Sashe 37
Feeryal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zama ya gyara ya tsunkuyar da kai yana d'an sosa bayan keyar sa.
Daddy ya dube sa yana fad'in
"Ya akayi kuma?."
dad'a tsunkuyar da kai ya yi yana shafo keyarsa sannan ya ce
"Am dama Daddy wani d'an kud'i ne nake da bukatar su."
Sallamar da su Ajeemal sukayi ne ya katse shi daga abin da yake son fad'a.
Daddy ya amsa suka karaso suka zazzauna kasan carpet suna gaida Daddy'n.
ya amsa yana tambayarsu sun tashi lafiya?.
duk suka amsa da lafiya lau.
Suma zaman suka gyara da alamar akwai abin da ke tafe da su.
Daddy ya dubi Zaraddin ya ce
"Uhum ina jin ka Zaraddin me ke tafe da kai?."
Zaraddin yabi su Ajeemal da kallon kasa-kasa duk ya harare su kana ya muskuta ya ce
"Da ma Daddy kud'i nake so, abokin mu ne zaiyi aure yau, ina kuma niman izini ba a garin nan za'ayi bikin ba, zamuje mu kwana d'aya gobe zamu dawo."
Daddy ya ce
"Nawa ne kake bukata?."
kai ya d'an sosa sannan ya ce
"2 million ne Daddy."
Daddy ya d'aga ido ya kalle shi kana ya ce
"1 million za'a baka sai ka lallab'a, ka koyi yadda ake maneji."
Faisal ya zubawa Zaraddin ido da mamakin karyar da ya sharara yanzu,
wanda yana jin sa sanda ya fito zai zo gurin Daddy yazo zai wuce ta kofar bedroom d'in sa yaji yana waya,
yana sanarwa wani abokin sa yau da karfe 12 na dare akwai birthday party na girl friend d'in su.
"Wato acan zaije ya kwana ke nan."
ya girgiza kai
Maganar Daddy ne yasashi maida hankali gurin sa
"Ku me ke tafe da ku?."
Ajeemal yad'an gyara zama sannan ya ce
"Daddy muna so ka cika mana kud'i ne mu siyi sabon computer, muna son mu samu babban namu saboda yanayin karatun mu."
Daddy ya jinjina kai ya ce
"Nawa ne cikon kud'in naku?."
Shamsuddin ya ce
"2-2 millons ne kud'in computer amma 1 million muke so a cika mana."
Faisal ya karb'i batun da cewa
"Mun samu irin wanda muke so a Germany zamuyi odar sa can."
"To madalla hakan abune me kyau."
Daddy ya fad'a yana d'aukar d'aya daga cikin wayoyin sa.
Ya yi wa ko wannensu transfer d'in million d'aya da rabi.
sannan ya dube su yana fad'in
"Miliyan d'aya da rabi-rabi na sa muku sai ku aje 500k ko wata bukatar zata taso muku,
kai Zaraddin sai kayi hidimar bikin da zakuyi, amma kai banji kace zaka sayi computer ba, ko kana da ita ne?."
Gefen kansa ya sosa ya ce
"Am eh.eh..idan na dawo ne zan yi maganar ni ma."
"To shike nan sai ku tashi kuje Allah ya yi jagora,
amma Shamsuddin Ajeemal Faisal wazai yi muku odar daga can bazakuyi wa d'an'uwanku magana, tun da yana can,
ya sako muku a jirgi ba, ko kun yarda da wanda zakuyi harkar da shi ne?."
Ajeemal ya ce
"Daddy shine ma zamu tura masa, munyi magana da shi ne kan muna son sabon computer shine ya ce,
mu turo da rabin kud'i sai ya cika ya siya mana."
Daddy ya ce
"Inji sa ya ce sai kun bada rabin kud'i kafin ya siya muku abu?
to duk ku maido min da kud'i na kuce masa nace ko sisi bazaku bada ba shi zai siya muku da kud'in sa,
ya baku sana'ar yi ne da zaku sami kud'i da har zaice ku bada rabin kud'i? a ina zaku sami kud'in kuna 'yan makaranta yabari idan kuka gama karatu kuka kama aiki shine zaiyi wannan maganar,
maza-maza kuce dashi na ce ko sisi bazaku bashi ba shi zai saya muku da kud'in sa."
Duk suka zaro wayoyin su suna kokarin maida masa kud'in da ya tura musu.
ya ce "Ku bar shi ku adana idan kuna da bukatar wani abin sai kuyi da shi, kada ku kuskura ku tura masa ko sisi cikin kud'in nan."
suka amsa da to sukayi masa godiya suka mike suka fito.
Suna fita Faisal ya dubi Zaraddin da yayi kicin-kicin da fuska, yana harararsu ya ce
"Yanzu kayiwa Daddy irin wannan karyar alhalin party zakaje kace zakayi tafiya,
ina jin kafa d'azu kana waya zakuje birthday party 12 na dare."
baki Shamsuddin ya bud'e ya rike hab'a ya ce
"Kasan da wannan Faisal shine kana ji ya yi wa Daddy karya,
ya ce zaije bikin abokin sa, ashe party zaije ya kwana a can,
to wlh sai na fad'awa Daddy tun da har abun naka yakai ka fara kwana a Club."
ya juya zai koma parlour'n Daddy.
Ajeemal ya ruko sa yana fad'in
"Rabu da shi karma kaje ka barshi yaci gaba tun da hakan ya zab'ar wa kansa."
"Munafukan banza, je ka fad'a mana,
in banda tsabar bakin ciki za'a bani 2 million,
kuka wani kwaso kafa kuka zo wai kuma a baku,
kuka sa a ka rage kud'in da za'a bani,
munafurcin banza kawai bansan me na tsare muku ba kuka bi kuka samin ido,
tun da Dad da Abbieh suna gida zan sami cikon miliyan d'ayan da kuka yi bakin cikin acika min,
'yan sa ido kawai."
Ya juya ya wuce.
Ajeemal ya ce
"Mujen ku kurabu da shi dan Allah Allah ya bashi sa'a."
Su Ajeemal suna fita Daddy ya gyara zaman shi bayan ya tura kira a wayarsa.
har kiran nashirin yankewa kafin aka d'aga.
Daddy ya amsa sallama had'e da gaisuwar da yake masa, sannan ya d'aura da fad'in
"Ya aikin dan naga alama aiki na shirin ya fimu a gurin ka, yanzu sai kayi kwana hud'u biyar sati baka neme mu ba,
mu in mun neme ka ma sai munyi da gaske muke samin ka,
yanzu ma har na cire rai da samin ka, watakila kana gidane yanzun ma yasa na same ka akan lokaci."
daga cikin wayar ya ce
"Kayi hakuri Daddy yanayin aikin namu ne, kwana biyun nan ina yawan shiga CS ne shiyasa bana samin time d'in d'aukar wayar, ya cikin gidan duk kuna lafiya?."
Daddy ya ce
"Kowa lafiya, kaifa kana lafiya?."
d'an gajeren tsaki ya sake cikin yanayin gajiya da kosawa ya ce
"Daddy bana samin bacci kwana biyu, kusan a tsaye nake kwana,
majinyatan Israel yawancin nan ake shigowa da su,
I'm busy this moment, nagaji kaina yana yawan ciwo,
I will go back to Nigeria very soon,
in ba haka ba zan iya samin bp."
Murmushi Daddy ya yi yasan shi sarai baya son damuwa da yawa, shi yasa ma tun farko yaki aikin likitanci sai da Daddy'n ya matsa masa sosai,
dan shi ya taso da burin gadar kakan sa Alhaji Shitu Fiya da kuma shi kansa Daddy'n,
wato harkar noma yafi bukata.
duk da Daddy'n yahanashi sai da ya sami digiri a harkar noma, bayan ya kammala karatun likitancinsa.
Daddy ya ce
"Haka kake cewa last year ma haka kace min zaka dawo amma baka dawo ba,
ya kamata ka dawo gida Nigeria dan kasarmu ma tana da bukatar ka,
duk d'inbin kud'in da suke biyan ka a can, ko da kasarka bata biyaka rabin sa ba,
yafi ka zauna a can kana musu aiki kadawo ka ceci al'ummar kasarka."
"Daddy ni fa aje aikin zanyi gaba d'aya, nagaji da shi,
zan dawo gida na huta."
"A'a bazaka aje aiki ba, aikin lada ai ba'a gajiya da shi, yanzu kasan ladan da kake samu na ceton rayukan da kake,
ko iya musulman Israel d'in da ka ceta ai lada me yawa ka samu,
duk da gwamnatin kasar ce ke biyan ka ai kana samin lada, dan wannan aikin Allah ne kad'ai ke iya biyan bawa bawai kud'in da ake biyan sa ba."
"Hmm."
kawai ya ce dan shi fa aikin ne baya so, baya son hayani ko kad'an.
Daddy ya ce
"Dr Omar, High Doctor of General Hospital, ya kirani da kansa ranar,
jiya ma yasake kirana yana min tuni,
mai girma gwamnan jihar nan Lagos ya tambaye ka da kansa, ana bukatar ka a kasarka a jihar nan,
me yasa bazaka dawo ka koma bakin aikin kaba, ga asibitocin ka ma kana ganin ma'aikatan ciki sun wadatar,
ka sa rana ka tattaro ka dawo kasar ka."
Shiru ya yi batare da yakuma cewa komai ba.
Daddy ya ce
"D'azu su Ajeemal suka zomin da batun wai ka ce su kawo kud'i ka cika musu ka siya musu computer,
to nace kar su tura ma ko sisi,
ka siya musu da kud'in ka,
suna sana'a ne da zasu sami kud'i."
"Daddy ai na ce musu surika zuwa d'aya daga cikin Company duk ranar weekend's,
na tambaye su suka ce min suna zuwa suma sun fara karb'ar salari, ina son sanin hazakarsu ne yasa nace su kawo kud'in."
Daddy ya ce
"Sun ce zasu fara zuwa ni na hanasu zuwa na ce su nutsu da hankalin su da karatu tukun, har su kammala."
Kai ya jinjina sannan ya ce
"To shike nan Daddy saura 10 minute na shiga CS idan na fito zamuyi waya."
"To Allah ya bada sa'a."
sukayi salla ya kashe wayar duka ya turashi gefe.
ahankali ya maida bayan sa jikin lafiyayyen kujerar office d'in sa, ya lumsahe idanun sa, masu d'auke da gashin ido zara-zara luf-luf kamar an zizara masa.
Kyakkyawa ne dogo mai murd'ad'd'in jiki,
yana da tsananin kwarjini da cikar haiba mai cika ido.
akan kyakkyawar fuskarsa zagaye da saje mai kyau da ya karawa fuskarsa kyau, zuwa gyemunsa da baiwuce kamu d'aya ba.
dogon hanci lips mai kyau da taushe,
kwantaccen gashin gira mai yelwa da zara-zaran gashin ido.
gashin kansa baki sutuf a nannad'e yasha gyara sai sheki yake.
yana da faffad'an kirji mai shinfid'e da gashi luf-luf,
daya dad'a kawata faffad'an kirjin nasa.
sai dai shi sam ba fari bane kuma baza'a kirashi da baki can ba, sai dai mu iya cewa wankan tarwad'a wato chocolate kolo.
Dr Abdurrahim Abubakar Shitu Fiya kenan.
inkiya (A.A FIYA)
Daddy ya dube sa yana fad'in
"Ya akayi kuma?."
dad'a tsunkuyar da kai ya yi yana shafo keyarsa sannan ya ce
"Am dama Daddy wani d'an kud'i ne nake da bukatar su."
Sallamar da su Ajeemal sukayi ne ya katse shi daga abin da yake son fad'a.
Daddy ya amsa suka karaso suka zazzauna kasan carpet suna gaida Daddy'n.
ya amsa yana tambayarsu sun tashi lafiya?.
duk suka amsa da lafiya lau.
Suma zaman suka gyara da alamar akwai abin da ke tafe da su.
Daddy ya dubi Zaraddin ya ce
"Uhum ina jin ka Zaraddin me ke tafe da kai?."
Zaraddin yabi su Ajeemal da kallon kasa-kasa duk ya harare su kana ya muskuta ya ce
"Da ma Daddy kud'i nake so, abokin mu ne zaiyi aure yau, ina kuma niman izini ba a garin nan za'ayi bikin ba, zamuje mu kwana d'aya gobe zamu dawo."
Daddy ya ce
"Nawa ne kake bukata?."
kai ya d'an sosa sannan ya ce
"2 million ne Daddy."
Daddy ya d'aga ido ya kalle shi kana ya ce
"1 million za'a baka sai ka lallab'a, ka koyi yadda ake maneji."
Faisal ya zubawa Zaraddin ido da mamakin karyar da ya sharara yanzu,
wanda yana jin sa sanda ya fito zai zo gurin Daddy yazo zai wuce ta kofar bedroom d'in sa yaji yana waya,
yana sanarwa wani abokin sa yau da karfe 12 na dare akwai birthday party na girl friend d'in su.
"Wato acan zaije ya kwana ke nan."
ya girgiza kai
Maganar Daddy ne yasashi maida hankali gurin sa
"Ku me ke tafe da ku?."
Ajeemal yad'an gyara zama sannan ya ce
"Daddy muna so ka cika mana kud'i ne mu siyi sabon computer, muna son mu samu babban namu saboda yanayin karatun mu."
Daddy ya jinjina kai ya ce
"Nawa ne cikon kud'in naku?."
Shamsuddin ya ce
"2-2 millons ne kud'in computer amma 1 million muke so a cika mana."
Faisal ya karb'i batun da cewa
"Mun samu irin wanda muke so a Germany zamuyi odar sa can."
"To madalla hakan abune me kyau."
Daddy ya fad'a yana d'aukar d'aya daga cikin wayoyin sa.
Ya yi wa ko wannensu transfer d'in million d'aya da rabi.
sannan ya dube su yana fad'in
"Miliyan d'aya da rabi-rabi na sa muku sai ku aje 500k ko wata bukatar zata taso muku,
kai Zaraddin sai kayi hidimar bikin da zakuyi, amma kai banji kace zaka sayi computer ba, ko kana da ita ne?."
Gefen kansa ya sosa ya ce
"Am eh.eh..idan na dawo ne zan yi maganar ni ma."
"To shike nan sai ku tashi kuje Allah ya yi jagora,
amma Shamsuddin Ajeemal Faisal wazai yi muku odar daga can bazakuyi wa d'an'uwanku magana, tun da yana can,
ya sako muku a jirgi ba, ko kun yarda da wanda zakuyi harkar da shi ne?."
Ajeemal ya ce
"Daddy shine ma zamu tura masa, munyi magana da shi ne kan muna son sabon computer shine ya ce,
mu turo da rabin kud'i sai ya cika ya siya mana."
Daddy ya ce
"Inji sa ya ce sai kun bada rabin kud'i kafin ya siya muku abu?
to duk ku maido min da kud'i na kuce masa nace ko sisi bazaku bada ba shi zai siya muku da kud'in sa,
ya baku sana'ar yi ne da zaku sami kud'i da har zaice ku bada rabin kud'i? a ina zaku sami kud'in kuna 'yan makaranta yabari idan kuka gama karatu kuka kama aiki shine zaiyi wannan maganar,
maza-maza kuce dashi na ce ko sisi bazaku bashi ba shi zai saya muku da kud'in sa."
Duk suka zaro wayoyin su suna kokarin maida masa kud'in da ya tura musu.
ya ce "Ku bar shi ku adana idan kuna da bukatar wani abin sai kuyi da shi, kada ku kuskura ku tura masa ko sisi cikin kud'in nan."
suka amsa da to sukayi masa godiya suka mike suka fito.
Suna fita Faisal ya dubi Zaraddin da yayi kicin-kicin da fuska, yana harararsu ya ce
"Yanzu kayiwa Daddy irin wannan karyar alhalin party zakaje kace zakayi tafiya,
ina jin kafa d'azu kana waya zakuje birthday party 12 na dare."
baki Shamsuddin ya bud'e ya rike hab'a ya ce
"Kasan da wannan Faisal shine kana ji ya yi wa Daddy karya,
ya ce zaije bikin abokin sa, ashe party zaije ya kwana a can,
to wlh sai na fad'awa Daddy tun da har abun naka yakai ka fara kwana a Club."
ya juya zai koma parlour'n Daddy.
Ajeemal ya ruko sa yana fad'in
"Rabu da shi karma kaje ka barshi yaci gaba tun da hakan ya zab'ar wa kansa."
"Munafukan banza, je ka fad'a mana,
in banda tsabar bakin ciki za'a bani 2 million,
kuka wani kwaso kafa kuka zo wai kuma a baku,
kuka sa a ka rage kud'in da za'a bani,
munafurcin banza kawai bansan me na tsare muku ba kuka bi kuka samin ido,
tun da Dad da Abbieh suna gida zan sami cikon miliyan d'ayan da kuka yi bakin cikin acika min,
'yan sa ido kawai."
Ya juya ya wuce.
Ajeemal ya ce
"Mujen ku kurabu da shi dan Allah Allah ya bashi sa'a."
Su Ajeemal suna fita Daddy ya gyara zaman shi bayan ya tura kira a wayarsa.
har kiran nashirin yankewa kafin aka d'aga.
Daddy ya amsa sallama had'e da gaisuwar da yake masa, sannan ya d'aura da fad'in
"Ya aikin dan naga alama aiki na shirin ya fimu a gurin ka, yanzu sai kayi kwana hud'u biyar sati baka neme mu ba,
mu in mun neme ka ma sai munyi da gaske muke samin ka,
yanzu ma har na cire rai da samin ka, watakila kana gidane yanzun ma yasa na same ka akan lokaci."
daga cikin wayar ya ce
"Kayi hakuri Daddy yanayin aikin namu ne, kwana biyun nan ina yawan shiga CS ne shiyasa bana samin time d'in d'aukar wayar, ya cikin gidan duk kuna lafiya?."
Daddy ya ce
"Kowa lafiya, kaifa kana lafiya?."
d'an gajeren tsaki ya sake cikin yanayin gajiya da kosawa ya ce
"Daddy bana samin bacci kwana biyu, kusan a tsaye nake kwana,
majinyatan Israel yawancin nan ake shigowa da su,
I'm busy this moment, nagaji kaina yana yawan ciwo,
I will go back to Nigeria very soon,
in ba haka ba zan iya samin bp."
Murmushi Daddy ya yi yasan shi sarai baya son damuwa da yawa, shi yasa ma tun farko yaki aikin likitanci sai da Daddy'n ya matsa masa sosai,
dan shi ya taso da burin gadar kakan sa Alhaji Shitu Fiya da kuma shi kansa Daddy'n,
wato harkar noma yafi bukata.
duk da Daddy'n yahanashi sai da ya sami digiri a harkar noma, bayan ya kammala karatun likitancinsa.
Daddy ya ce
"Haka kake cewa last year ma haka kace min zaka dawo amma baka dawo ba,
ya kamata ka dawo gida Nigeria dan kasarmu ma tana da bukatar ka,
duk d'inbin kud'in da suke biyan ka a can, ko da kasarka bata biyaka rabin sa ba,
yafi ka zauna a can kana musu aiki kadawo ka ceci al'ummar kasarka."
"Daddy ni fa aje aikin zanyi gaba d'aya, nagaji da shi,
zan dawo gida na huta."
"A'a bazaka aje aiki ba, aikin lada ai ba'a gajiya da shi, yanzu kasan ladan da kake samu na ceton rayukan da kake,
ko iya musulman Israel d'in da ka ceta ai lada me yawa ka samu,
duk da gwamnatin kasar ce ke biyan ka ai kana samin lada, dan wannan aikin Allah ne kad'ai ke iya biyan bawa bawai kud'in da ake biyan sa ba."
"Hmm."
kawai ya ce dan shi fa aikin ne baya so, baya son hayani ko kad'an.
Daddy ya ce
"Dr Omar, High Doctor of General Hospital, ya kirani da kansa ranar,
jiya ma yasake kirana yana min tuni,
mai girma gwamnan jihar nan Lagos ya tambaye ka da kansa, ana bukatar ka a kasarka a jihar nan,
me yasa bazaka dawo ka koma bakin aikin kaba, ga asibitocin ka ma kana ganin ma'aikatan ciki sun wadatar,
ka sa rana ka tattaro ka dawo kasar ka."
Shiru ya yi batare da yakuma cewa komai ba.
Daddy ya ce
"D'azu su Ajeemal suka zomin da batun wai ka ce su kawo kud'i ka cika musu ka siya musu computer,
to nace kar su tura ma ko sisi,
ka siya musu da kud'in ka,
suna sana'a ne da zasu sami kud'i."
"Daddy ai na ce musu surika zuwa d'aya daga cikin Company duk ranar weekend's,
na tambaye su suka ce min suna zuwa suma sun fara karb'ar salari, ina son sanin hazakarsu ne yasa nace su kawo kud'in."
Daddy ya ce
"Sun ce zasu fara zuwa ni na hanasu zuwa na ce su nutsu da hankalin su da karatu tukun, har su kammala."
Kai ya jinjina sannan ya ce
"To shike nan Daddy saura 10 minute na shiga CS idan na fito zamuyi waya."
"To Allah ya bada sa'a."
sukayi salla ya kashe wayar duka ya turashi gefe.
ahankali ya maida bayan sa jikin lafiyayyen kujerar office d'in sa, ya lumsahe idanun sa, masu d'auke da gashin ido zara-zara luf-luf kamar an zizara masa.
Kyakkyawa ne dogo mai murd'ad'd'in jiki,
yana da tsananin kwarjini da cikar haiba mai cika ido.
akan kyakkyawar fuskarsa zagaye da saje mai kyau da ya karawa fuskarsa kyau, zuwa gyemunsa da baiwuce kamu d'aya ba.
dogon hanci lips mai kyau da taushe,
kwantaccen gashin gira mai yelwa da zara-zaran gashin ido.
gashin kansa baki sutuf a nannad'e yasha gyara sai sheki yake.
yana da faffad'an kirji mai shinfid'e da gashi luf-luf,
daya dad'a kawata faffad'an kirjin nasa.
sai dai shi sam ba fari bane kuma baza'a kirashi da baki can ba, sai dai mu iya cewa wankan tarwad'a wato chocolate kolo.
Dr Abdurrahim Abubakar Shitu Fiya kenan.
inkiya (A.A FIYA)