Sashe 44
Feeryal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har lokacin FEERYAL tana bacci.
tsayuwa suka yi a bakin gadon Dr Imran ya ware ido sosai a kanta yana kallon ta da yadda ruwan yake shiga a hankali sosai.
yana mai mamakin a ina suka samo ta, ko tana cikin masu kawowa Nigeria ziyara ce ciwo ya kamata.
Dr Imran ya dubi Jasin ya ce
"Ina fayel d'in ta d'uko system mu gani?."
nurse Jasin ya ce
"Ba'a bud'e fayel file ba."
kai ya jinjina a kasan ransa ya ke fad'in
"A.A ke nan 'yar da yake sawa mutuwa gata haryanzu tana numfashi, ai tun da ta fad'o hannunka da ikon Allah da sauran shanruwanta."
nan shima ya d'aura nashi aikin kan na Dr A.A Fiya.
Su Abba sun kasa nutsuwa har sai da suka taho asibitin, sai dai har lokacin da suka ison ma bata farkaba.
Tuni 'yan jaridu da gidajen TV dana radio harma da social media suka fara watsa labarai da rahotanni kan faruwal lamarin.
inda suke sanar da nasarar da jami'an tsaro suka samu kan kama 'yan ta'addan da aka jima ake farautarsu.
NTA ta fito da rahoton faruwar lamarin da yadda komai ya kasance.
ta bakin d'an jaridar da yake karanto labaran kamar haka
"Jami'an tsaron Nigeria sojoji da 'yan sanda sun sami nasarar cafke 'yan tadaddan nan, kungiyar da akeyiwa lakabi da 'yan d'aukar amarya,
ajiya litinin 5 ga wata,
inda suka yi zuga zuwa d'aukar wata yarinya,
a Maitama gidan shahararren d'an kasuwan nan Alhaji Tahir Abbas, dake cikin birnin tarayya Abuja,
in da jami'an tsaro suka sami labari sukayi fitar gaggawa,
inda sukayi bata kashi sakanin su da 'yanta'addan sukayi nasarar cafkesu, suka kuma kwato yarinyar da yanzu haka tana gadon asibiti,
rahoto ya tabbatar mana da cewa jami'ai uku sun sami rauni, sakamakon musayar wutar daya shiga sakanin jami'an da 'yan ta'addan.
a yanzu haka shugaban na 'yan ta'addan Bala kwari da sauran mabiyan tawagarsa na d'aukar amarya suna nan, a hannun hukuma.
Bala Kwari ya jima yana ta'addanci ba a iya birnin taraiya ba harma da sauran jahoyin kasarnan,
duk yarinyar da yaga ta masa ko budurwa ko matar aure to sai ya d'auketa, shekarar data gabata motocin d'aukar amarya yake garkuwa da su bayan ya d'auke amaryar sai ya sake sauran mutanen ya tafi da amaryar.
wakilanmu suna can ofishin hukuma da asibitin da yarinyar take dan son sanin halin da ake ciki,
ku cigaba da biyo mu dan son salin halin da ake ciki."
Labarin da kasa gaba d'ya ta waye gari da shi ke nan, inda jama'a suka ji dad'in nasarar da aka samu na cafke 'yan ta'addan, tawagar d'aukar amarya, da suka addabi al'umma ana kuma yiwa yarinyar fatar samin sauki.
Wani irin mikewa Daddy ya yi yana ware idanunsa kan TV in da ake hasko labaran,
Aunty da ta fito rike da tray daga kichin ta ja ta tsaya jikinta na b'ari.
da sauri Daddy ya d'au rimut ya kashe TV yana kallonta yana fatan Allah yasa bata ji ba dan yasan ta da iya firgicewa, sai dai alamu sun nuna taji ga yadda gaba d'aya yanayin ta ya sauya.
hannu na b'ari murya na rawa tashiga fad'in
"Innalillahi wa innailaihirraji'un me nake ji haka Daddy ka kunna TV mana, Alhaji Tahir Abbas Maitama, Abba ke nan fa, gidan mu meke faruwa a gidan mu wa aka sace!."
gaba d'aya Aunty ta firgice.
da sauri Daddy ya je ya karb'i tray'n da yake kokarin sub'ucewa a hannunta, ya dire shi kasa kana ya ce
"Ki nutsu Fad'imatu, insha'allah komai yazo cikin sauki, ai kinji basukaiga gudu da wacce suka d'aukan ba aka sami nasarar cafke su,
wace ce cikin su Maryam ce ko FEERYAL?
ya Allah ka tsayar haka."
Aunty ta girgiza kai tana fad'in
"FEERYAL ce ma nasan ita ce ita ce kullum ake kawo wa hari."
"Ko wace ce cikin su Allah mun gode maka da ka kawo mana saukin lamarin, bari na kira Alhaji'n Abuja shima wata kila damuwar ce yasa bai sanar mana ba."
Ya dannan number Abba yayi ta ring ba'a d'agaba.
a b'angaren Abba kuwa wayar tasa a gida ya barta suka taho asibiti inda FEERYAL take.
Sau biyar Daddy yana kira ba'a d'agawa, ganin haka yasa hankalin sa ya soma tashi, sai dai bai nuna ta inda Aunty zata gane har ta dad'a birkicewa ba.
ya dube ta yana cewa
"Bari naje na dawo kada ki tada hankalin ki babu komai, ai kinji da akwai da 'yan jaridun sun fad'a."
ita dai shiru tayi amma Allah ne kad'ai yasan ya take ji cikin zuciyarta.
Daddy na fita yasa akayi masa bukin na jirgi, bada jimawa ba kuwa jirgi ta tashi zuwa Abuja.
Ko da ya isa maitama gidan Alhaji Tahir Abbas, ya taras da ba mutan gidan sai ma'aikatan gidan.
nan suke shaida masa suna asibiti, akayi masa jagora zuwa, A.A FIYA Hospital.
Su Abba suka cika da mamakin ganin Daddy dan basuyi sammanin ganin nasa ba, saboda basu sanar musu da me ke faruwa ba.
Abba ya tari Daddy yana fad'in
"Ina da shirin nimanka, amma bayan na tabbatar da farkawarta, dan bansan ta inda zan fara sanar da kai, inda amanar da ka bani ta kasan ce ba."
Daddy ya girgiza kai yana cewa
"Ko a gurin mu idan Allah ya kaddara hakan zata faru sai ta kasance, amma ya jikin nata ta farfad'o kuwa?."
"Har yanzu dai amma ance bacci take."
kai Daddy ya jinjina tare da fad'in
"Allah ya bata lafiya, babu dai abinda suka mata ko?
kuma babu abin da sukayi muku komai lafiya dai ko?."
"Basuyi mata komai ba firgici ne yasa ta shiga dogon suma, amma an sami nasarar cirota a dogon suman yanzu dai tana bacci tun daren jiya amma kikita yanzu ya tabbatar mana idan ruwan da ke jikin ta ya kare zata farka,
babu wanda suka cutar a cikin mu."
"Allah ya bata lafiya, ya tsare na gaba."
cewar Daddy yana sauke numfashi tare da goya hannunsa a baya yana d'an zaga gurin.
Major Sadam da Inspector Nasir ne suka shigo da Dr Imran.
suka shige ICU.
har lokacin FEERYAL na kwance bata ko motsi sai dai numfashin da take saukewa a hankali.
Major Sadam ya dubi Dr Imran jiki ba kwari yana fad'in
"Dr takai 9h tana baccin nan ace har yanzu bata farka ba,
wai ina Dr can yake ne anya ba wani abin yamata ba ace har yanzu tana bacci bata farka ba,
no! ina banma yadda ba kirawo shi, je ka kirashi yazo nan, oya kirashi maza ya zo nan!."
Dr Imran ya ce
"Zata farka daga zaran ruwan nan ya kare mud'an jira zuwa karewar ruwan."
"Kai wai wani irin ruwane ma wannan ace tun cikin dare yana shiga jikinta ace har kuma yanzu bai gama ba,
a cire wannan ruwan tafarka tukun a maida mata."
ya mika hannu yana kokarin zare cannula hannunta.
da sauri Dr Imran ya ce
"Kar ka soma! idan ka maida ita dogon suma ni da kai bazamu iya dawo da ita ba, karshe abinda ake gudun ne zata kasance, ko tantama babu wannan numfashin da kake gani ma, bazaka sake ganin sa ba,
mutuwa zata yi!."
da karfi Sadam ya janye hannunsa ya yi baya da sauri yana fad'in
"What!."
kai Dr Imran ya jinjina tare da cewa
"Tabbas! Dr A.A Fiya baya ma kasar bare ya bata taimakon gaggawa kamar dai yanzu a inda take d'innan,
farkawarta batare da karewar wannan ruwan ba, barazana ce ga rayuwarta,
shi ya saita ruwan a kan dai-dai awannin da yakamata ta farka,
ba ruwa gama gari ne da ka sani ba, ruwa ne mai d'auke da sinadaran magunguna na musamman masu inganci a cikin sa,
dan haka ka jira cikawar awannin koda kuwa wuni zatayi ta kuma kwana a haka."
Inspector Nasir ya ce "Shike nan Major kadai ji a bari kar aje a b'allo wata likin, amma shi Dr yaushe zai dawo?."
murmushi Imran ya yi yana fad'in
"Bana ce ba duk san da ya yi ra'ayi zai juyo."
jinjina kai Nasir ya yi tun a jiya ya fahimci likitan mai tsastsauran bahagon ra'ayi ne,
irin wanda ba'a sasu ba'a hanasun nan,
babu kuma d'igon tsoro a gare shi.
sai kuma ya yi murmushi dan ya burge shi ba kad'an ba.
Fad'a Major Sadam ya soma yana fad'in
"Shine ya bar patient ya tsallaka ya tafi, shi da ya fara ba sai ya karasa ba, idan ya sake aka sami matsala na rantse shima sai ya yi freezing."
hannunsa Nasir ya rike ya jasa sukayi waje.
Dr Imran ya yi karamar dariya yana girgiza kai.
irin dai yafad'i son ransa, baisan da wa yake zancen ba.
shima ya biyo bayan su bayan ya tabbatar da komai dai-dai cikin room d'in.
Dr Imran ya yi mamakin ganin Daddy a asibitin tare da su Abba.
ya karaso ya shiga gaidashi cikin girmamawa,
Daddy ya amsa yana tambayar sa ya mai jikin dai?
ya ce da sauki sosai.
Bayan a wanni uku wanda ya yi dai-dai da awannin 12 kenan FEERYAL ke kwance a asibitin.
sai a lokacin ruwan ya kare bayan mintuna 15 da karewar nasa kuwa ta farka.
Su Daddy Abba Hajja Umma Maryam sunyi matukar farinciki da farkawar nata,
zo kaga Major Sadam yakasa zaune ya kasa ysaye.
Inspector Nasir sai dariya da tsiya yake masa.
A b'angaren Dr Imran ma yaji dad'in farkawar nata ya d'agata a ICU ya canza mata d'aki.
su Daddy suna cikin d'akin suna ta yi mata sannu da murnar ganin lafiya bayyane a gareta.
tsayuwa suka yi a bakin gadon Dr Imran ya ware ido sosai a kanta yana kallon ta da yadda ruwan yake shiga a hankali sosai.
yana mai mamakin a ina suka samo ta, ko tana cikin masu kawowa Nigeria ziyara ce ciwo ya kamata.
Dr Imran ya dubi Jasin ya ce
"Ina fayel d'in ta d'uko system mu gani?."
nurse Jasin ya ce
"Ba'a bud'e fayel file ba."
kai ya jinjina a kasan ransa ya ke fad'in
"A.A ke nan 'yar da yake sawa mutuwa gata haryanzu tana numfashi, ai tun da ta fad'o hannunka da ikon Allah da sauran shanruwanta."
nan shima ya d'aura nashi aikin kan na Dr A.A Fiya.
Su Abba sun kasa nutsuwa har sai da suka taho asibitin, sai dai har lokacin da suka ison ma bata farkaba.
Tuni 'yan jaridu da gidajen TV dana radio harma da social media suka fara watsa labarai da rahotanni kan faruwal lamarin.
inda suke sanar da nasarar da jami'an tsaro suka samu kan kama 'yan ta'addan da aka jima ake farautarsu.
NTA ta fito da rahoton faruwar lamarin da yadda komai ya kasance.
ta bakin d'an jaridar da yake karanto labaran kamar haka
"Jami'an tsaron Nigeria sojoji da 'yan sanda sun sami nasarar cafke 'yan tadaddan nan, kungiyar da akeyiwa lakabi da 'yan d'aukar amarya,
ajiya litinin 5 ga wata,
inda suka yi zuga zuwa d'aukar wata yarinya,
a Maitama gidan shahararren d'an kasuwan nan Alhaji Tahir Abbas, dake cikin birnin tarayya Abuja,
in da jami'an tsaro suka sami labari sukayi fitar gaggawa,
inda sukayi bata kashi sakanin su da 'yanta'addan sukayi nasarar cafkesu, suka kuma kwato yarinyar da yanzu haka tana gadon asibiti,
rahoto ya tabbatar mana da cewa jami'ai uku sun sami rauni, sakamakon musayar wutar daya shiga sakanin jami'an da 'yan ta'addan.
a yanzu haka shugaban na 'yan ta'addan Bala kwari da sauran mabiyan tawagarsa na d'aukar amarya suna nan, a hannun hukuma.
Bala Kwari ya jima yana ta'addanci ba a iya birnin taraiya ba harma da sauran jahoyin kasarnan,
duk yarinyar da yaga ta masa ko budurwa ko matar aure to sai ya d'auketa, shekarar data gabata motocin d'aukar amarya yake garkuwa da su bayan ya d'auke amaryar sai ya sake sauran mutanen ya tafi da amaryar.
wakilanmu suna can ofishin hukuma da asibitin da yarinyar take dan son sanin halin da ake ciki,
ku cigaba da biyo mu dan son salin halin da ake ciki."
Labarin da kasa gaba d'ya ta waye gari da shi ke nan, inda jama'a suka ji dad'in nasarar da aka samu na cafke 'yan ta'addan, tawagar d'aukar amarya, da suka addabi al'umma ana kuma yiwa yarinyar fatar samin sauki.
Wani irin mikewa Daddy ya yi yana ware idanunsa kan TV in da ake hasko labaran,
Aunty da ta fito rike da tray daga kichin ta ja ta tsaya jikinta na b'ari.
da sauri Daddy ya d'au rimut ya kashe TV yana kallonta yana fatan Allah yasa bata ji ba dan yasan ta da iya firgicewa, sai dai alamu sun nuna taji ga yadda gaba d'aya yanayin ta ya sauya.
hannu na b'ari murya na rawa tashiga fad'in
"Innalillahi wa innailaihirraji'un me nake ji haka Daddy ka kunna TV mana, Alhaji Tahir Abbas Maitama, Abba ke nan fa, gidan mu meke faruwa a gidan mu wa aka sace!."
gaba d'aya Aunty ta firgice.
da sauri Daddy ya je ya karb'i tray'n da yake kokarin sub'ucewa a hannunta, ya dire shi kasa kana ya ce
"Ki nutsu Fad'imatu, insha'allah komai yazo cikin sauki, ai kinji basukaiga gudu da wacce suka d'aukan ba aka sami nasarar cafke su,
wace ce cikin su Maryam ce ko FEERYAL?
ya Allah ka tsayar haka."
Aunty ta girgiza kai tana fad'in
"FEERYAL ce ma nasan ita ce ita ce kullum ake kawo wa hari."
"Ko wace ce cikin su Allah mun gode maka da ka kawo mana saukin lamarin, bari na kira Alhaji'n Abuja shima wata kila damuwar ce yasa bai sanar mana ba."
Ya dannan number Abba yayi ta ring ba'a d'agaba.
a b'angaren Abba kuwa wayar tasa a gida ya barta suka taho asibiti inda FEERYAL take.
Sau biyar Daddy yana kira ba'a d'agawa, ganin haka yasa hankalin sa ya soma tashi, sai dai bai nuna ta inda Aunty zata gane har ta dad'a birkicewa ba.
ya dube ta yana cewa
"Bari naje na dawo kada ki tada hankalin ki babu komai, ai kinji da akwai da 'yan jaridun sun fad'a."
ita dai shiru tayi amma Allah ne kad'ai yasan ya take ji cikin zuciyarta.
Daddy na fita yasa akayi masa bukin na jirgi, bada jimawa ba kuwa jirgi ta tashi zuwa Abuja.
Ko da ya isa maitama gidan Alhaji Tahir Abbas, ya taras da ba mutan gidan sai ma'aikatan gidan.
nan suke shaida masa suna asibiti, akayi masa jagora zuwa, A.A FIYA Hospital.
Su Abba suka cika da mamakin ganin Daddy dan basuyi sammanin ganin nasa ba, saboda basu sanar musu da me ke faruwa ba.
Abba ya tari Daddy yana fad'in
"Ina da shirin nimanka, amma bayan na tabbatar da farkawarta, dan bansan ta inda zan fara sanar da kai, inda amanar da ka bani ta kasan ce ba."
Daddy ya girgiza kai yana cewa
"Ko a gurin mu idan Allah ya kaddara hakan zata faru sai ta kasance, amma ya jikin nata ta farfad'o kuwa?."
"Har yanzu dai amma ance bacci take."
kai Daddy ya jinjina tare da fad'in
"Allah ya bata lafiya, babu dai abinda suka mata ko?
kuma babu abin da sukayi muku komai lafiya dai ko?."
"Basuyi mata komai ba firgici ne yasa ta shiga dogon suma, amma an sami nasarar cirota a dogon suman yanzu dai tana bacci tun daren jiya amma kikita yanzu ya tabbatar mana idan ruwan da ke jikin ta ya kare zata farka,
babu wanda suka cutar a cikin mu."
"Allah ya bata lafiya, ya tsare na gaba."
cewar Daddy yana sauke numfashi tare da goya hannunsa a baya yana d'an zaga gurin.
Major Sadam da Inspector Nasir ne suka shigo da Dr Imran.
suka shige ICU.
har lokacin FEERYAL na kwance bata ko motsi sai dai numfashin da take saukewa a hankali.
Major Sadam ya dubi Dr Imran jiki ba kwari yana fad'in
"Dr takai 9h tana baccin nan ace har yanzu bata farka ba,
wai ina Dr can yake ne anya ba wani abin yamata ba ace har yanzu tana bacci bata farka ba,
no! ina banma yadda ba kirawo shi, je ka kirashi yazo nan, oya kirashi maza ya zo nan!."
Dr Imran ya ce
"Zata farka daga zaran ruwan nan ya kare mud'an jira zuwa karewar ruwan."
"Kai wai wani irin ruwane ma wannan ace tun cikin dare yana shiga jikinta ace har kuma yanzu bai gama ba,
a cire wannan ruwan tafarka tukun a maida mata."
ya mika hannu yana kokarin zare cannula hannunta.
da sauri Dr Imran ya ce
"Kar ka soma! idan ka maida ita dogon suma ni da kai bazamu iya dawo da ita ba, karshe abinda ake gudun ne zata kasance, ko tantama babu wannan numfashin da kake gani ma, bazaka sake ganin sa ba,
mutuwa zata yi!."
da karfi Sadam ya janye hannunsa ya yi baya da sauri yana fad'in
"What!."
kai Dr Imran ya jinjina tare da cewa
"Tabbas! Dr A.A Fiya baya ma kasar bare ya bata taimakon gaggawa kamar dai yanzu a inda take d'innan,
farkawarta batare da karewar wannan ruwan ba, barazana ce ga rayuwarta,
shi ya saita ruwan a kan dai-dai awannin da yakamata ta farka,
ba ruwa gama gari ne da ka sani ba, ruwa ne mai d'auke da sinadaran magunguna na musamman masu inganci a cikin sa,
dan haka ka jira cikawar awannin koda kuwa wuni zatayi ta kuma kwana a haka."
Inspector Nasir ya ce "Shike nan Major kadai ji a bari kar aje a b'allo wata likin, amma shi Dr yaushe zai dawo?."
murmushi Imran ya yi yana fad'in
"Bana ce ba duk san da ya yi ra'ayi zai juyo."
jinjina kai Nasir ya yi tun a jiya ya fahimci likitan mai tsastsauran bahagon ra'ayi ne,
irin wanda ba'a sasu ba'a hanasun nan,
babu kuma d'igon tsoro a gare shi.
sai kuma ya yi murmushi dan ya burge shi ba kad'an ba.
Fad'a Major Sadam ya soma yana fad'in
"Shine ya bar patient ya tsallaka ya tafi, shi da ya fara ba sai ya karasa ba, idan ya sake aka sami matsala na rantse shima sai ya yi freezing."
hannunsa Nasir ya rike ya jasa sukayi waje.
Dr Imran ya yi karamar dariya yana girgiza kai.
irin dai yafad'i son ransa, baisan da wa yake zancen ba.
shima ya biyo bayan su bayan ya tabbatar da komai dai-dai cikin room d'in.
Dr Imran ya yi mamakin ganin Daddy a asibitin tare da su Abba.
ya karaso ya shiga gaidashi cikin girmamawa,
Daddy ya amsa yana tambayar sa ya mai jikin dai?
ya ce da sauki sosai.
Bayan a wanni uku wanda ya yi dai-dai da awannin 12 kenan FEERYAL ke kwance a asibitin.
sai a lokacin ruwan ya kare bayan mintuna 15 da karewar nasa kuwa ta farka.
Su Daddy Abba Hajja Umma Maryam sunyi matukar farinciki da farkawar nata,
zo kaga Major Sadam yakasa zaune ya kasa ysaye.
Inspector Nasir sai dariya da tsiya yake masa.
A b'angaren Dr Imran ma yaji dad'in farkawar nata ya d'agata a ICU ya canza mata d'aki.
su Daddy suna cikin d'akin suna ta yi mata sannu da murnar ganin lafiya bayyane a gareta.