Sashe 46
Dahuwar Ƙaho Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ai wallahi daga yau yaya ya daina saya wa mahaifinta maganin hawan jinin, gara da kika faÉ—a mini. Ina zuwa wallahi kamar Umma ta ji labari..."
Maganarta ta maƙale sakamakon ido huɗu da suka yi da Maman Sudais, murmushin takaici ta sakar mata ta ce.
"Maimuna kenan, na ba ki yarda da aminci ashe cin dunduniyata kike? Idan kuwa ni ce yadda Annabi ya bar duniya na bar ki kenan."
Cike da borin kunya Maimuna ta ce, "To zancenki ake yi da za ki faɗa wa mutane magana? Idan kin bar ni Baban Asiya ne ya bar ni ko me? Ai dama ba zamanki nake yi ba." A ranar haka suka rabu baram-baram dutse a hannun riga, tun daga wannan ranar idan ba abin jaje ko gaisuwa ba ne babu abin da yake haɗa su da Maimuna. Gaisuwar ma sai da Abban Sudais ya takura mata da yake ta sanar da shi komai, kuma shi mutum ne mai fahimta ya ce ta kiyaye zamanta da maƙota. Don haka take takatsantsan da gabaɗayansu, tsakaninta da su sai hirar duniya ko ta yara. Kuma tun daga lokacin ta rage ba su fuska, shi ya sa yawanci suka daina shigar mata sai Maman Nana da take leƙa mata sama-sama.
Sai da Maimuna ta sayo gawayi bayan ta ɗora girki, ta sake shiga ɗaki ta ɗauko sabuwar wayarta da Jafar ya aiko mata, dama tun bayan fitar Nazir ta ciro ta haɗe da saita komai ta yi masa Salam ta whatsapp. Saboda farinciki kamar Jafad zau taka rawa haka suka ɓa ta lokaci suna musayar kalaman soyayya, domin a ranar Maimuna ba ta yi aiki gida da wuri ba. Don haka a yanzun ma da ta koma ta kira shi voice call ta whatsapp da yake ta ga yana online, yana ɗauka suka dasa daga inda suka tsaya. Daga ƙarshe ya ce ta ɗauki hotuna masu kyau ta tura masa. Wannan ne ya sanyaya mata jiki, kuma tsoro ya kamata. Har ta shiga wasu-wasin kada ta zo tsautsayi ya ratsa Maman Nana ta gani, duk da ta ji ya ce mata zai ɓoye amma haja kawai ta ji tana tsoron tura hoton. A ɓangaren ɗaya kuma ta ji kamar ba ta kyauta masa ba, domin shi ya zuba maƙudan kuɗinsa ya saya mata wayar saboda haka. Jin ta shiru ba ta tura masa ba ya sa shi kiranta a waya ya sake tunasar da ita, sai da Jafar ya yi da gaske sannan ra iya tura masa tana sake jadadda masa da ya san yadda zai yi ya adana hoton ta yadda kwaɓarsu ba za ta taɓa yin ruwa tsululu ba.
Nazir irin bauɗaɗɗun mazan nan ne, kuma yana ɗaya daga cikin mazan da ba su damu da ba wa mace haƙuri ko lallaɓa ta ba idan ta yu fushi ko idan sun yi mata laifi. Idan har Maimuna ta ga ya ɗan sakar mata fuska to a ranar yana buƙatar kusantarta ne. Abin da ya fi ci wa Maimuna tuwo a ƙwarya bai wuce rashin ba ta kulawa ba, idan Nazir ya dawo gida ba shi da abokiyar hira sai wayarsa. Koda hira Maimuna ta zauna tana yi masa sai dai ya dinga ba ta amsa sama-sama, amma kaso casa'in cikin ɗari (90%) hankalinsa yana kan wayarsa. Da yake Maimuna tana da ɗan surutu ta dinga yi masa mita kenan, tana nuna ɓacin ranta. Hakan ne ya sa wani lokacin Nazir ba ya dawowa gida da wuri, sai ya gama uzurorinsa a waje. Ya kasance mutum mai takura, bin diddigi da rashin yarda. Don hatta maƙota ba ya barin Maimuna shiga, su ma kuma a ɓoye suke shigo mata bai sani ba. Duk inda Maimuna za ta je shi zai kai ta, kuma bai cika kai ta da rana ba har sai ya dawo daga kasuwa. Kuma idan ya kai ta duk taron da ake yi sai dai ya jira ta a ƙofar gida agama ya tafi da ita. Maimuna tun tana zama ta ci kuka bayan aurensu har abin ya zame mata jiki, kuma sannu a hankali Nazir ya aurensa ya sure mata har take jin Allah Ya kawo sanadin da za su rabu wala mutuwa ko sakin aure. Sakamakon halinsu da ya yi hannun riga da ita, tun da har babbar waya ya hana ta riƙewa a cewarsa duk wani abu da zai buɗe idonta ba zai lamunra ba. Tun da ai sai mace ta yi mu'amala da mutane ake ba ta munanan shawarwari, ko a zuge ta ta sauya halaye. Idan kuwa aka ɗora mace a doron da ya ɗora Maimuna, a ganinsa hakan ne zai daidaita mace ta zama kamila tun da idonta bai buɗe ba.
Tarihin Maimuna
Maimuna 'yar asalin garin Dutse ce da ke jigawa, mahaifi da mahaifiyarta duk 'yan can ne. Kuma su biyar ne a wurin iyayensu, yayanta Sadik shi ne babba sai ita take binsa ƙannenta mata uku suke biye da ita.
Maimuna ta yi karatunta na addini daidai gwargwado, ha boko kuma ta tsaya a secondary. Domin mahaifinsu mai sauƙin ra'ayi ne, idan yarinya ta samu miji zai aurar da ita ra'ayin mijinta ne ta cigaba ko ya hana ta. Idan ba ta samu miji ba kuma ta cigaba da karatu, kuma hakan ce ta faru da Maimuna.
Tun tasowar Maimuna 'yar gayu ce mai sosai, tana son ƙwalisa. Uwa-uba tana da wayewa, don ƙawayen da take hulɗa da su duk masu buɗaɗɗan ido ne. Maimuna tun tasowarta take da tsari, don ra'ayinta ne auren namiji mai kuɗi da iya soyayya. Kuɗin ma bai cika tasiri a ranta ba matuƙar namiji zai ba ta kulawa da soyayya koda mai rufin asiri ne za ta iya zama da shi. Dalilin haka ya sa ta gama tsara rayuwar da za ta gudanar a gidan aurenta, ita da mijinta.
Tarihin Nazir
Nazir haifaffan garin Kano ne, sai dai mahaifi da mahaifiyarsa asalinsu 'yan garin Katsina ne. Neman kuɗi ne ya kawo mahaifinsa garin Kano, a nan duk aka haife su shi da ƙannensa. Mahaifinsa yana da mata biyu da 'ya'ya takwas, ƙannensa da suke uwa ɗaya guda uku ne duka maza. Sai waɗanda suke uba ɗaya su shida kasancewar shi ne babba a wurin mahaifinsa. Nazir kasuwancin hulunan maza yake a kasuwar kwari, shagonsa babba ne kuma yana da rufin asiri bakin gwargwado.
Nazir ya haɗu da Maimuna ne a wurin dinner wani abokinsa da suka yi a garin jigawa, da yake tana daga cikin manyan ƙawayen amarya. Tun da Nazir ya ganta ya maƙale mata har aka tashi daga taron, amma kafin su a watse sai da suka yi musayar lamba sannan ya kai ta har ƙofar gidansu ya sauke ta.
Ko kaɗan Nazir bai kwanta a ran Maimuna ba, don tun daga yanayinsa bai yi mata kalar irin mijin da take burin zama da shi ba. Shi kansa Nazir ya fahimci haka, don ko kiran wayarta ya yi wani lokacin ba ta ɗauka. Da ya yi bincike a kanta, sai aka yi masa bayanin halinta tsaf da yanayin waɗaanda take mu'amala da su. Hakan ne ya sa Nazir ya lulluɓe kura da fatar akuya, sai da ya tabbatar da da ya siffantu da irin mijin da Maimuna take muradi sannan ya koma mata tsamo-tsamo. Tun Maimuna tana share shi har ya fara karkato da hankalinta kansa, don tuni ya saye zuciyarta ta hanyar ƙyale-ƙyale da kayan ƙawa. Ya shiga shayar da ita romon zallar soyayya tana sharɓa, har sai da ta dinga gina musu irin rayuwar da za su gudanar a gaba. Hakan ya sa Nazir ya bijirowa Maaimuna da maganar turo magabatansa, kafin ta amince da ta suka yi yarjejeniya a kan bayan sun yi aure za ta cigaba da karatu. Don tana da burin yin aiki a gaba, tashin farko Nazir ya amince mata. Hakan ya sa aka tsayar musu da lokacin aure, da lokacin ya ƙarato Nazir ya yu mata bajimta ta hanyar kama manyan kuma ƙayatattun wuraren taro na alfarma.
Matsalar farko da Maimuna ta fara fuskata a ɓangaren ƙawayenta ne, domin ko wata ba su yi ba da aka tashi bikin wata ƙawarsu ya ce ba za ta je ba. Lamarin da ya kai su ga yin faɗa, saboda Samira aminiyar Maimuna ce ta yi mata ƙoƙari a sha'anin bikinta. Wannan faɗan har sai da ya kai su gaban iyaye, a nan kuma kowa ya ba wa Maimuna rashin gaskiya da cewar mijinta yana da damar da zai hana ta zuwa bikin kowacce ƙawa, kuma mahaifinta ya jadadda mata idan har ta kashe aurenta ba tare da wani dalili ba sai dai ta nemi wani wurin ba gidansa ba.
Wannan ikon da Nazir ya samu ya sa kai tsaye ya yanke alaƙar Maimuna da ƙawayenta, tun suna yin kara suna zuwa wurinta har kowa ya janye jikinsa saboda ba zuwa wurinsu take yi ba. Hatta garinsu sai ta shafe lokaci mai tsayi.ba ta je ba, idan sun tashi tafiya kuma shi zai kai ta ya zauna a ƙofar gida idan yamma ta yi ya ɗauko ta su dawo gida. Sannu a hankali Nazir ya dinga bijirowa Maimuna da ɓoyayyun halayensa, tun daga wani faɗa da suka yi ya karɓe babbar wayarta ya ba ta ƙarama. Sannan makarantar da suka yi yarjejeniya ya ce ba za ta cigaba da karatu ba, da ta kai ƙararsa gida kuma sai iyayenta suka nuna mata tun da aure gaba yake da komai gara ta zauna ta yi ibadar zaman aure. Da zaman aurensu ya yi zama ne Maimuna ta fahimci kuɗin da yake mata facaka da su ba su kai haka ba, don a farko kallon mai kuɗi take yi masa sai daga baya ta gane duk munfurtarta y yi. Tun daga wannan lokacin Nazir ya sire wa Maimuna, tana dai zaune da shi ne saboda biyayyar mahaifinta. Da zaman haka ya ishe ta sai ta nuna wa Nazir tana buƙatar yin kasuwanci, amma fir ya ƙi ba ta dama.
Wata irin ƙaunar Fauziya ce ta lulluɓe Kabir, yana daga tsaye ya zauna a gefenta ya haɗe ta ita da jaririyar ya rungume su cike da so da ƙauna. Ƙwace kanta Fauziya ta shiga yi, ya riƙe ta tsam sai suka saki ajiyar zuciya kusan lokaci ɗaya.
Maganarta ta maƙale sakamakon ido huɗu da suka yi da Maman Sudais, murmushin takaici ta sakar mata ta ce.
"Maimuna kenan, na ba ki yarda da aminci ashe cin dunduniyata kike? Idan kuwa ni ce yadda Annabi ya bar duniya na bar ki kenan."
Cike da borin kunya Maimuna ta ce, "To zancenki ake yi da za ki faɗa wa mutane magana? Idan kin bar ni Baban Asiya ne ya bar ni ko me? Ai dama ba zamanki nake yi ba." A ranar haka suka rabu baram-baram dutse a hannun riga, tun daga wannan ranar idan ba abin jaje ko gaisuwa ba ne babu abin da yake haɗa su da Maimuna. Gaisuwar ma sai da Abban Sudais ya takura mata da yake ta sanar da shi komai, kuma shi mutum ne mai fahimta ya ce ta kiyaye zamanta da maƙota. Don haka take takatsantsan da gabaɗayansu, tsakaninta da su sai hirar duniya ko ta yara. Kuma tun daga lokacin ta rage ba su fuska, shi ya sa yawanci suka daina shigar mata sai Maman Nana da take leƙa mata sama-sama.
Sai da Maimuna ta sayo gawayi bayan ta ɗora girki, ta sake shiga ɗaki ta ɗauko sabuwar wayarta da Jafar ya aiko mata, dama tun bayan fitar Nazir ta ciro ta haɗe da saita komai ta yi masa Salam ta whatsapp. Saboda farinciki kamar Jafad zau taka rawa haka suka ɓa ta lokaci suna musayar kalaman soyayya, domin a ranar Maimuna ba ta yi aiki gida da wuri ba. Don haka a yanzun ma da ta koma ta kira shi voice call ta whatsapp da yake ta ga yana online, yana ɗauka suka dasa daga inda suka tsaya. Daga ƙarshe ya ce ta ɗauki hotuna masu kyau ta tura masa. Wannan ne ya sanyaya mata jiki, kuma tsoro ya kamata. Har ta shiga wasu-wasin kada ta zo tsautsayi ya ratsa Maman Nana ta gani, duk da ta ji ya ce mata zai ɓoye amma haja kawai ta ji tana tsoron tura hoton. A ɓangaren ɗaya kuma ta ji kamar ba ta kyauta masa ba, domin shi ya zuba maƙudan kuɗinsa ya saya mata wayar saboda haka. Jin ta shiru ba ta tura masa ba ya sa shi kiranta a waya ya sake tunasar da ita, sai da Jafar ya yi da gaske sannan ra iya tura masa tana sake jadadda masa da ya san yadda zai yi ya adana hoton ta yadda kwaɓarsu ba za ta taɓa yin ruwa tsululu ba.
Nazir irin bauɗaɗɗun mazan nan ne, kuma yana ɗaya daga cikin mazan da ba su damu da ba wa mace haƙuri ko lallaɓa ta ba idan ta yu fushi ko idan sun yi mata laifi. Idan har Maimuna ta ga ya ɗan sakar mata fuska to a ranar yana buƙatar kusantarta ne. Abin da ya fi ci wa Maimuna tuwo a ƙwarya bai wuce rashin ba ta kulawa ba, idan Nazir ya dawo gida ba shi da abokiyar hira sai wayarsa. Koda hira Maimuna ta zauna tana yi masa sai dai ya dinga ba ta amsa sama-sama, amma kaso casa'in cikin ɗari (90%) hankalinsa yana kan wayarsa. Da yake Maimuna tana da ɗan surutu ta dinga yi masa mita kenan, tana nuna ɓacin ranta. Hakan ne ya sa wani lokacin Nazir ba ya dawowa gida da wuri, sai ya gama uzurorinsa a waje. Ya kasance mutum mai takura, bin diddigi da rashin yarda. Don hatta maƙota ba ya barin Maimuna shiga, su ma kuma a ɓoye suke shigo mata bai sani ba. Duk inda Maimuna za ta je shi zai kai ta, kuma bai cika kai ta da rana ba har sai ya dawo daga kasuwa. Kuma idan ya kai ta duk taron da ake yi sai dai ya jira ta a ƙofar gida agama ya tafi da ita. Maimuna tun tana zama ta ci kuka bayan aurensu har abin ya zame mata jiki, kuma sannu a hankali Nazir ya aurensa ya sure mata har take jin Allah Ya kawo sanadin da za su rabu wala mutuwa ko sakin aure. Sakamakon halinsu da ya yi hannun riga da ita, tun da har babbar waya ya hana ta riƙewa a cewarsa duk wani abu da zai buɗe idonta ba zai lamunra ba. Tun da ai sai mace ta yi mu'amala da mutane ake ba ta munanan shawarwari, ko a zuge ta ta sauya halaye. Idan kuwa aka ɗora mace a doron da ya ɗora Maimuna, a ganinsa hakan ne zai daidaita mace ta zama kamila tun da idonta bai buɗe ba.
Tarihin Maimuna
Maimuna 'yar asalin garin Dutse ce da ke jigawa, mahaifi da mahaifiyarta duk 'yan can ne. Kuma su biyar ne a wurin iyayensu, yayanta Sadik shi ne babba sai ita take binsa ƙannenta mata uku suke biye da ita.
Maimuna ta yi karatunta na addini daidai gwargwado, ha boko kuma ta tsaya a secondary. Domin mahaifinsu mai sauƙin ra'ayi ne, idan yarinya ta samu miji zai aurar da ita ra'ayin mijinta ne ta cigaba ko ya hana ta. Idan ba ta samu miji ba kuma ta cigaba da karatu, kuma hakan ce ta faru da Maimuna.
Tun tasowar Maimuna 'yar gayu ce mai sosai, tana son ƙwalisa. Uwa-uba tana da wayewa, don ƙawayen da take hulɗa da su duk masu buɗaɗɗan ido ne. Maimuna tun tasowarta take da tsari, don ra'ayinta ne auren namiji mai kuɗi da iya soyayya. Kuɗin ma bai cika tasiri a ranta ba matuƙar namiji zai ba ta kulawa da soyayya koda mai rufin asiri ne za ta iya zama da shi. Dalilin haka ya sa ta gama tsara rayuwar da za ta gudanar a gidan aurenta, ita da mijinta.
Tarihin Nazir
Nazir haifaffan garin Kano ne, sai dai mahaifi da mahaifiyarsa asalinsu 'yan garin Katsina ne. Neman kuɗi ne ya kawo mahaifinsa garin Kano, a nan duk aka haife su shi da ƙannensa. Mahaifinsa yana da mata biyu da 'ya'ya takwas, ƙannensa da suke uwa ɗaya guda uku ne duka maza. Sai waɗanda suke uba ɗaya su shida kasancewar shi ne babba a wurin mahaifinsa. Nazir kasuwancin hulunan maza yake a kasuwar kwari, shagonsa babba ne kuma yana da rufin asiri bakin gwargwado.
Nazir ya haɗu da Maimuna ne a wurin dinner wani abokinsa da suka yi a garin jigawa, da yake tana daga cikin manyan ƙawayen amarya. Tun da Nazir ya ganta ya maƙale mata har aka tashi daga taron, amma kafin su a watse sai da suka yi musayar lamba sannan ya kai ta har ƙofar gidansu ya sauke ta.
Ko kaɗan Nazir bai kwanta a ran Maimuna ba, don tun daga yanayinsa bai yi mata kalar irin mijin da take burin zama da shi ba. Shi kansa Nazir ya fahimci haka, don ko kiran wayarta ya yi wani lokacin ba ta ɗauka. Da ya yi bincike a kanta, sai aka yi masa bayanin halinta tsaf da yanayin waɗaanda take mu'amala da su. Hakan ne ya sa Nazir ya lulluɓe kura da fatar akuya, sai da ya tabbatar da da ya siffantu da irin mijin da Maimuna take muradi sannan ya koma mata tsamo-tsamo. Tun Maimuna tana share shi har ya fara karkato da hankalinta kansa, don tuni ya saye zuciyarta ta hanyar ƙyale-ƙyale da kayan ƙawa. Ya shiga shayar da ita romon zallar soyayya tana sharɓa, har sai da ta dinga gina musu irin rayuwar da za su gudanar a gaba. Hakan ya sa Nazir ya bijirowa Maaimuna da maganar turo magabatansa, kafin ta amince da ta suka yi yarjejeniya a kan bayan sun yi aure za ta cigaba da karatu. Don tana da burin yin aiki a gaba, tashin farko Nazir ya amince mata. Hakan ya sa aka tsayar musu da lokacin aure, da lokacin ya ƙarato Nazir ya yu mata bajimta ta hanyar kama manyan kuma ƙayatattun wuraren taro na alfarma.
Matsalar farko da Maimuna ta fara fuskata a ɓangaren ƙawayenta ne, domin ko wata ba su yi ba da aka tashi bikin wata ƙawarsu ya ce ba za ta je ba. Lamarin da ya kai su ga yin faɗa, saboda Samira aminiyar Maimuna ce ta yi mata ƙoƙari a sha'anin bikinta. Wannan faɗan har sai da ya kai su gaban iyaye, a nan kuma kowa ya ba wa Maimuna rashin gaskiya da cewar mijinta yana da damar da zai hana ta zuwa bikin kowacce ƙawa, kuma mahaifinta ya jadadda mata idan har ta kashe aurenta ba tare da wani dalili ba sai dai ta nemi wani wurin ba gidansa ba.
Wannan ikon da Nazir ya samu ya sa kai tsaye ya yanke alaƙar Maimuna da ƙawayenta, tun suna yin kara suna zuwa wurinta har kowa ya janye jikinsa saboda ba zuwa wurinsu take yi ba. Hatta garinsu sai ta shafe lokaci mai tsayi.ba ta je ba, idan sun tashi tafiya kuma shi zai kai ta ya zauna a ƙofar gida idan yamma ta yi ya ɗauko ta su dawo gida. Sannu a hankali Nazir ya dinga bijirowa Maimuna da ɓoyayyun halayensa, tun daga wani faɗa da suka yi ya karɓe babbar wayarta ya ba ta ƙarama. Sannan makarantar da suka yi yarjejeniya ya ce ba za ta cigaba da karatu ba, da ta kai ƙararsa gida kuma sai iyayenta suka nuna mata tun da aure gaba yake da komai gara ta zauna ta yi ibadar zaman aure. Da zaman aurensu ya yi zama ne Maimuna ta fahimci kuɗin da yake mata facaka da su ba su kai haka ba, don a farko kallon mai kuɗi take yi masa sai daga baya ta gane duk munfurtarta y yi. Tun daga wannan lokacin Nazir ya sire wa Maimuna, tana dai zaune da shi ne saboda biyayyar mahaifinta. Da zaman haka ya ishe ta sai ta nuna wa Nazir tana buƙatar yin kasuwanci, amma fir ya ƙi ba ta dama.
Wata irin ƙaunar Fauziya ce ta lulluɓe Kabir, yana daga tsaye ya zauna a gefenta ya haɗe ta ita da jaririyar ya rungume su cike da so da ƙauna. Ƙwace kanta Fauziya ta shiga yi, ya riƙe ta tsam sai suka saki ajiyar zuciya kusan lokaci ɗaya.