Sashe 30
Feeryal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Satin Hajiya guda ke nan tana zaune tana jinyar kafa,
har kuma yanzu Daddy bai dawo ba yana can kasar China,yana gudanar da wasu harkokin sa.
sai dai kullum suna video call yana ganin yanayin jikin nata.
duk da cuwon dake jikin Hajiya baisa ta saduda ba,
tana daga zaune tana bada umurni da oda.
haka ta kekashe kasa ta hana a rika d'aukar Feeryal a motar kaisu school, takuma sa dole Daddy ya canza musu wata mota yana can kasar bai dawo ba,
a cewar ta wai akwai abu a ciki tun da Feeryal ta shiga.
Ajeemal ne ke kai ta school a motar sa, wani lokacin ya jirata har su tashi idan bashi da abin da zaiyi, wani lokacin kuma ya ajeta yaje ya dawo ya d'auke ta.
baya tab'a bari Zaraddin ya kaita ko ya d'aukota, ko baya da lokaci, yakan iya kashe damuwar sa wajen kaita da d'auko ta,
sau d'aya yatab'a sa Shamsuddin da Faisal suka tab'a d'aukota, ranar d'in ma yana class ne bai fito ba, dan su yana da d'an tabbacin nutsuwa tare da su.
Aunty na kichin tana aiki Feeryal da ta dawo daga school ta shigo.
ta fad'a jikin ta,
Aunty tayi murmushi ta rungume ta tana fad'in
"Oyoyo 'yanmatan Ammie, an dawo ya school?."
d'an karamin bakin ta ta cuno cikin tsiririyar muryarta mai fita da yanayin shagwab'a ta ce
"Ammie wai ba ke kika haife ni ba?."
hannu takai ta toshe bakin ta,
sannan ta waro ido ta ce
"Inji wa? ni na haife ki Feeryal duk wanda ya fad'a miki yafad'a ne kawai, kar ki yadda ki sawa ranki hakan,
to idan ba ni na gaife ki ba to waya haife ki, ko akwai wata mamarki ce a gidan nan?."
kai ta girzaza tana kallon fuskar Aunty.
kumatun ta taja ta ce
"Ko in kaiki gurin wata ce tazamo mamarki tun da kin gaji da ni."
da sauri ta fad'a jikin ta tana cewa
"O'o Ammie ni dai bazanje ba."
dariya Aunty taji ta dad'a rungume ta tana jin kaunarta cikin zuciyar ta.
baki ta kuma cunowa ta ce
"Basu Ameerah bace suke fad'a, wai ke ba ce mamata ba ce kuma Daddy ma ba babana bane, wai ni mayyar aljana ce."
da sauri Aunty ta ce
"Karya suke ni ce nan mamarki Daddy kuma baban ki, kar ki sake biye musu,
oya je ki cire uniform kiyi wanka kizo, ko nazo nayi miki."
kafad'a ta make
"A'a ni zanyi Ammie Miemie tana min dari ta ce wai har yanzu ana min wanka."
"To in banda Miemie ai itace gaba da ke, in ita ta iya ke da sauran ki."
"Ni dai Ammie na iya nima."
"To je jiyi yanzu anjima da daddare da kaina zan miki."
ta juya da sassarfa tayi ta fice a kichin d'in..
Hajiya ce kwance a kan makeken gadon ta tana sharara bacci sai gwarti take saukewa.
daga cikin bacci taji ana kiran sunan ta, ana jajjan kafafunta.
A firgice ta mike tana fad'in
"Wayyooo ni Hanne nayi mugun ji, waye waye anan, Bishira wane ne?."
ta lalub'o makunni wuta dake d'aure a kan bedside ta kunna.
d'akin ya bada haske ba mai yawa ba.
can kuma hasken ya soma karuwa da kansa, yayi wani irin bau ya haske d'akin gaba d'aya lokaci guda.
a take kuma d'akin yasoma amsakuwar magana had'e da tafi tamkar ana gad'a cikin d'akin.
ga wasu irin maganganu barkatai wannan nayi wancan nayi fad'i a ke
"Hajiyaaaa taso muyi gad'a, taso ke ce da shiga fili yanzuuu."
Hajiya da fitsari ke kokarin kwace mata sabar azabebben tsoro tashiga fad'in
"To to laaaha'ilaaaha'illallahu, wasayyahu wasayyahu wasayyahuuu, li'eelafiiiikuraishin,
dan girman Allah kuyihakuri wlh lalurar ido gare ni, ga kwab'ewar gwuiwa, ta ina zan fara,
kuyi min rai."
"Bafa zamu kyale ki ba ke ce da shiga fili taso ki fad'o mu cab'e."
Hajiya ta kwalala uban ihu
"Wayyo Allah jama'a ku kawo min d'auki yaukam nayi gamo,
dan Allah dan ma'aiki Rasulullahi nagama ku da Allah kui hakuri ku kyale ni,
ta ina zan fad'o bana ganin ku, tun zamanin yaranta rabon da nayi gad'a,
wlh babu kafar yin gad'a kuyi hakuri kuje gurin masu kafa."
"Dole ki taso Hajiyaaa ko mu d'aga ki, kuyi sama da ke."
Ba sai ga Hajiya ta mike da kafafunta ba, dama tun sati biyu aka ce ta gwada takawa ta ki ta ce wai da saura tukun guiwar bata gama had'ewa ba.
"Ku taro ta zata gudu."
tuni Hajiya ta saki fitsari, jiki na kakkarwa ta nufi kofa fitsari na zuba,
kafin ta isa kofar ta bud'e tazo daf zata fice kofar yakuma kullewa garamm.
Hajiya tayi dakuwan 'yan bori a kasa, daram da d'uwawu.
ta rufe idanunta gam tana fad'in.
"Yasin kafa dubu, li'eelafi kafa bakwai, lakadija'akum kafa d'ari ba d'aya,
yasin me manjagara yakwasheku ya zubdaku can kuyi nesa ku tsaya a can, wasayyahuuu wasayyahuuu ku tsaya a can laaaa'ilaaaha'illahu,
aniya bi aniya aniya bi aniya, fatiha da salatin annabi."
Ji kake kuuu cikin Hajiya na bada sauti, tsoro iya tsoro firgici iya firgici a tare da Hajiya.
sai ihu da kwalala take kamar makogoron ta zai fita.
A tare Hajiya Bishira da Kulu suka fito daga d'akunan su, suna rige-rigen shi ga d'akin Hajiya.
a bakin kofa suka ganta tayi zaman dirshem tana kwarara ihu.
duk sukayi kanta suna had'a baki wajen fad'in
"Lafiya Hajiya me yafaru, ciwon kafar ce ta motsa? subhanalillahi!."
Jin moryoyin Hajiya Bishira da kulu yasa Hajiya bud'e idanunta.
ta kankame kafafunsu kad'an yarage ta zubar da su kasa.
Hajiya Bishira ta kara hasken d'akin ta hanyar kunna makunnin koyayen wutan da sukayi wa tsakiyar p.o.p d'akin kawanya,
tamkar kwalliya ta sama.
d'akin yabada haske sosai tamkar tsakiyar rana.
Hajiya tashiga binsu da kallo da alama dai yanzu ne ta dawo cikin hayyacin ta.
Hajiya ki sake mu kar ki yardamu a kanki."
cewar Bishira tana janye kafafun ta daga rukon da tayi musu.
cikin sauke numfashi'n tsoro irin wanda mutum ya kub'uta daga azaba Hajiya ta ce
"Nayi gamo gamo nayi da bakaken aljanu, ku kaini bayan gida ciki na ya rud'e."
"Hajiya wa ya kawo ki nan to ke da ba tafiya kike ba?."
cewar Kulu tana rike hab'a.
"Ban san ya akayi nazo nan ba ina ga su suka kawo ni, ke da'alla kamani ku kaini masai ko sai nayi anan nabar muku aiki."
Suka tallafe ta ta mike Hajiya ta d'aga kafa tana d'ingisawa.
"Hajiya kin warke ashe."
Kulu ta fad'a tana bin kafarta da kallo sai kuma ta waro ido
"Me zan gani Hajiya fitsari kamar kikayi a zaune."
"Har uwar fitsari ma zanyi a nan in ya kama,
da'alla ku kaini bayi na matsu."
Hajiya Bishira ta bi gurin da kallo tambas fitsari ne tun daga bakin gado har zuwa inda suka same ta zaune.
Suna kaita bayi ta sunkuya gudawa daya murd'e ta, zasu fita su bata guri, ta ce babu wan da ya isa ya fita su jirata sai ta gama.
Suna fito da ita takuma cewa su koma tana jin wani.
sai da ta shiga bayi sau biyar a kai a kai.
Tana zaune a bakin gado tana sauke numfashi, su Hajiya Bishira da suka gama tsaftace cikin d'akin da sarkake shi,
suka dawo inda take suna yi mata sannu.
Kulu ta dube ta tana fad'in
"Sannu Hajiya dare d'aya har kin zabge, wai ya akayi mu bamuga bakaken aljanun ba sai ke, ta ina suka shigo ne, ko dai mafarki kika yi,
anya ba mayu ke bibiyar ki ba kuwa?."
"Uhum ke dai bari Kulu ko ta sama ko ta kasa sai Allah, ina bacci narika jin ana kira na, da na amsa kiran da sun tafi da ni, kin san ba'a amsa kiran dare kana amsawa to ka tafi ke nan,
yazama dole a sawa gidan nan kafi, tun ba yau ba nake fad'awa Abubakar ya sa kafi a gidan nan sabo da miyagu yaki ji, to ba ga irin ta ba da babu wani mugun da zai iya shigowa gidan nan, kota sama ko ta kasa ko a b'oye ko a bayyane,
badun nayi ta addu'a ina ja musu yasin ina sauke wa ba da sun tafi da ni."
D'ip Hajiya tayi jin motsi karkashin gado ta kankame su Kulu ta na fad'in
"Yasin kafa dubu li'eelafi kafa bakwai lakadija'akum kafa d'ari ba d'aya fatiha da salatin annabi wasayyahuuuu."
Hajiyq Bishira ta ce
"Hajiya bafa komai kinga ni kyanwarki ce gata can fa, magen ki ce a kasan gado taga haske ta fito."
"Kin tabbata mage ce."
Hajiya ta fad'a tana zazzare ido.
"Itace ba gata nan ba ta fito, watakila ma ita ce ta razane ki d'azu."
"Um-um ba ita ba ce magana naji bilhakki, kyanwa tana maga ne."
"Hajiya in zaki kwanta kirika addu'a, babu abin da zai same ki insha'allahu."
"Ai ni yau naga karfin addu'a baki ji yanzu ma nayi ba, ai addu'a tana da amfani yana kora miyagu."
"Ai Hajiya wannan da kikayi yanzu ba addu'a ba ce, ki karanta shi a karance ba ki fad'a irin yadda kika fad'i yanzu ba,
ayatul'kursiyu da suratul iklas da falaki da nasi, a duk sanda zaki kwanta ki karantasu sun'ishe ki komai da komai,
zasu karake daga sharrin komai."
Hajiya ta mara baki tana fad'in
"Ahaf wannan addu'ar da kike gani tun muna yawo da jajayen sawu muke ganin amfanin sa, duk shi mukeyi da kawayen mu, muyi fad'a da uban kowa mu kwana lafiya, ai ko munga amfanin sa."
Hajiya Bishira ta girgiza kai tana fad'in
"Allah shi kyauta."
Sun so tafiya d'akunan su Hajiya ta ce sai dai fa su zauna su waye gari anan tun da gari yakusa waye wa.
Washegari Hajiya ta d'agawa Daddy hankali a waya wai sai dai yadawo yanimo kafi a sa a gidan, miyagu nason ganin bayan su.
ya ce mata to yakusa dawowa.
Shirye-shiryen bikin Farida nadad'a matsowa.
uwar amarya Mommy ba zama.
anata kai kawo yadda biki zai gudana baza aji kunyar kawaye ba.
har kuma yanzu Daddy bai dawo ba yana can kasar China,yana gudanar da wasu harkokin sa.
sai dai kullum suna video call yana ganin yanayin jikin nata.
duk da cuwon dake jikin Hajiya baisa ta saduda ba,
tana daga zaune tana bada umurni da oda.
haka ta kekashe kasa ta hana a rika d'aukar Feeryal a motar kaisu school, takuma sa dole Daddy ya canza musu wata mota yana can kasar bai dawo ba,
a cewar ta wai akwai abu a ciki tun da Feeryal ta shiga.
Ajeemal ne ke kai ta school a motar sa, wani lokacin ya jirata har su tashi idan bashi da abin da zaiyi, wani lokacin kuma ya ajeta yaje ya dawo ya d'auke ta.
baya tab'a bari Zaraddin ya kaita ko ya d'aukota, ko baya da lokaci, yakan iya kashe damuwar sa wajen kaita da d'auko ta,
sau d'aya yatab'a sa Shamsuddin da Faisal suka tab'a d'aukota, ranar d'in ma yana class ne bai fito ba, dan su yana da d'an tabbacin nutsuwa tare da su.
Aunty na kichin tana aiki Feeryal da ta dawo daga school ta shigo.
ta fad'a jikin ta,
Aunty tayi murmushi ta rungume ta tana fad'in
"Oyoyo 'yanmatan Ammie, an dawo ya school?."
d'an karamin bakin ta ta cuno cikin tsiririyar muryarta mai fita da yanayin shagwab'a ta ce
"Ammie wai ba ke kika haife ni ba?."
hannu takai ta toshe bakin ta,
sannan ta waro ido ta ce
"Inji wa? ni na haife ki Feeryal duk wanda ya fad'a miki yafad'a ne kawai, kar ki yadda ki sawa ranki hakan,
to idan ba ni na gaife ki ba to waya haife ki, ko akwai wata mamarki ce a gidan nan?."
kai ta girzaza tana kallon fuskar Aunty.
kumatun ta taja ta ce
"Ko in kaiki gurin wata ce tazamo mamarki tun da kin gaji da ni."
da sauri ta fad'a jikin ta tana cewa
"O'o Ammie ni dai bazanje ba."
dariya Aunty taji ta dad'a rungume ta tana jin kaunarta cikin zuciyar ta.
baki ta kuma cunowa ta ce
"Basu Ameerah bace suke fad'a, wai ke ba ce mamata ba ce kuma Daddy ma ba babana bane, wai ni mayyar aljana ce."
da sauri Aunty ta ce
"Karya suke ni ce nan mamarki Daddy kuma baban ki, kar ki sake biye musu,
oya je ki cire uniform kiyi wanka kizo, ko nazo nayi miki."
kafad'a ta make
"A'a ni zanyi Ammie Miemie tana min dari ta ce wai har yanzu ana min wanka."
"To in banda Miemie ai itace gaba da ke, in ita ta iya ke da sauran ki."
"Ni dai Ammie na iya nima."
"To je jiyi yanzu anjima da daddare da kaina zan miki."
ta juya da sassarfa tayi ta fice a kichin d'in..
Hajiya ce kwance a kan makeken gadon ta tana sharara bacci sai gwarti take saukewa.
daga cikin bacci taji ana kiran sunan ta, ana jajjan kafafunta.
A firgice ta mike tana fad'in
"Wayyooo ni Hanne nayi mugun ji, waye waye anan, Bishira wane ne?."
ta lalub'o makunni wuta dake d'aure a kan bedside ta kunna.
d'akin ya bada haske ba mai yawa ba.
can kuma hasken ya soma karuwa da kansa, yayi wani irin bau ya haske d'akin gaba d'aya lokaci guda.
a take kuma d'akin yasoma amsakuwar magana had'e da tafi tamkar ana gad'a cikin d'akin.
ga wasu irin maganganu barkatai wannan nayi wancan nayi fad'i a ke
"Hajiyaaaa taso muyi gad'a, taso ke ce da shiga fili yanzuuu."
Hajiya da fitsari ke kokarin kwace mata sabar azabebben tsoro tashiga fad'in
"To to laaaha'ilaaaha'illallahu, wasayyahu wasayyahu wasayyahuuu, li'eelafiiiikuraishin,
dan girman Allah kuyihakuri wlh lalurar ido gare ni, ga kwab'ewar gwuiwa, ta ina zan fara,
kuyi min rai."
"Bafa zamu kyale ki ba ke ce da shiga fili taso ki fad'o mu cab'e."
Hajiya ta kwalala uban ihu
"Wayyo Allah jama'a ku kawo min d'auki yaukam nayi gamo,
dan Allah dan ma'aiki Rasulullahi nagama ku da Allah kui hakuri ku kyale ni,
ta ina zan fad'o bana ganin ku, tun zamanin yaranta rabon da nayi gad'a,
wlh babu kafar yin gad'a kuyi hakuri kuje gurin masu kafa."
"Dole ki taso Hajiyaaa ko mu d'aga ki, kuyi sama da ke."
Ba sai ga Hajiya ta mike da kafafunta ba, dama tun sati biyu aka ce ta gwada takawa ta ki ta ce wai da saura tukun guiwar bata gama had'ewa ba.
"Ku taro ta zata gudu."
tuni Hajiya ta saki fitsari, jiki na kakkarwa ta nufi kofa fitsari na zuba,
kafin ta isa kofar ta bud'e tazo daf zata fice kofar yakuma kullewa garamm.
Hajiya tayi dakuwan 'yan bori a kasa, daram da d'uwawu.
ta rufe idanunta gam tana fad'in.
"Yasin kafa dubu, li'eelafi kafa bakwai, lakadija'akum kafa d'ari ba d'aya,
yasin me manjagara yakwasheku ya zubdaku can kuyi nesa ku tsaya a can, wasayyahuuu wasayyahuuu ku tsaya a can laaaa'ilaaaha'illahu,
aniya bi aniya aniya bi aniya, fatiha da salatin annabi."
Ji kake kuuu cikin Hajiya na bada sauti, tsoro iya tsoro firgici iya firgici a tare da Hajiya.
sai ihu da kwalala take kamar makogoron ta zai fita.
A tare Hajiya Bishira da Kulu suka fito daga d'akunan su, suna rige-rigen shi ga d'akin Hajiya.
a bakin kofa suka ganta tayi zaman dirshem tana kwarara ihu.
duk sukayi kanta suna had'a baki wajen fad'in
"Lafiya Hajiya me yafaru, ciwon kafar ce ta motsa? subhanalillahi!."
Jin moryoyin Hajiya Bishira da kulu yasa Hajiya bud'e idanunta.
ta kankame kafafunsu kad'an yarage ta zubar da su kasa.
Hajiya Bishira ta kara hasken d'akin ta hanyar kunna makunnin koyayen wutan da sukayi wa tsakiyar p.o.p d'akin kawanya,
tamkar kwalliya ta sama.
d'akin yabada haske sosai tamkar tsakiyar rana.
Hajiya tashiga binsu da kallo da alama dai yanzu ne ta dawo cikin hayyacin ta.
Hajiya ki sake mu kar ki yardamu a kanki."
cewar Bishira tana janye kafafun ta daga rukon da tayi musu.
cikin sauke numfashi'n tsoro irin wanda mutum ya kub'uta daga azaba Hajiya ta ce
"Nayi gamo gamo nayi da bakaken aljanu, ku kaini bayan gida ciki na ya rud'e."
"Hajiya wa ya kawo ki nan to ke da ba tafiya kike ba?."
cewar Kulu tana rike hab'a.
"Ban san ya akayi nazo nan ba ina ga su suka kawo ni, ke da'alla kamani ku kaini masai ko sai nayi anan nabar muku aiki."
Suka tallafe ta ta mike Hajiya ta d'aga kafa tana d'ingisawa.
"Hajiya kin warke ashe."
Kulu ta fad'a tana bin kafarta da kallo sai kuma ta waro ido
"Me zan gani Hajiya fitsari kamar kikayi a zaune."
"Har uwar fitsari ma zanyi a nan in ya kama,
da'alla ku kaini bayi na matsu."
Hajiya Bishira ta bi gurin da kallo tambas fitsari ne tun daga bakin gado har zuwa inda suka same ta zaune.
Suna kaita bayi ta sunkuya gudawa daya murd'e ta, zasu fita su bata guri, ta ce babu wan da ya isa ya fita su jirata sai ta gama.
Suna fito da ita takuma cewa su koma tana jin wani.
sai da ta shiga bayi sau biyar a kai a kai.
Tana zaune a bakin gado tana sauke numfashi, su Hajiya Bishira da suka gama tsaftace cikin d'akin da sarkake shi,
suka dawo inda take suna yi mata sannu.
Kulu ta dube ta tana fad'in
"Sannu Hajiya dare d'aya har kin zabge, wai ya akayi mu bamuga bakaken aljanun ba sai ke, ta ina suka shigo ne, ko dai mafarki kika yi,
anya ba mayu ke bibiyar ki ba kuwa?."
"Uhum ke dai bari Kulu ko ta sama ko ta kasa sai Allah, ina bacci narika jin ana kira na, da na amsa kiran da sun tafi da ni, kin san ba'a amsa kiran dare kana amsawa to ka tafi ke nan,
yazama dole a sawa gidan nan kafi, tun ba yau ba nake fad'awa Abubakar ya sa kafi a gidan nan sabo da miyagu yaki ji, to ba ga irin ta ba da babu wani mugun da zai iya shigowa gidan nan, kota sama ko ta kasa ko a b'oye ko a bayyane,
badun nayi ta addu'a ina ja musu yasin ina sauke wa ba da sun tafi da ni."
D'ip Hajiya tayi jin motsi karkashin gado ta kankame su Kulu ta na fad'in
"Yasin kafa dubu li'eelafi kafa bakwai lakadija'akum kafa d'ari ba d'aya fatiha da salatin annabi wasayyahuuuu."
Hajiyq Bishira ta ce
"Hajiya bafa komai kinga ni kyanwarki ce gata can fa, magen ki ce a kasan gado taga haske ta fito."
"Kin tabbata mage ce."
Hajiya ta fad'a tana zazzare ido.
"Itace ba gata nan ba ta fito, watakila ma ita ce ta razane ki d'azu."
"Um-um ba ita ba ce magana naji bilhakki, kyanwa tana maga ne."
"Hajiya in zaki kwanta kirika addu'a, babu abin da zai same ki insha'allahu."
"Ai ni yau naga karfin addu'a baki ji yanzu ma nayi ba, ai addu'a tana da amfani yana kora miyagu."
"Ai Hajiya wannan da kikayi yanzu ba addu'a ba ce, ki karanta shi a karance ba ki fad'a irin yadda kika fad'i yanzu ba,
ayatul'kursiyu da suratul iklas da falaki da nasi, a duk sanda zaki kwanta ki karantasu sun'ishe ki komai da komai,
zasu karake daga sharrin komai."
Hajiya ta mara baki tana fad'in
"Ahaf wannan addu'ar da kike gani tun muna yawo da jajayen sawu muke ganin amfanin sa, duk shi mukeyi da kawayen mu, muyi fad'a da uban kowa mu kwana lafiya, ai ko munga amfanin sa."
Hajiya Bishira ta girgiza kai tana fad'in
"Allah shi kyauta."
Sun so tafiya d'akunan su Hajiya ta ce sai dai fa su zauna su waye gari anan tun da gari yakusa waye wa.
Washegari Hajiya ta d'agawa Daddy hankali a waya wai sai dai yadawo yanimo kafi a sa a gidan, miyagu nason ganin bayan su.
ya ce mata to yakusa dawowa.
Shirye-shiryen bikin Farida nadad'a matsowa.
uwar amarya Mommy ba zama.
anata kai kawo yadda biki zai gudana baza aji kunyar kawaye ba.