← Book details Dr Khaleed Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 91

Sashe 22

Dr Khaleed Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

[10/10, 6:43 AM] ‪+234 701 117 6189‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar
35.....
Khaleel na shigowa falon yyi mamakin rashin ganin Ashnaah, ya juya yana kallon Zeenat da ke bayansa yace "ina yarinyar nn take" Zeenat ma ta shiga bin falon da kallo tace "xaune naganta daxu kafin in fita ban san inda tayi ba kuma" juyawa da sauri yyi ya fice daga falon xuwa gun mai gadi, "don Allah baba kaga wata ta fita daxu" mai gadin yyi shiru snn yana girgixa kai yace "gskya bbu Wanda ya fita tun bayan fitan hajiya" wani ajiyar xuciya Khaleel ya sauke ba tare da ya sani ba, ya juya ya kuma komawa cikin gidan, har lkcn Zeenat na tsaye gun da ya bar ta, sama ya nufa ya bude dakin Meenah, Meenah na xaune kasan dakin sae faman hira take ma Ashnaah dake xaune kan gadonta tana kyalkyala dariya, tsayawa kallonsu yyi da mamaki, Ashnaah ta dan yi tsaki tace "dalla ci gaba Meenah" Meenah ta Mike daga xaunen da take a kasa ita ma tayi tsakin tace "ni tsoro ma aka ban wllh, mutum in xae shigo dakin mutane ba sae yyi sallama ba" karaso wa cikin dakin Khaleel yyi, Meenah ta nufi bathroom dinta da sauri ta shige ta rufe, Khaleel na ma Ashnaah wani mugun kallo yace "me kike yi a nn" xaro ido tayi tana kallonsa tace "ban gane me nake yi ba, don me ka kawo ni nn, ba don in yi xumunci ba, don kuma ina hira da yar uwarka shine nayi laifi" ta tabe baki ta dauke kanta, kallonta kawae ya tsaya yi, can yace "tashi ki fita" bae rufe baki ba ta galla masa harara tace "sllh xan yi" a fusace ya karaso inda take ya fixgota ta mike a tsorace ta rike hannunsa tace "don Allah kayi hkuri wllh xan fita dama sllh na shigo yi" bata jira me xae ce ba ta fice daga dakin da sauri, dole a bayin kasa tayi alwala yace Zeenat ta dauko mata sallaya tayi sllhn a falo, Zeenat ta sauko rike da darduman ta mika ma Khaleel snn ta koma sama, Ashnaah ta tabe baki tace "ni dae bn aiketa ba, kuma in har ita ke sllh kae to baxan yi ba" Khaleel yace "kin fi ta tsafta ne" mikewa Ashnaah tayi a fusace tace "wnn ce ta fi ni tsafta, Ae da na ji haushi wllh, ko kai ka gwada min tsafta bare wnn bnxar" mikewa yyi yana nunata da yatsa yace "watch ur tongue" ta dauke kanta ta ja tsaki, ya nufi sama don yin alwala ya tafi masallaci. Ashnaah na idar da sllh momy ta shigo, Ashnaah ta yi mata sannu da xuwa ta amsa tace "ke kadae kuma a falo fateema me yasa baki hau sama ba, ina su Aminan suke" Ashnaah tayi murmushi bata ce komae ba, momy ta nufi kitchen, sae ga ta ta fito rike da abinci da drinks a faranti ta kawo ta ajiye gaban Ashnaah tace "ga abinci fateema" Ashnaah tace "ngd momy" takwas saura Khaleel ya shigo gidan, Ashnaah na xaune da momy da Zeenat a falo, momy tace Zeenat ta kawo masa abincin sa kan dining, yace "wllh mum ni kam a koshe nake," Momy tace "me kaci xaka ce ka koshi?" Ashnaah tace "dama hka xae ce momy, sae mun koma gida yace sae na masa girki" da sauri Khaleel ya juya yana kallonta, ta galla masa harara, momy tace "to ku tafi da shi mana, amma da Daren nn wani girki xa a yi in an koma gida" Khaleel yyi murmushi yace "to momy xan tafi da shi" mikewa Khaleel yyi yace "momy dare na yi bari mu kama hanya" momy ta Mike tace "to bari in sa maku kulan a leda" dinnin ta nufa sae ga ta ta dawo da abincin ta mika ma Khaleel, yyi mata gdya Ashnaah ta mike tace "bari mu yi sallama da Meenah" sama ta nufa Khaleel ya bi ta da kallo ba daman ya bi ta, ta samu Meenah ta fito daga wanka tace "ke xa mu tafi, dan yi min copyn din nmbr nn a paper" Meenah tace "to har ynxu ba ki gaya min me xa ki yi ba Ae" Ashnaah tace "ke dae ki rubuta min, yaushe xa ki xo" Meenah tace "aa ni tsoron mijin nn naki nake" Ashnaah tace "dalla can ki xo, me ya isa yyi maki ina nn, Ae baxan bari ba" Meenah tace "to gobe idan Allah ya yrda xan xo" Ashnaah tayi murmushi tace "ko ke fa" nmbrs din Meenah ta kwafe mata a takarda ta mika mata, Ashnaah ta karba ta ce "yawwa kawas sae kin xo" snn ta fice da sauri. Har suka bar gidan Khaleel bae daina Satan kallon Ashnaah ba, sae da suka bar anguwar snn yyi parking yana kallonta fuskarsa a hade yace "me kika je yi a sama" Ashnaah ta ce "sallama fa naje muka yi" yana kallonta da kyau yace "kina ji na" ta yi shiru tana kallonsa, ya ci gaba "bbu ke bbu yarinyar nn, kika bari na sake ganin ku tare sae na..." Da sauri tana hararansa tace "A'ah, sbda me ba yar uwarka bace" fixgota yyi yace "ni kike tambaya sbda me" da sauri tace "aa kayi hkuri na ji wllh" yyi kwafa ya turata, yace "meye kike boyewa cikin hijab" ta Ciro turaren da momy ta bata da sauri ta nuna masa, dauke kansa yyi ya ci gaba da tukinsa. Karfe tara saura Khaleel yyi parking a gidan sa, ya fito yana jiran Ashnaah ta fito, ta fito snn ya kulle motarsa ya nufi cikin gida, ta dan yi tsaki ta shiga bin sa a baya, falo ta same sa a xaune ya kunna TV, yana bude abincin da smll mum dinsa ta basa, Ashnaah ta tsaya daga bayan kujerar da yake xaune ya juya da sauri yana hararanta yace "meye kika wani tsaya a kaina" ta koma baya tace "aa dama cewa xan yi in kawo plate ka debar min don ina jin kunya ban ci da yawa a can ba kuma ynxu yunwa nake ji" tsayawa kallonta kawae Khaleel yyi, can ya girgixa kai yace "kika bari na tashi wllh sae kin sha mamaki, ta shi min a bayana" ya karasa mgnr cikin tsawa, ta koma baya da sauri don ta ji tsoron tsawan da yyi mata, can tayi tsaki ta nufi sama kmr xata tashi sama.

36.....
Karfe sha daya da kusan rabi Ashnaah na kwance dakinta bayan ta gama shan tea, kmr warce ta tuna abu ta mike xaune da sauri ta nufi gaban madubinta ta dauki takardan da Meenah ta rubuta mata nmbr dad din Zeenat tana kallo, to ynxu ita ina xata samu wayar da xata kira nmbr nn, ta koma gefen gadonta ta xauna tayi tagumi tana tunane tunane, duk fa na ynda xata samo waya, bude kofar dakinta aka yi ta boye takardan da sauri a bayanta tana kallon kofar, Khaleel ya shigo dakin rike da kulan abincin yana kallonta yace "mayya! kin sa na kware hankalinki ya kwanta, sae ki cinye abincin" yyi tsaki ya fice daga dakin, Ashnaah ta tabe baki tace "ni ba mayya bace sae dae in kai ne mayye" ta mike ta dauko abincin ta bude taga kadan ya ci, naman kam bata ga alaman ya taba ba ma, tayi murmushi ta dauki spoon din ta shiga cin kayanta, tana gamawa ta shiga wanka, ko da ta fito hijab kawae ta xura bayan ta goge jikinta ta dauki kulan da ta ci abinci ta fita don xuwa ta kai shi kitchen.

~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar
37.....
Ashnaah ta tabe baki ganin duk ya kashe wutan gidan sae dim blue light da ya bari a kunne a falon, kitchen ta nufa ta kunna wuta ta ajiye abin hannunta a sink snn ta kashe wutan ta fito ta kulle kitchen din ta nufi sama, har ta bude dakinta xa ta shiga sae kuma ta juya tana kallon kofar Khaleel, to ko dae ta sato wayarsa ynxu ne tayi abinda xata yi don bata son ya riga ta kiran dad din Zeenat, a hankali ta nufi kofar falonsa, ta kusa minti biyar tana tunanin ta shiga ko kar ta shiga, daga karshe ta murda kofar a hankali ta leka falon ta ga a kashe wutan falon yake, hkn yasa ta shiga ta karasa xuwa bedroom dinsa cikin sanda, ta ji kofar ma a rufe, gabanta ya shiga faduwa, to in idonsa biyu ya xata yi knn, tunanin hkn yasa ta kuma tsorata ta juya da gudu ta koma can bakin kofar falon xuciyarta na bugawa, kamshin sabulu da ta dinga ji ya gauraye duk falon yasa tace to ko dae wanka yake, komawa kofar dakin tayi ta kasa kunne bakin kofar taji kmr saukan ruwa a bayi, hkn yasa ta murda kofar a hankali inda Allah ya taimake ta ma kofar ko kadan baya kara, ta leka dakin taga dim bedside lamp ne kadae a kunne, ta shiga dakin ta nufi gaban madubi da sauri ta laluba bata ga wayar ba, dudduba gado ta shiga yi tana laluba ko ina ko xata gani amma bata ga alamar waya ba, ba karamin haushi hkn ya bata ba har ta fidda rae xata fita ta hango wayar can kan bedside drawer ta daya bangaren da take tsaye, da sauri da sauri ta nufi gun, ta duka ta dauki wayar, ta juya xata bar wajen knn taji an bude kofar bathroom, ji tayi kmr an buga mata guduma a kirji tsabar faduwar gaba, ta tsaya cak har lkcn wayar na hannunta sae rawa jikinta yake, da mugun mamaki Khaleel ke kallonta, ta dake taki kallon inda yake, ta ajiye wayar hannunta ta juya da sauri xata bar wajen yyi saurin fixgota ta fado kirjinsa, dama kuma dae dae nn take kai sa, ta dago kai a tsorace tana kallonsa, ssae taji tsoron ynda ta gansa ta rufe idonta da sauri ta mayar kan faffadan kirjin nasa ta saki kuka tana cewa "wayyo ni fa agogo na xo dubawa na daki na ya tsaya"
Like · 2 · Reply · Report ·
Chapter 22 · 0% Book details