← Book details Feeryal Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 52

Sashe 26

Feeryal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kai Aunty ta jinjina tana fad'in
"Mungode Malam Allah ya saka da alheri."
"Amin amin Allah ya tsare muku hanya nasan bazasu bari ku d'au hanya ku kad'ai ba, zaku sami 'yan rakiya, dan ita d'in mai girma ce agare su, tana tare da tsaron su a ko yaushe, gudun faruwar wani abu."
kai Aunty ta jinjina ta mike tana cigaba da masa godiya ta ruko hannun Feeryal, sukayi masa sallama har bakin zaure Inna Delu ta rako su.

Malam Buba Mani kuwa har jikin mota sai da yaga tashin su kafin ya koma gurin zaman su da mutanen sa.

Cikin garin Bauchi suka dawo a government House suka kwana washegari suka bi jirgi suka koma Lagos.
zuciyar Aunty wasai da jin Feeryal d'in ta mutum ce, sai dai wani b'arin zuciyar ta na kunshe da tambayoyi da son sanin dalilin daya sa wasu ke niman ta.

A b'angaren Daddy ma sai da suka dawo gida kafin yasa mi sukunin tambayar ta me Malam Buba Mani ya fad'a a kanta.
Aunty ta shaida masa komai, ya jinjina lamarin ba kad'an ba ya ce
"Ita d'in ikon Allah ce, Allah ya taya mu rukonta ya kauda idon makiya a kanta,
zamu bada iya karfin mu wajen bata kariya idan har idanunmu zai iya ganin abin cutarwa a gare ta."
Aunty ta amsa da amin amin.

Daddy ya mike yanufi kofa domin zuwa side d'insa, dan dama Umma Karima ce da shi, tafiyar daya taso ne ya tsallaka ya tafi.
har ya d'aura hanu kan handle ya jiyo muryar Feeryal
"Daddy kar ka kwanta a kan gadon ka akwai jiji."
cak yaja ya tsaya tare da juyo wa.
Aunty ta yi saurin cewa
"Ke Feeryal a ina kika ga jijin?."
"Na gani yana cikin pillow Daddy."
Daddy ya tako in da take yarage tsawon sa dai-dai nata ya ruko fad'unta sannan ya ce
"Zai min wani abu ko?."
ido ta wawwaro ta ce
"Eh jiji ne fa Daddy, yana cikin pillow'n ka."
kai ya jinjina ya ja kumatun ta yana murmushi.

Ya juya har ya kai kofa Aunty ta ce
"Jira ni Daddy, Feeryal je gurin Baba Rabi tayi miki wanka."
da gudu tayi kichin gun Baba Rabi ita kuma tabi bayan Daddy.

Tare suka tafi side d'in sa.
suna shiga bedroom d'in sa suka soma binciken cikin pilullukan da suke jere a kan makeken bed d'in sa na alfarma.
kaf suka cire rigunan filon basuga komai ba, suna cikin mai da pillowcases d'in ne idon Aunty ya sauka kan na hannunta da alamun kamar anyi d'inki ta tsakiyar sa, wan da duk pillows d'in na kamfani ne babu alamun d'in ki a jikin sa.
hannu ta saka tana shafa gurin,
ganin hankalin ta ya koma kan sa Daddy shima ya maida hankalin sa kan gurin.
ya mika hannu ya janyo durowar gifen gado ya d'au almakashi ya tsaga gurin, ya zazzage audugar pillow'n a sakiyar gadon sai ga wani d'aurin laya ya fad'o.
Aunty tayi saurin d'auka da mamaki suke kallon sa.
Daddy ya karb'a yana kokarin warware shi Aunty takuma amshewa tana fad'in
"Babu amfanin bud'e wa aga me ya kunsa a kona kawai."
kai ya jinjina.

Tayi saurin tattara audugar ta mai da shi cikin pillon kana ta maida komai in da yake, taje ta d'auko wani sabon pillow ta saka masa pillow cases d'in da ta citewa wancan, ta d'au wanda aka saka layar ciki ta tafi da shi side d'in ta.
a tabaya ta can gefen garden taje ta kona duka da layar da pillow'n.

Aunty da Daddy kad'ai suka san da wannan labarin na Feeryal ko Baba Rabi da kusan komai ya faru a kan idon ta bata fahimci komai ba, sai dai itama da tarin tambayoyin cikin zuciyar ta,
bata kuma da mai bata amsa dan bata da ikon tinkarar uwar gijiyar tata, haka tabar abin a ranta.

Yau Monday Aunty ta gama wa Feeryal shirin makaranta tsaf, suna zaune kan carpet tana breakfast, Aunty ta dube ta cikin hikima ta ce
"Yammatan Ammie, kina ji na ko, kada ki fad'awa wani kina ganin wasu, ko Miemie ce kada ki fad'a mata,
in ba hakaba zasuce ke mayya ce, ko kina so su Ameerah su rika ce miki mayya suna dukanki?."
kai ta girgiza tana yin rau-rau da ido hawaye nason taruwa.
"To ko kin ga kawayen ki kiyi shiru kada ki fad'awa kowa, idan ke da sune babu kowa a gurin sai kuyi wasan ku, kinji ko."
ta ce "Tom."
"Yauwa good girl, to yi sauri ki cinye ku tafi karkuyi latti."

Kamar kullum da ko yaushe har cikin mota ta kaita kafin ta dawo......!

Mommyn Twins ce

🌺🌺 *FEERYAL* 🌺🌺

*NA*
*RASHEEDAT S DIRECTOR*

( _Book 1_)

*~Free page~*

*_Littafin na kud'i ne 500 account no 3170524141 Rashida Salihu first bank ka-ki tura shaidar biya ta WhatsApp number ta 08034690723_*

*____________________________________*

*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍�*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻

https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association

*____________________________________*

🅿�12

(Bayan shekaru uku)

Wanda hakan yayi dai-dai da shekarun Feeryal 7 ke nan ta kara girma da wayo sosai.
ya yin da kyara da tsangwamar dake sakanin ta da su Ameerah Sahla Nabila, da kuma iyayen su mata ke dad'a ninkuwa.
kawancen ta da shakuwar ta da Miemie kuwa ke kara karfi.

Egypt

Hajiya ce zaune a wani kayattaccen parlour a can ka'sar Egypt.
Kulu na zaune a kasa a gefen ta, tana mammasa mata kafafu.
tun safiyar yau Hajiya ta tashi da masifa, ita fa bata kuma kwanar kasar nan k'asar ta zata koma ita dai gida zata koma taga jikokin ta.
waya ta mika wa Kulu ta na fad'in
"Kulu kirawo min Abubakar, yau bani kuma kwanan k'asar nan, aikin banza kawai yakawo ni ya aje cikin masu jajayen kunnuwa ina rayuwa ni kad'ai kamar mayya,
duk sanyi yabi ya addabe ni, jekoki na suna can ni ina wani gurin,
to yau bazan kuma kwana garin nan ba maza yasa jirgi ya d'auke ni ya mai da ni in da nafi wayo."

Kulu ta mika mata wayar tana cewa
"Gashi Hajiya ya d'aga."
"Yauwa bani ni shi nan."
daga cikin wayar Daddy ya yi sallama yana kokari gaisheta ta katsashi da fad'in
"Kai Abubakar ka kawo ni ka aje nan ni kad'ai kamar mayya, shekaru uku ina zaune kamar wata mara galihu,
kullum nace kasa a maido ni gida sai ka ce to zaka sa, sai kuma kayi buris abib ka,
wancan zuwan naka na ce mu tafi tare kace nabari nadad'a jin sauki tukun,
awani dadilin zaka rabani da kasata; ce maka akai banji sauki ba,
jikoki na suna can ni ina wata duniyar daban, to yau-yau d'in nan ka sa a maidani gida dan ni na warke,
ko kai yanzu baka kaini lafiyar ido ba,
an d'aga ni an rabani da jikoki na an kawo ni wata duniyar da ban san kowa ba, shekara uku ina zaune kamar mara galihu,
to nagaji da zama tun marmaza kasa a mai da ni gida, yau-yau d'in nan."
Daddy ya ce
"Kiyi hakuri Hajiya bari nasa ayi muku bukin d'in jirgi zuwa ranar Litinin sai ku dawo."
"Da dai yafi dan ni nagaji da zaman shiru, in ba haka ba naje tasha nashiga mota."
"Hajiya daga can zaki shigo mota zuwa Nigeria ai bazai yuwu ba, jirgi ma zaki biyo kiyi hakuri dai."
"Ni dai na fad'a maka idan ranar Litinin tayi baka sa an d'auko mu ba tambaya zanyi a kai ni tashi."
ta katse wayar tana cigaba da bombomi.
Hajiya Bishira dake gefe tayi murmushi rigimar uwar tasu kullum karuwa yake.

Ta ce
"Hajiya wa ya ce miki akwai tashar mota na zuwa Nigeria anan, ai sai dai airport d'in jirji,
dan Allah ki barmu mu zauna anan yafi mana babu hayaniya ba komai, sai dai kaci ka kwanta hankali kwance,
acan fa hayaniyar yara ma kad'ai ya isheka, da wad'an nan masifaffun matan Yaya Abubakar d'in."
"Allah ya sawake min ni da zaman shiru ai sai dai in nashiga kabari, da raina ina numfashi kam baza a hanani walwala ba,
ai dama ku zaman bariki baya damun ku, in da Abubakar zaibi ta nawa ma da gida muka koma can Yelwan Shandam, muje muyi zaman mu hankali kwance, amma kullum kana kulle a gida baka d'an zagawa ina zan iya ciwon kafa ya kamani, ai in baka yawatawa kai da ciwon kafa kun kulla,
ina zan iya wani zama anan, ku da kuka ga zaku iya zama ga guri nan amma ni kam kafata tana takalmi gara na koma in da nafi wayo."

"Wlh kuwa hajjaju da kin bari mudad'a hutawa jiya kuwa Hajiya Bishira take cewa yau direba zai kuma fita da mu mu yawata."
cewar Kulu tana washe baki.
"Amma dai anyi asara Kulu, ina zaki yawatan da kai duk furfura,
an girma ana cin kasa,
sai kuyi ta zama ni kam dai jikoki na nake son gani,
tafiya gida ba fashi, ina zan iya da zaman shiru,
in ban da ma abokin turawa, ya kawo min ziyara wancan satin ai da tun a satin na koma Nigeria abina,
ina zan iya shege da hauka,
tun da kunga gurin zama sai kuyi ta zama."

Kulu ta b'ata rai ita a duniya bata so ace mata tsohuwa, ta buga cinya tana mara baki.
"To Allah ya baki hakuri Hajiya."

Hajiya ta mike tana fad'in
"Bari ma kiga, ni kam naje na fara shiri."
ta shige bedroom..

Ranar Litinin tun da Hajiya tayi sallar asuba bata zauna ba ta rika jidar kayan ta dana tsarabar datayi,
ta tarasu a parlour.
tsabar mitar da take yasa su Hajiya Bishira fito da nasu kayan badun sun shirya ba.
"Ke bishira sake kira min Abubakar idan jirgin ta cika yanzu direba ya kai mu tasha mushiga mota."
Chapter 26 · 0% Book details