Sashe 43
Feeryal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Why!."
ya furta a file sai kuma ya yi gajeren tsaki.
ya na bud'e idanun nasa,ya janye shi daga gareta ya matsa gefe, yasoma had'a abubuwan da zai yi mata amfani da su wajen bata taimakon gaggawa.
ya taho dasu bakin gadon.
tsayuwar sa ya gyara, a hanlali ya kamo tsinsiyar hannunta, da yatsunsa biyu kamar baya son tab'awa, idanunsa yana kan na'urar da yake ta kokarin saita shi.
2 seconds yana rike da hannun nata, tsaki ya ja sai kuma ya saki hannun,
ya dad'a matsowa yakai hannunsa ta saman wuyan rigar baccin jikinta yad'an jashi kasa,
ya saka yatsarsa a jikin jijiyar gefen wuyanta,
2 seconds nan ma yatsarsa yana gurin, kana ya janye.
ya d'an juyo ya dubi nurse d'in da ke tsaye a gefen sa ya ce
"Je ka kirasu suzo su d'auke ta ta mutu."
da sauri ya juya ya fita yaje ya sanar musu.
a razane duk suka mike suka had'a baki wajen fad'in
"What!."
Major Sadam da ya ji kansa na juyawa ya nufi kofar ICU Nasir na biye da shi.
ya tura kofar da karfi yana fad'in
"No bazai yuwu ace ta mutu ba! ya za'ayi kace ta mutu no bazai yuwu ba!."
gefe Dr A.A Fiya ya matsa yana zura hannayen sa cikin aljuhu, tare da mara baki ganin yadda Major Sadam yawani birkice ya yi kanta yana fad'in
"FEERYAL please ki tashi no bazai yuwu ace kin mutu ba!."
ya jijjiga hannunta yana kiran sunanta.
sai kuma yayi wani irin juyowa yana duban Dr A.A Fiya da jajayen ido
ya ce
"Kar ka sake kabari ta mutu, wlh idan ta mutu da kai da b'arayin can, tare zakuyi freezing sannan na harbe ku da kaina, kayi mata abin da zaisa ta tashi!."
Sadam ya fad'a da karfi yana jijjiga kafad'ar Dr A.A Fiya.
ture hannunsa ya yi daga kafad'arsa ya ce
"Kai ka dawo da ita mana kayi mata abinda zaisa tatashin,
ka d'auke ta ku fita min a asibiti ni na gama nawa sai kaje kayi yadda zata tashin a can waje."
Inspector Nasir ya matso da sauri yana fad'in
"Please let me know Dr da gaske ta mutu!?."
kafad'a ya d'aga kana ya ce
"Ina tunanin hakan."
da sauri Nasir ya rike hannunsa ya ce
"No! tunani kake, bai tabbata ba, ka taimaka ka sake gwadawa insha'allah zata tashi, aikin ka ne mu bamusan yadda zamuyi da ita ba, dan Allah Dr dan Allah ka taimaka dan Allah dan Allah please help."
ya jijjiga hannunsa yana magiya da rokon sa.
hannu ya d'aga musu yana jifan Major Sadam da mugun kallo kana ya ce
"Ku jira a waje."
Nasir yaja Sadam da sauri sukayi waje.
Gajeren tsaki yaja ya matsa bakin gadon,
ya rike kugu yana dad'a jan tsaki.
sannan a hankali ya kai hannunsa kan cikinta ya janye rigar baccin jikinta da yatsu biyu,
ta d'an sama har zuwa saman cibiyarta, yadda yake yi kamar mai tab'a wani abin kyama da baya son hannunsa ya tab'a.
ya d'au defibrillator yana had'asu, kana ya dad'a matsowa ya manna shi kan cikin ta.
da karfi ta zabura ta kuma komawa tana kokarin kuma shiga dogon suman.
yakuma manna mata sau biyu a jere tawani irin zabura da karfi tare da jan numfashi,
mai had'e da ihu a firgice ta yunkura ta fad'a jikinsa ta tsakalo wuyansa ta kankamesa da karfi tare da fasa kuka,
tana b'oye fuskarta cikin kirjinsa.
cikin fizgar munfashi mai nuni da zallar tsoro wanda a yanzu kwakwalwar ta ke tsaye cak baya nanata komai sai kasantuwarta da b'arayin nan.
cikin had'a kalomomi take fad'in
"Dan Allah.. ka..kayi hakuri kar..kar ka tafi da ni, ni bana sonka bazan aure ka ba."
A fusace ya fisgota da karfi ya cirota a kirjinsa ya turata kan bed d'in, ya yi saurin binta da allura ya dannan mata, ta saki wani uban kara jikinta na rawa.
zuwa can kuma a hankali tashiga sauke numfashi, a hankali a hankali nan da nan bacci ya tafi da ita.
Tsayuwarsa ya gyara tare da gyara zaman singilet d'in jikin sa da ta tukuikuye shi,
yawani had'e rai yana kumbura had'e da jan tsaki, kamar wacce take ganin sa,
a ransa yake fad'in
"Yar wannan abin wai take maganar aure msstt."
yaja tsaki had'e da yin kwafa,
duk ta gajiyar da shi ta makalkale masa wuya,
kwafa ya yi a fili.
kana nan da nan ya shiga bata taimakon gaggawa, yana yi yana jan gajeren tsaki da kaga yadda yake dai zakasan bawai da son ransa yake taimakon nata ba.
daga bisani ya d'aura mata drip had'e da ruwan allurai masu karfi da inganci.
yana gamawa kuwa ya juya bai kuma waiwayota ba ya yi gaba abinsa.
nurse yashiga kimsa abubuwan da yayi amfani da su.
Yana fita Major Sadam da Inspector Nasir suka mike suna son jin meke faruwa kuma yanzu.
Nasir ya ce
"Ka sami nasarar cito rayuwarta kuwa?."
"Kushiga ku duba."
yafad'a a takaice.
da sauri sukayi cikin room d'in, shiko yasa kai ya fice a asibitin.
Wani numfashi Major Sadam ya sauke ganinta a kwance tana numfashi, sai dai idanunta a fure da alama dai bacci take.
Nasir ya ce
"Alhamdulillah!."
nurse d'in dake ta kimsa gurin ya yi murmushi yana cewa
"Ai tun da Dr A.A Fiya ne ya fara jinyarta da kansa ai insha'allah zata tashi."
Sai a lokacin suka sami sukuni ganin ta farfad'o har ta sami bacci.
wajen karfe 3 da rabi na dare.
nan suka fita a asibitin bayan sun aje jami'an tsaro kewaye da asibitin.
A b'angaren su Hajja Umma kuwa, ranar sunga tashin hankali.
ga tashin hankalin sace FEERYAL ga karar harb'e-harben da ya birkita cikin unguwar kamr za'a tada unguwar da harbi. bayan lafawar tarzoman,
aka turo jami'an tsaro gidan, yadda sukaga rana haka sukaga dare kowa a zaune ya kwana cikin zullumi da fargaba.
duk da Inspector Nasir ya sanar musu sun kwato FEERYAL a hannun 'yan ta'addan nan sai dai a dame suke da son jin halin da take ciki, dan ya sanar musu tana asibiti.
fatan su dai Allah yasa ba harbinta akayi ko wani abun b'arayin sukayi mata ba.
a cikin daren Nasir yasanar musu ta farfad'o.
Abba ya ce zasuje su ganta, ya ce subari
gari ya waye tukun, tana cikin tsaro sosai a asibitin.
A b'angaren Dr A.A Fiya kuwa, yana komawa gidan sa.
ya fad'a bathroom ya yi wanka tare da d'auro al'waka ya zura jallabi, ya haye kan sallaya yasoma gabatar da sallar nafila,
har sai da aka kira sallar asuba kana ya fita zuwa masallaci.
bayan an idar ya gabatar da azkhar sannan ya nufo gida.
yana shiga bedroom d'in sa ya soma had'a kaya, ya janyo wayarsa ya daddannan kana ya kara a kunnensa.
ringing d'aya ana biyu a ka d'aga.
"Zo ka kaini airport 6:30 airplane zai tashi."
yana fad'in haka ya kashe wayar.
Dr Imran yabi wayar da kallo yana nanata kalmar da ya fad'a.
ya maida kiran nasa yana d'agawa Dr Imran ya ce
"A.A wai ina zakaje ne da asuba d'in nan?."
"Kana b'ata min lokaci kafito kazo ka kai ni ko na aje motar a can airport kazo ka d'auko ta."
ya kashe wayar.
da sauri Dr Imran ya mike yafito daga gidan kwanan likitoci, wan da shima d'aya ne daga cikin gidajen sa da suke cikin unguwar. likitoci ma'aikatan asibitin sa ne suke zaune a ciki.
Dr Imran na shiga gidan nasa ya hangosa a parking lot yana saka jakarsa cikin mota.
ya karaso da sauri ya iso gurin.
key'n motar ya jefawa Dr Imran kana yabud'e gaban motar ya shiga ya zauna yana fad'in
"Yi sauri muje time na tafiya."
Dr Imran yashiga mazaunin direba ya juyo yana duban sa.
"A.A wai ina zakaje ne shekaran jiya-jiyan nan fa ka shigo, ko zaka shiga Lagos ne kabari na shirya mu tafi tare mana."
"Germany zan koma kamar nafi samin bacci da hutu acan, na zo dan na huta amma jiya ko rumtsawa ba'a barni nayi ba, akan wata yarinyar da ma ba lallaine tayi raiba,
haka shikaran jiya ina sauka kuka wani barni da patent, ba gara na koma ba kawai."
baki Dr Imran ya bud'e da mamaki yake kallonsa, sannan ya ce
"Kayi hakuri ka bar tafiyar nan, shima can ai duk aikin ne idan ka koma,
ka dai sani patient zaman jiranka suke, suna sanin komawar ka kuwa zasu taho ganin ka, kuma dole ka duba su, kaga ba hutu ke nan can d'inma."
"Dan Allah muje."
yafad'a yana nuna masa hanya
Dr Imran ya girgiza kai ya yi wa motar key mai gadi ya bud'e suka fice a gidan.
A hanya Dr Imran ya yi ta bashi baki ko zai canza shawari ya hakura da tafiyar, amma sai ce wa ya yi, maganar Imran d'in ma karasa masa gajiya take, yabar cika masa kunne.
sanin halinsa yasa Dr Imran yin shiru, har suka isa airport suna isa kuwa baifi da minti 10 ba jirgi ta d'aga.
Dr Imran ya juyo gida.
tun daga kwanar shiga layin ya hango motar sojoji dana police a kofar asibitin su.
har zai wuce gida kafin ya yi shirin fitowa asibitin. sai kuma ya yi kwana ya shige asibitin dan son sanin me ke faruwa.
Major Sadam da Inspector Nasir da shigowarsu kenan yagani tsaye a parlour'n asibitin, suna tambayar nurse's har yanzu likitan bai zoba suma sauran likitocin basu fito?.
suna kokarin basu amsa Dr Imran ya shigo.
suka nuna shi suna cewa ga Dr d'aya ma ya shigo.
inspector Nasir ya dubi Dr Imran ya mika masa hannu suka gaisa kana ya ce
"Muna da patient a ciki jiya muka kawo ta da daddare, patient in Dr A.A Fiya ne, amma kamar bai shigo asibiti har yanzu ba ko?."
Dr Imran ya ce
"Eh bai shigo ba tukun, amma ta fard'o kuwa Jasin?."
ya karasa maganar yana duban nurse Jasin ya nufi ICU Nurse Jasin ya biyo bayansa yana fad'in
"Sir har yanzu tana bacci, akwai allurar bacci cikin drip d'in da ke shiga jikinta."
kai ya jinjina dai-dai san da suke shigewa cikin room d'in.
ya furta a file sai kuma ya yi gajeren tsaki.
ya na bud'e idanun nasa,ya janye shi daga gareta ya matsa gefe, yasoma had'a abubuwan da zai yi mata amfani da su wajen bata taimakon gaggawa.
ya taho dasu bakin gadon.
tsayuwar sa ya gyara, a hanlali ya kamo tsinsiyar hannunta, da yatsunsa biyu kamar baya son tab'awa, idanunsa yana kan na'urar da yake ta kokarin saita shi.
2 seconds yana rike da hannun nata, tsaki ya ja sai kuma ya saki hannun,
ya dad'a matsowa yakai hannunsa ta saman wuyan rigar baccin jikinta yad'an jashi kasa,
ya saka yatsarsa a jikin jijiyar gefen wuyanta,
2 seconds nan ma yatsarsa yana gurin, kana ya janye.
ya d'an juyo ya dubi nurse d'in da ke tsaye a gefen sa ya ce
"Je ka kirasu suzo su d'auke ta ta mutu."
da sauri ya juya ya fita yaje ya sanar musu.
a razane duk suka mike suka had'a baki wajen fad'in
"What!."
Major Sadam da ya ji kansa na juyawa ya nufi kofar ICU Nasir na biye da shi.
ya tura kofar da karfi yana fad'in
"No bazai yuwu ace ta mutu ba! ya za'ayi kace ta mutu no bazai yuwu ba!."
gefe Dr A.A Fiya ya matsa yana zura hannayen sa cikin aljuhu, tare da mara baki ganin yadda Major Sadam yawani birkice ya yi kanta yana fad'in
"FEERYAL please ki tashi no bazai yuwu ace kin mutu ba!."
ya jijjiga hannunta yana kiran sunanta.
sai kuma yayi wani irin juyowa yana duban Dr A.A Fiya da jajayen ido
ya ce
"Kar ka sake kabari ta mutu, wlh idan ta mutu da kai da b'arayin can, tare zakuyi freezing sannan na harbe ku da kaina, kayi mata abin da zaisa ta tashi!."
Sadam ya fad'a da karfi yana jijjiga kafad'ar Dr A.A Fiya.
ture hannunsa ya yi daga kafad'arsa ya ce
"Kai ka dawo da ita mana kayi mata abinda zaisa tatashin,
ka d'auke ta ku fita min a asibiti ni na gama nawa sai kaje kayi yadda zata tashin a can waje."
Inspector Nasir ya matso da sauri yana fad'in
"Please let me know Dr da gaske ta mutu!?."
kafad'a ya d'aga kana ya ce
"Ina tunanin hakan."
da sauri Nasir ya rike hannunsa ya ce
"No! tunani kake, bai tabbata ba, ka taimaka ka sake gwadawa insha'allah zata tashi, aikin ka ne mu bamusan yadda zamuyi da ita ba, dan Allah Dr dan Allah ka taimaka dan Allah dan Allah please help."
ya jijjiga hannunsa yana magiya da rokon sa.
hannu ya d'aga musu yana jifan Major Sadam da mugun kallo kana ya ce
"Ku jira a waje."
Nasir yaja Sadam da sauri sukayi waje.
Gajeren tsaki yaja ya matsa bakin gadon,
ya rike kugu yana dad'a jan tsaki.
sannan a hankali ya kai hannunsa kan cikinta ya janye rigar baccin jikinta da yatsu biyu,
ta d'an sama har zuwa saman cibiyarta, yadda yake yi kamar mai tab'a wani abin kyama da baya son hannunsa ya tab'a.
ya d'au defibrillator yana had'asu, kana ya dad'a matsowa ya manna shi kan cikin ta.
da karfi ta zabura ta kuma komawa tana kokarin kuma shiga dogon suman.
yakuma manna mata sau biyu a jere tawani irin zabura da karfi tare da jan numfashi,
mai had'e da ihu a firgice ta yunkura ta fad'a jikinsa ta tsakalo wuyansa ta kankamesa da karfi tare da fasa kuka,
tana b'oye fuskarta cikin kirjinsa.
cikin fizgar munfashi mai nuni da zallar tsoro wanda a yanzu kwakwalwar ta ke tsaye cak baya nanata komai sai kasantuwarta da b'arayin nan.
cikin had'a kalomomi take fad'in
"Dan Allah.. ka..kayi hakuri kar..kar ka tafi da ni, ni bana sonka bazan aure ka ba."
A fusace ya fisgota da karfi ya cirota a kirjinsa ya turata kan bed d'in, ya yi saurin binta da allura ya dannan mata, ta saki wani uban kara jikinta na rawa.
zuwa can kuma a hankali tashiga sauke numfashi, a hankali a hankali nan da nan bacci ya tafi da ita.
Tsayuwarsa ya gyara tare da gyara zaman singilet d'in jikin sa da ta tukuikuye shi,
yawani had'e rai yana kumbura had'e da jan tsaki, kamar wacce take ganin sa,
a ransa yake fad'in
"Yar wannan abin wai take maganar aure msstt."
yaja tsaki had'e da yin kwafa,
duk ta gajiyar da shi ta makalkale masa wuya,
kwafa ya yi a fili.
kana nan da nan ya shiga bata taimakon gaggawa, yana yi yana jan gajeren tsaki da kaga yadda yake dai zakasan bawai da son ransa yake taimakon nata ba.
daga bisani ya d'aura mata drip had'e da ruwan allurai masu karfi da inganci.
yana gamawa kuwa ya juya bai kuma waiwayota ba ya yi gaba abinsa.
nurse yashiga kimsa abubuwan da yayi amfani da su.
Yana fita Major Sadam da Inspector Nasir suka mike suna son jin meke faruwa kuma yanzu.
Nasir ya ce
"Ka sami nasarar cito rayuwarta kuwa?."
"Kushiga ku duba."
yafad'a a takaice.
da sauri sukayi cikin room d'in, shiko yasa kai ya fice a asibitin.
Wani numfashi Major Sadam ya sauke ganinta a kwance tana numfashi, sai dai idanunta a fure da alama dai bacci take.
Nasir ya ce
"Alhamdulillah!."
nurse d'in dake ta kimsa gurin ya yi murmushi yana cewa
"Ai tun da Dr A.A Fiya ne ya fara jinyarta da kansa ai insha'allah zata tashi."
Sai a lokacin suka sami sukuni ganin ta farfad'o har ta sami bacci.
wajen karfe 3 da rabi na dare.
nan suka fita a asibitin bayan sun aje jami'an tsaro kewaye da asibitin.
A b'angaren su Hajja Umma kuwa, ranar sunga tashin hankali.
ga tashin hankalin sace FEERYAL ga karar harb'e-harben da ya birkita cikin unguwar kamr za'a tada unguwar da harbi. bayan lafawar tarzoman,
aka turo jami'an tsaro gidan, yadda sukaga rana haka sukaga dare kowa a zaune ya kwana cikin zullumi da fargaba.
duk da Inspector Nasir ya sanar musu sun kwato FEERYAL a hannun 'yan ta'addan nan sai dai a dame suke da son jin halin da take ciki, dan ya sanar musu tana asibiti.
fatan su dai Allah yasa ba harbinta akayi ko wani abun b'arayin sukayi mata ba.
a cikin daren Nasir yasanar musu ta farfad'o.
Abba ya ce zasuje su ganta, ya ce subari
gari ya waye tukun, tana cikin tsaro sosai a asibitin.
A b'angaren Dr A.A Fiya kuwa, yana komawa gidan sa.
ya fad'a bathroom ya yi wanka tare da d'auro al'waka ya zura jallabi, ya haye kan sallaya yasoma gabatar da sallar nafila,
har sai da aka kira sallar asuba kana ya fita zuwa masallaci.
bayan an idar ya gabatar da azkhar sannan ya nufo gida.
yana shiga bedroom d'in sa ya soma had'a kaya, ya janyo wayarsa ya daddannan kana ya kara a kunnensa.
ringing d'aya ana biyu a ka d'aga.
"Zo ka kaini airport 6:30 airplane zai tashi."
yana fad'in haka ya kashe wayar.
Dr Imran yabi wayar da kallo yana nanata kalmar da ya fad'a.
ya maida kiran nasa yana d'agawa Dr Imran ya ce
"A.A wai ina zakaje ne da asuba d'in nan?."
"Kana b'ata min lokaci kafito kazo ka kai ni ko na aje motar a can airport kazo ka d'auko ta."
ya kashe wayar.
da sauri Dr Imran ya mike yafito daga gidan kwanan likitoci, wan da shima d'aya ne daga cikin gidajen sa da suke cikin unguwar. likitoci ma'aikatan asibitin sa ne suke zaune a ciki.
Dr Imran na shiga gidan nasa ya hangosa a parking lot yana saka jakarsa cikin mota.
ya karaso da sauri ya iso gurin.
key'n motar ya jefawa Dr Imran kana yabud'e gaban motar ya shiga ya zauna yana fad'in
"Yi sauri muje time na tafiya."
Dr Imran yashiga mazaunin direba ya juyo yana duban sa.
"A.A wai ina zakaje ne shekaran jiya-jiyan nan fa ka shigo, ko zaka shiga Lagos ne kabari na shirya mu tafi tare mana."
"Germany zan koma kamar nafi samin bacci da hutu acan, na zo dan na huta amma jiya ko rumtsawa ba'a barni nayi ba, akan wata yarinyar da ma ba lallaine tayi raiba,
haka shikaran jiya ina sauka kuka wani barni da patent, ba gara na koma ba kawai."
baki Dr Imran ya bud'e da mamaki yake kallonsa, sannan ya ce
"Kayi hakuri ka bar tafiyar nan, shima can ai duk aikin ne idan ka koma,
ka dai sani patient zaman jiranka suke, suna sanin komawar ka kuwa zasu taho ganin ka, kuma dole ka duba su, kaga ba hutu ke nan can d'inma."
"Dan Allah muje."
yafad'a yana nuna masa hanya
Dr Imran ya girgiza kai ya yi wa motar key mai gadi ya bud'e suka fice a gidan.
A hanya Dr Imran ya yi ta bashi baki ko zai canza shawari ya hakura da tafiyar, amma sai ce wa ya yi, maganar Imran d'in ma karasa masa gajiya take, yabar cika masa kunne.
sanin halinsa yasa Dr Imran yin shiru, har suka isa airport suna isa kuwa baifi da minti 10 ba jirgi ta d'aga.
Dr Imran ya juyo gida.
tun daga kwanar shiga layin ya hango motar sojoji dana police a kofar asibitin su.
har zai wuce gida kafin ya yi shirin fitowa asibitin. sai kuma ya yi kwana ya shige asibitin dan son sanin me ke faruwa.
Major Sadam da Inspector Nasir da shigowarsu kenan yagani tsaye a parlour'n asibitin, suna tambayar nurse's har yanzu likitan bai zoba suma sauran likitocin basu fito?.
suna kokarin basu amsa Dr Imran ya shigo.
suka nuna shi suna cewa ga Dr d'aya ma ya shigo.
inspector Nasir ya dubi Dr Imran ya mika masa hannu suka gaisa kana ya ce
"Muna da patient a ciki jiya muka kawo ta da daddare, patient in Dr A.A Fiya ne, amma kamar bai shigo asibiti har yanzu ba ko?."
Dr Imran ya ce
"Eh bai shigo ba tukun, amma ta fard'o kuwa Jasin?."
ya karasa maganar yana duban nurse Jasin ya nufi ICU Nurse Jasin ya biyo bayansa yana fad'in
"Sir har yanzu tana bacci, akwai allurar bacci cikin drip d'in da ke shiga jikinta."
kai ya jinjina dai-dai san da suke shigewa cikin room d'in.