fita ta kaita mota da kanta, sai ta tabbatar da sun bar gidan kafin ta koma,
lokacin dawowar su nayi kuwa zata fito ta tsaya har sai taga shigowar su ta kama d'iyarta su shige ciki.

Wannan ke nan.

A can cikin fadar sarkin aljanu.
sarki aljani Matip ne hakimce a kan karagarsa,
ya yin da fadawarsa ke zagaye da shi.
wasu kyawawan yara mata ne guda biyu ke zaune a gefe da gefen sa,
kan wasu kujeru masu tsananin walkiya.
waziri Kutup ya d'ago da dubansa daga kan wani makeken madubi dake ta juyayi kamar ruwa.
ya dubi sarki Matip yana fad'in
"Ya shugaba na, ga dukkan alamu tana cikin koshin lafiya, da kulawar daya dace, babu wani abin cutarwar da yake dumfarota a yanzu."
kai sarki aljani Matip ya jijjiga sannan ya ce
"Akwai kalubale a gaba mai tarin yawa cikin rayuwar ta lokaci baiyi ba tukun,
amma sai dai bayan mu akwai wani wanda zai bayyana zata kuma sami kariyar daya dace feye da wanda muke bata."
kasa waziri Kutub ya yi da kansa ya ce
"Ya shugaba na shin akwai wani wanda zai bayyana ya bata kariyar kwatankwacin irin wanda muke bata."
sarki aljani Matip ya jijjiga kai
"Kwaraikuwa akwai shi zai yayyana."
"A jinsinmu ko a jinsin bil'adama?."
yakuma jefo masa tambayar.
sarki aljani Matip ya gyara zaman sa sannan ya ce
"A jinsin bil'adama zai bayyana, shi babban kariya ne a gare ta."

Wasiri Kutub ya jinjina kai yana mai makikin girman isa irin na wannan bil'adama da har zai fisu bata kariya wanda su duk motsinta tamkar a kan idanunsu yake.
ya ce
"Wani hukunci ne za'ayi wa yaron da ya nimi cutar da ita."
sarki aljani Matip ya ce
"Sa'ar sa guda da ya yi amfani da duhu ba a haske ba, da yayi kokarin cimma burinsa a haske ne da mun makantar da shi, a barshi a iya tsoratarwar da akayi masa, gaba idan bai kiyaye ba zamu waiwaye sa,
a kirawo Tarmuzu yanzun nan."
Chapter 20 · 0% Book details