Sashe 46
Feeryal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daddy ne zaune a parlour'n Abba bayan sunyi sallama da ba'i mazan da suka zo wa Abba jaje.
Daddy ya gyara zama tare da duban agogon hannunsa, kana ya dubi Abba sannan ya ce
"Alhaji mu zamu wuce zamubi jirgin karfe 7, gashi har 6 ta kusa."
"Ah wai yau ne zaku tafin inace sai gobe, ai yanzu dare zatayi, da ka bari zuwa gobe dai."
"Babu ko mai zamu wuce yau har an shirya mana tafiya karfe 7."
"To shike nan bari nayi musu magana zanyi kewar amaryata, amma fa daga zaran komai ya lafa zaka dawo min da ita,
amma wani hanzari ba gudu ba, ya zakayi da Hajiyar ka, kana ganin babu matsala komawar nata can,
ko dai zanyi magana da Aliyu ne a kaita can kasar Lebanon, in yaso zuwa jibi angama shirya mata komai sai ta tafi."
Daddy ya ce
"Babu komai insha'allah zanji da komai baza'a sami wata matsala ba in Allah ya yarda."
"To Allah ya sa, in dai kaga hakan zai janyo wata matsalar to barin kasar natama gaba d'aya zaifi bata tsaro."
Abba ya fad'a yana mikewa ya nufi b'angaren Hajja Umma.
Tun da FEERYAL ta sami labarin zasu tafi da Daddy yanzu, tarika sakin murmushi.
dan dama tun da ta dawo gidan, hankalin ta sam baya kwance, gani take kamar b'arayen nan zasu kuma dawowa cikin daren yau,
bugu da kari kuma dama tana so taga Ammie'n ta, da suka shafi shekaru goma sha, basu zauna sun jima tare ba.
dan ko Aunty tazo Lagos baifi tayi kwana uku biyu ta koma ba.
Hajja Umma da Maryam suka had'a mata kayanta, kasancewar ba komawa duka zatayi ba iya manyan akwatuna biyu suka cika mata.
Duk suka fito musu rakiya jikin motar kamfanin Daddy daya zo d'aukar su.
Hajja Umma tana ta zolayar FEERYAL wai tayi ta tafi dama so take ta tafi ta bar mata mijinta.
a gefe guda kuwa sam basuso ta kauce a cikin su ba, sai dai hakan ce hanyar da ta dace dan su ketarar da ita daga gudun kuma fad'awa wata hatsari, tun da har hukuma da kansu sunce ta kauce a cikin garin.
sannan ita kanta yarinyar zatafi samin nutsuwa ne idan ta kauce na d'an wani lokaci daga inda abin ya faru.
Maryam ta rungume FEERYAL tana hawaye, tambas zatayi kewarta tun da tazo gidan bata tab'a sa kafarta a guri batare da ita ba.
da kyar ta saketa ta shige mota itama tana hawaye.
su Abba suna d'aga musu hannu direba yaja suka nufi airport..
Karfe 9 da mintuna 30 dai-dai jirgin su ya sauka a Lagos.
inda tuntuni direban Daddy ya iso airport yake jiran saukowarsu.
FEERYAL tarika baza ido, tana tuna wai ta tab'a rayuwa a garin duk da bata da wayo sosai lokacin,
sai dai kwakwalwar yaro takan tuna wasu abin tsinta-tsinta ba duka ba kam.
Daddy yad'an zuba mata ido ya lura da tashiga tunani tun sanda suka sauko a jirgi, sai ya yi ta janta da hira yana nuna mata hanyoyi da tambayarta tasan nan ta san can.
kai kawai ta girgiza masa da alama bata fa gane ko ina ba.
suna isa direba ya yi hon security suka bud'e masa get.
direct part d'in Aunty ya nufa kamar yadda Daddy ya umurce sa.
ya yi hon bakin get d'in side d'in mai gadin kofar ya bud'e.
Aunty na tsaye a tsakiyar farfajiya suka karaso, da sauri ta isa ta bud'e gefen da FEERYAL take
ta fito suka rungume juna, cike da farincikin ganin juna.
Daddy yana ta yi musu dariya, ya ce
"Ya yi kyau Fad'imatu ita kad'ai kika sani ko,
ni an share ni."
sai sannan ta sake ta ta rungume shi tana fad'in
"Ayya Daddy na jima ban ganta bane."
"To gashi nan na kawo miki d'iyarki."
"Nagode Daddy."
ta fad'a tana dad'a rungume shi.
Aunty ta ja hannun Daddy dana FEERYAL suka shige ciki, direba ya kwaso kayan ya biyo su da shi.
D'akin FEERYAL na tun da Aunty ta shige da ita,
in da shi kuma Daddy ya wuce bedroom d'in Aunty, domin ya d'an watsa ruwa.
a bakin kofar d'akin direba ya aje akwatin, Aunty ta kwaso ta shigo da su ciki.
FEERYAL tana ta bin d'akin da kallo wanda yake a gyare tsaf sai kamshi yake.
tana ganin d'akin tun da a idon kuruciya,
ga komai na wasanta a ciki har yanzu.
da sauri ta isa inda babyn wasan ta yake ta d'auka ta sunbace ta tana sakin murmushi.
Aunty tana kallonta cike da jindad'i ta ce
"Kin tuna da 'yar tsanan, ki ko."
murmushi tayi tana rungume babyn ta ce
"Na tuna Ammie."
Aunty baki yaki rufuwa taga d'iyarta, a b'angaren FEERYAL ma haka abin yake, farincikinta bazai fad'u ba.
Bayan Aunty tasa FEERYAL tayi wanka dan ta rage gajiya,
suka fito parkour dan sun rigada sun yi sallar su tun a jirgi.
suka yada zangonsu a parlour,
Daddy ya fito ya same su.
abinci Aunty ta kawo musu kala-kala, har da cake da yoghurt dan tasan abincin da tafi so ke nan.
aiko bataci komai sai sai cake da yoghurt d'in.
Aunty ta d'auke plt d'in cake a gabanta ta ce
"Sa hanu kici abinci, har yanzu baki dai na cin wannan abin da bazai koshar da ke d'in nan ba ko."
kai ta langwab'ar gefe.
Daddy ya ce
"Ajiye mata taci kayanta, in da bata koshi ai bazata ci ba."
aiko ta saki murmushin jin dad'i, Aunty ta girgiza kai tana sakar mata hararar wasa.
Sun jima sosai suna hirar yaushe gamo sai da Daddy ya ce FEERYAL taje ta kwanta ganin tana ta sauke hamma..
Washegari da sassafe Daddy ya yi sammakon zuwa gurin Hajiya.
kai tsaye bedroom d'in ta ya wuce, ya tadda ita zaune tana shafa maganin ciwon kafa, a gwuiwarta.
ya sami guri ya zauna kan kujera ya shiga gaisheta ta amsa tana fad'in
"Jiya ban gankaba wannan yaron Ajimi yake ce min wai yanaga tafiya kayi."
"Am..Eh d'an tafiya nayi bamai nisa ba,
amma Hajiya kafar tana damin ki ne da yawa haka?."
"Wlh kwana biyun nan kafar tana d'an tab'ani amma ina shafa wannan maganin sai naji kafar tamin wasai."
"Ai ban sani ba Hajiya da an koma asibiti."
"Ai tun ranar da kafar ta tashi mukayi waya da
abokin turawa, nake fad'a masa yadda yake min ya ce wa Ajimi yaje ya siyo min wannan maganin,
ya ce kullum safiya da maraice narika shafashi,
shike nan na nimi ciwon na rasa,
ni har zan aje maganin ma danaji na warke shi ya ce kar na aje nacigaba da shafawa har sai ya kare."
Daddy ya ce
"To Allah ya sauwaka ya kara lafiya Hajiya."
Ido Hajiya ta zubawa TV dake aiki cikin d'akin tana mara baki,
a b'angaren Daddy shima hankalin sa ya maida kan TV jin labaran da suke watsawa.
Hajiya ta tab'e baki tana fad'in
"Tun jiya labarannan kad'ai akeyi,
ni kamar naji ance gidan Alhaji Tahir Abbas ne b'arayin suka shiga, basu tafi da 'yar da suka sace ba a ka kamasu,
Tahir Abbas d'in nan ba shine surukinka ba?."
Daddy ya ce
"Eh shine mahaifin Fad'imatu ne, Allah ya takaita ma basu tafi da ita ba, mutumin yana da had'ari sosai lalata yara yake daga bisani ya sako su wasu da ciki wasu da goyo."
Hajiya ta ware ido ta dafe kirji
"Kai wannan anyi mugun matsiyaci, wasayyahu ya tsaya masa acan, Allah kare kikokin mu,
amma dai an bincika baiyiwa yarinyar komai ba ko,
dan irin su basa d'aukar asara biyu,
idan yaga alamun fa ya shiga hanu bayada mafaka,
zai iya aiwatar da mugun nufinsa a kan ta kar ya yi biyu babu,
banaji suna fad'in yarinyar tana asibiti ba."
Daddy ya ce
"Amin ya Allah da sauran yara baki d'aya, beyi mata komai ba, ta firgita da lamarin ne shine ta suma aka kaita asibiti,
Hajiya yarinyar nan ce fa FEERYAL wacce ta zauna nan gurin Fad'imatu ita sukayi kokarin sacewar."
Hajiya ta gyara zama da mamaki ta ce
"To..too wacce 'yar kenan ohoo kace aljanar can, dama tana gurin su ashe, yoo ai da sun tafi da ita dama an rage mugun iri,
irin su kam da ma mene ne gaiyan tsiya gayyan fitina a guri,
to ina ga irin ta duk irin abin da nake hangowa ke nan,
ai wannan yarinyar zamanta fitina ce a guri, dama sun bari an tafi da ita da an rage mugun iri,
dan ita ce fitinar da ta janyo b'arayi gidan, wa ya sani ma ko baki suka had'a da ita,
azo ayi sata a gidan,
da yanzu gidan nan zata turo mana su,
ashe haka ta shahara ta zamo gaggaruma."
Daddy ya d'anyi shiru yana tunanin ta ina zai fara bi da Hajiya kana ya ce
"Hajiya ba haka bane su wad'an nan 'yanta'addan suna da tawagarsu na musamman, ba wani ke kawo musu kwangila ba su suke aikinsu da kansu suke b'arna a kasa,
duk wacce suka gani ta musu shike nan sai subi dare ko da rana ma suna shiga su d'auko ta sukuma tafi da ita,
Allah dai ya kare mu daga sharrin su yasa karshensu ke nan da aka kama su."
Hajiya ta mara baki tana fad'in
"Hmm to ai shike nan yadai tsaya musu a can."
Daddy ya girgiza kai kawai sannan yad'an gyara zaman sa kana yaci gaba da fad'in
"Hajiya dama wata alfarma nazo nima a gurin ki,
kinga abin da ya farun nan jami'an tsaro sunci a d'aga yarinyar a garin saboda 'yan ta'addan zasu iya zuwa su sace ta,
shine nake niman alfarma a gurinki tazo ta zauna damu nad'an wani lokaci kafin komai ya lafa, hukuma sugama bincike su kama sauran 'yan ta'addan sai ta koma Abuja,
Daddy ya gyara zama tare da duban agogon hannunsa, kana ya dubi Abba sannan ya ce
"Alhaji mu zamu wuce zamubi jirgin karfe 7, gashi har 6 ta kusa."
"Ah wai yau ne zaku tafin inace sai gobe, ai yanzu dare zatayi, da ka bari zuwa gobe dai."
"Babu ko mai zamu wuce yau har an shirya mana tafiya karfe 7."
"To shike nan bari nayi musu magana zanyi kewar amaryata, amma fa daga zaran komai ya lafa zaka dawo min da ita,
amma wani hanzari ba gudu ba, ya zakayi da Hajiyar ka, kana ganin babu matsala komawar nata can,
ko dai zanyi magana da Aliyu ne a kaita can kasar Lebanon, in yaso zuwa jibi angama shirya mata komai sai ta tafi."
Daddy ya ce
"Babu komai insha'allah zanji da komai baza'a sami wata matsala ba in Allah ya yarda."
"To Allah ya sa, in dai kaga hakan zai janyo wata matsalar to barin kasar natama gaba d'aya zaifi bata tsaro."
Abba ya fad'a yana mikewa ya nufi b'angaren Hajja Umma.
Tun da FEERYAL ta sami labarin zasu tafi da Daddy yanzu, tarika sakin murmushi.
dan dama tun da ta dawo gidan, hankalin ta sam baya kwance, gani take kamar b'arayen nan zasu kuma dawowa cikin daren yau,
bugu da kari kuma dama tana so taga Ammie'n ta, da suka shafi shekaru goma sha, basu zauna sun jima tare ba.
dan ko Aunty tazo Lagos baifi tayi kwana uku biyu ta koma ba.
Hajja Umma da Maryam suka had'a mata kayanta, kasancewar ba komawa duka zatayi ba iya manyan akwatuna biyu suka cika mata.
Duk suka fito musu rakiya jikin motar kamfanin Daddy daya zo d'aukar su.
Hajja Umma tana ta zolayar FEERYAL wai tayi ta tafi dama so take ta tafi ta bar mata mijinta.
a gefe guda kuwa sam basuso ta kauce a cikin su ba, sai dai hakan ce hanyar da ta dace dan su ketarar da ita daga gudun kuma fad'awa wata hatsari, tun da har hukuma da kansu sunce ta kauce a cikin garin.
sannan ita kanta yarinyar zatafi samin nutsuwa ne idan ta kauce na d'an wani lokaci daga inda abin ya faru.
Maryam ta rungume FEERYAL tana hawaye, tambas zatayi kewarta tun da tazo gidan bata tab'a sa kafarta a guri batare da ita ba.
da kyar ta saketa ta shige mota itama tana hawaye.
su Abba suna d'aga musu hannu direba yaja suka nufi airport..
Karfe 9 da mintuna 30 dai-dai jirgin su ya sauka a Lagos.
inda tuntuni direban Daddy ya iso airport yake jiran saukowarsu.
FEERYAL tarika baza ido, tana tuna wai ta tab'a rayuwa a garin duk da bata da wayo sosai lokacin,
sai dai kwakwalwar yaro takan tuna wasu abin tsinta-tsinta ba duka ba kam.
Daddy yad'an zuba mata ido ya lura da tashiga tunani tun sanda suka sauko a jirgi, sai ya yi ta janta da hira yana nuna mata hanyoyi da tambayarta tasan nan ta san can.
kai kawai ta girgiza masa da alama bata fa gane ko ina ba.
suna isa direba ya yi hon security suka bud'e masa get.
direct part d'in Aunty ya nufa kamar yadda Daddy ya umurce sa.
ya yi hon bakin get d'in side d'in mai gadin kofar ya bud'e.
Aunty na tsaye a tsakiyar farfajiya suka karaso, da sauri ta isa ta bud'e gefen da FEERYAL take
ta fito suka rungume juna, cike da farincikin ganin juna.
Daddy yana ta yi musu dariya, ya ce
"Ya yi kyau Fad'imatu ita kad'ai kika sani ko,
ni an share ni."
sai sannan ta sake ta ta rungume shi tana fad'in
"Ayya Daddy na jima ban ganta bane."
"To gashi nan na kawo miki d'iyarki."
"Nagode Daddy."
ta fad'a tana dad'a rungume shi.
Aunty ta ja hannun Daddy dana FEERYAL suka shige ciki, direba ya kwaso kayan ya biyo su da shi.
D'akin FEERYAL na tun da Aunty ta shige da ita,
in da shi kuma Daddy ya wuce bedroom d'in Aunty, domin ya d'an watsa ruwa.
a bakin kofar d'akin direba ya aje akwatin, Aunty ta kwaso ta shigo da su ciki.
FEERYAL tana ta bin d'akin da kallo wanda yake a gyare tsaf sai kamshi yake.
tana ganin d'akin tun da a idon kuruciya,
ga komai na wasanta a ciki har yanzu.
da sauri ta isa inda babyn wasan ta yake ta d'auka ta sunbace ta tana sakin murmushi.
Aunty tana kallonta cike da jindad'i ta ce
"Kin tuna da 'yar tsanan, ki ko."
murmushi tayi tana rungume babyn ta ce
"Na tuna Ammie."
Aunty baki yaki rufuwa taga d'iyarta, a b'angaren FEERYAL ma haka abin yake, farincikinta bazai fad'u ba.
Bayan Aunty tasa FEERYAL tayi wanka dan ta rage gajiya,
suka fito parkour dan sun rigada sun yi sallar su tun a jirgi.
suka yada zangonsu a parlour,
Daddy ya fito ya same su.
abinci Aunty ta kawo musu kala-kala, har da cake da yoghurt dan tasan abincin da tafi so ke nan.
aiko bataci komai sai sai cake da yoghurt d'in.
Aunty ta d'auke plt d'in cake a gabanta ta ce
"Sa hanu kici abinci, har yanzu baki dai na cin wannan abin da bazai koshar da ke d'in nan ba ko."
kai ta langwab'ar gefe.
Daddy ya ce
"Ajiye mata taci kayanta, in da bata koshi ai bazata ci ba."
aiko ta saki murmushin jin dad'i, Aunty ta girgiza kai tana sakar mata hararar wasa.
Sun jima sosai suna hirar yaushe gamo sai da Daddy ya ce FEERYAL taje ta kwanta ganin tana ta sauke hamma..
Washegari da sassafe Daddy ya yi sammakon zuwa gurin Hajiya.
kai tsaye bedroom d'in ta ya wuce, ya tadda ita zaune tana shafa maganin ciwon kafa, a gwuiwarta.
ya sami guri ya zauna kan kujera ya shiga gaisheta ta amsa tana fad'in
"Jiya ban gankaba wannan yaron Ajimi yake ce min wai yanaga tafiya kayi."
"Am..Eh d'an tafiya nayi bamai nisa ba,
amma Hajiya kafar tana damin ki ne da yawa haka?."
"Wlh kwana biyun nan kafar tana d'an tab'ani amma ina shafa wannan maganin sai naji kafar tamin wasai."
"Ai ban sani ba Hajiya da an koma asibiti."
"Ai tun ranar da kafar ta tashi mukayi waya da
abokin turawa, nake fad'a masa yadda yake min ya ce wa Ajimi yaje ya siyo min wannan maganin,
ya ce kullum safiya da maraice narika shafashi,
shike nan na nimi ciwon na rasa,
ni har zan aje maganin ma danaji na warke shi ya ce kar na aje nacigaba da shafawa har sai ya kare."
Daddy ya ce
"To Allah ya sauwaka ya kara lafiya Hajiya."
Ido Hajiya ta zubawa TV dake aiki cikin d'akin tana mara baki,
a b'angaren Daddy shima hankalin sa ya maida kan TV jin labaran da suke watsawa.
Hajiya ta tab'e baki tana fad'in
"Tun jiya labarannan kad'ai akeyi,
ni kamar naji ance gidan Alhaji Tahir Abbas ne b'arayin suka shiga, basu tafi da 'yar da suka sace ba a ka kamasu,
Tahir Abbas d'in nan ba shine surukinka ba?."
Daddy ya ce
"Eh shine mahaifin Fad'imatu ne, Allah ya takaita ma basu tafi da ita ba, mutumin yana da had'ari sosai lalata yara yake daga bisani ya sako su wasu da ciki wasu da goyo."
Hajiya ta ware ido ta dafe kirji
"Kai wannan anyi mugun matsiyaci, wasayyahu ya tsaya masa acan, Allah kare kikokin mu,
amma dai an bincika baiyiwa yarinyar komai ba ko,
dan irin su basa d'aukar asara biyu,
idan yaga alamun fa ya shiga hanu bayada mafaka,
zai iya aiwatar da mugun nufinsa a kan ta kar ya yi biyu babu,
banaji suna fad'in yarinyar tana asibiti ba."
Daddy ya ce
"Amin ya Allah da sauran yara baki d'aya, beyi mata komai ba, ta firgita da lamarin ne shine ta suma aka kaita asibiti,
Hajiya yarinyar nan ce fa FEERYAL wacce ta zauna nan gurin Fad'imatu ita sukayi kokarin sacewar."
Hajiya ta gyara zama da mamaki ta ce
"To..too wacce 'yar kenan ohoo kace aljanar can, dama tana gurin su ashe, yoo ai da sun tafi da ita dama an rage mugun iri,
irin su kam da ma mene ne gaiyan tsiya gayyan fitina a guri,
to ina ga irin ta duk irin abin da nake hangowa ke nan,
ai wannan yarinyar zamanta fitina ce a guri, dama sun bari an tafi da ita da an rage mugun iri,
dan ita ce fitinar da ta janyo b'arayi gidan, wa ya sani ma ko baki suka had'a da ita,
azo ayi sata a gidan,
da yanzu gidan nan zata turo mana su,
ashe haka ta shahara ta zamo gaggaruma."
Daddy ya d'anyi shiru yana tunanin ta ina zai fara bi da Hajiya kana ya ce
"Hajiya ba haka bane su wad'an nan 'yanta'addan suna da tawagarsu na musamman, ba wani ke kawo musu kwangila ba su suke aikinsu da kansu suke b'arna a kasa,
duk wacce suka gani ta musu shike nan sai subi dare ko da rana ma suna shiga su d'auko ta sukuma tafi da ita,
Allah dai ya kare mu daga sharrin su yasa karshensu ke nan da aka kama su."
Hajiya ta mara baki tana fad'in
"Hmm to ai shike nan yadai tsaya musu a can."
Daddy ya girgiza kai kawai sannan yad'an gyara zaman sa kana yaci gaba da fad'in
"Hajiya dama wata alfarma nazo nima a gurin ki,
kinga abin da ya farun nan jami'an tsaro sunci a d'aga yarinyar a garin saboda 'yan ta'addan zasu iya zuwa su sace ta,
shine nake niman alfarma a gurinki tazo ta zauna damu nad'an wani lokaci kafin komai ya lafa, hukuma sugama bincike su kama sauran 'yan ta'addan sai ta koma Abuja,