← Book details Dahuwar Ƙaho Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 81

Sashe 18

Dahuwar Ƙaho Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Wallahi na gaji Alhaji, yanzu saboda wulaƙanci na haifi 'yar a cikina. Duk wata ragamar ɗawainiyar raino da tarbiyya na yi mata, rana tsaka ka ba wa wata bare kuɗin hidimar bikinta, wallahi ba zai yuwu ba. Ai kuwa wannan karon sai dai duk abin da zai faru ya faru."

"Rashin mutumci za ki yi mini Karima?"

"Wallahi duk abin da za ka faɗa sai dai ka faɗa, amma babu ƙatuwar da za ta yi mini wannan cin kashin." Ita ma Mommy ta katse shi a zafafe, Daddy ya miƙe a fusace ya ce.

"Ba ni ne ubanta ba, wallahi idan kika saka tsiya auren ma sai na fasa shi." Cak Hajiya Karima ta tsaya, ta dube shi rai a ɓace ta ce.
"Saboda mace za ka zubarwa da kanka mutumci, to wallahi bari ka ji idan har ka yi wannan abin kunyar. Wallahi zamana da kai ya zo ƙarshe, sai dai ka zauna da Shukura ba ni ba." Daddy ya matsa gabanta ya ce.
"A yanzu ma kina iya tafiya ai ban riƙe ki ba."

"Wallahi da zaman wulaƙancin da kake yi mini gara ka sawwaƙe mini, amma wallahi ka ji na ratse ba zan yarda ace kayan ɗakina da kuɗin hidimar biki yana hannun matarka ba."
Hajiya Karima tana rufe baki Daddy ya ce.
"Karima ba ki san na jima ina haƙurin zama da ke ba ko? To tun da haka ne ki je na sake ki saki ɗaya. Idan ya so sai ki yi rayuwar jin daɗi, 'ya dai ni na haife ta. Zan ga uban da zai ɗaura mata aure." Yana gama faɗa ya fice a fusace.

Ummou Aslam Bint Adam🌚
07062062624
[17/06, 18:06] Ameera Adam: *DAHUWAR ƘAHO*

©AMEERA ADAM

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

GargaÉ—i: Ban amince a sarrafa mini littafi ta kowacce siga, ko a karanta shi a kafar sadarwa, ko É—orawa a wata manhaja ba tare da izinina ba. Yin hakan yana iya kai wa ga matakin Hukuma, don haka a kiyaye.

Tsokaci: Ƙirƙirarran labari ne bai faru a gaske ba, idan ya yi daidai da yanayin labarinki/ka arashi ne.

SHAFI NA GOMA

ALL NATURAL PRODUCT💃🏻
Tsumi
Tsumin tighten
Tsumin Sanyi
Tsumin basir
Tsumin 3in1

Kazar Amare yan mata.
Kazar Amare zawarawa.
Kazar Masu haihuwa.
Kazar 3in1
Kazar uwargida ko amarya da suke son burge oga.

Gumbar dabino.
Gumbar kwakwa.
Gumbar Madara.

Garin dahuwar kaza.
Garin dahuwar ciccibi.
Garin dahuwar hanta.
Garin dahuwar kwai.
Garin dahuwar kifi.

Garin hakin maye na sha da Madara ko nono.

Ingantaccen tsumin maganin sanyi, wanda aka samo daga masunta masu kamun kifi,bayan maganin infection yana magance sanyin da aka sha a ruwa ko a tiles ko irin sanyin nan mai kumbura jikin mutum.

Bugu da kari ana iya ba yara kanana masu fama da mura ko tari, haka akan dace idan yaro yana fitsarin kwance aka bashi in sha Allah yana dainawa.
Ta tuntuɓe mu a wannan lambar. 09065730652

***

Wani irin sanyi ƙafafuwan Mommy suka yi, kanta ta ji ya sara kamar an buga mata guduma. Da sauri ta tsugunna a ƙasa, saboda yadda ta ji juwa tana barazanar taɗe ƙafafuwanta zuwa ƙasa. Cikin ɗacin zuciya ta fashe da wani irin kuka, jin kukanta ya sa Ruƙayya ta shiga da gudu tana tambayarta. Yadda jikin mahaifiyarta yake rawa ne ya sa ta riƙe ta hankali a tashe ta ce.

"Mommy lafiya me yake faruwa?" Har lokacin ba ta daina kuka ba, don haka ita ma Ruƙayya hawayen ya fara zubo mata. Sai da Mommy ta yi kuka mai isarta sannan ta ce.

"Daddynku ne ya sake ni Ruƙayya."

Da wani irin kallo Ruƙayya ta bi mahaifiyarsu, sai kuma ta zabura kamar zararriya ta miƙe tana ja da baya.

"What are you trying to said Mommy? Don Allah kada ki maimaita mini wannan maganar, saki like how? Kina nufin Daddy ya sake ki, babu aurensa a kanki or what?"

Cikin kuka Mommy ta ce, "Haka nake nufi Mami, tun farkon aurena da mahaifinku ko yaji ban taɓa yi ba. Amma because of that yarinyar har yau ni mahaifinku ya saka, Mami har yanzu ina ganin kamar mafarki nake yi."

Ruƙayya tana shirin yin magana suka ji ƙarar taunar cingam ƙas ƙas ƙas, da sauri suka ɗago sai suka ci karo da Shukura a tsaye tana bin su da wulaƙantaccan kallo tana taunar cingma.

"Ke! Zo ki karɓi takardar sakin uwarki ki kai mata, sai ku yi hanzarin tattare kayanku ku bar gidan nan. Don ba zan iya ganin wannan abar tana giftawa a gaban mijina ba, kin san zuciya ba ta da ƙashi. Kada shaiɗan ya gifta su fara wani irin zama da ita." Shukura ta furta cikin isa da izgilanci. Ran Mommy sake ɓaci ya yi, za ta yi magana Ruƙayya ta ƙarasa zuciyarta tana zafi. Cike da tsanar Shukura ta karɓi takardar ta fara kantawa. Babu ko tantama rubutun mahaifinsu ta gani, sai dai a wannan lokacin ta fi ganin laifin Daddy fiye da na Shukura, saboda da bai ba ta ba; ba za ta samu ƙwarin gwiwar zuwa wurinsu tana rashin mutumci ba. Shukura ta sake yamutsa fuska ta ce.

"Yawwa, a gaggauta fita tun da ba gidan..."

Marin da Ruƙayya ta zabga mata ne ya katse kalaman da take yi, cikin jin azaba ta dafe kumatunta. Kafin ta ɗago Ruƙayya ta sake ɗauke fuskarta da mari har sai da kanta ya bugu da bango. A razane Shukura ta ja da baya, ta saka hannuwa biyu ta dafe kumatunta cikin tsoro ta ce.
"Ni kika mara Mami?"

Cikin zafin zuciya Ruƙayya ta sake yin kanta gadan-gadan ta ce, "Na mare ki, wallahi idan kika sake furta kalma mara daɗi a kan mahaifiyata sai na yi ƙasa-ƙasa da ke. Annoba makira, In Shaa Allahu da sannu za ki girbi abin da kika shuka."

Shukura ta sauke hannunta, ta nuna Ruƙayya da yatsa ta ce.
"Wallahi za ki san kin kai hannunki saman kumatuna, na rantse da Allah sai na rama a kan wannan tsohuwar kilakin." Tana ganin Ruƙayya ta yo kanta, ta fita da gudu haɗe da fashewa da kuka. Lokacin da Shukura ta fita harabar gidan, Alhaji Umar ya shiga mota kenan zai fita. Tana zuwa jikin motar ta sake rushewa da kuka tana riƙe cikinta, da sauri Daddy ya fito jikinsa har rawa yake yi ya ce.

"Me ya faru Shukura? Mene ne ya samu cikin naki?"

Durƙushewa Shukura ta yi cikin kuka ta ce. "Kawai daga kai wa Hajiya takarda, shi kenan ita da Mami suka rufe ni da duka. Hajiya har tana dukan cikina, wai gara na rasa cikin kowa ya huta. Ni gaskiya ba zan cigaba da zaman gidan nan ba, wallahi ko dai su fice su bar ni ko kuma ni na fita bar su, don wallahi ba zan zauna su kashe ni ba."

Cikin kumfar baki Daddy ya ce.
"Ita Hajiyan saboda ba ta da hankali ta dake ki a ciki? Wato saboda na sake ta sai ita da Mami su huce a kanki ko? Bari na shiga gidan." Yana gama faɗar haka ya shige da sauri, har babbar rigarsa tana shirin kayar da shi. Shukura miƙewa ta yi tana sakin murmushin ƙeta, sannan ta rifa masa baya. Maigadi shiru ya yi cike da jimami, don duk da 'yan gidan ba shiga huruminsa suke yi ba amma ya fahimci zuwan Shukura bai kawo komai a gidan ba sai sharri.

Lokacin da Shukura ta fita da faɗa Mommy ta tari Ruƙayya tana faɗin, "Ruƙayya kanki ɗaya kuwa? Kin san me kika aikata? So kike ki janyo wa kanki masifa kina zaune ƙalau?" Hawaye yana zuba daga idonta ta ce.
"Mommy ba ki ji abin da take faÉ—a ba? Duk wannan maganganun sai na yi mata shiru, yanzu saboda Allah ban da Daddy ya ba ta fuska ta isa ta faÉ—a miki haka?"

"Tun da mahaifiyarku ta ɗaure muku ai dole ku yi rashin mutumcin da kuka ga dama." Daddy ya furta a zafafe, cikin sauri Ruƙayya ta waiga ta ce.
"Daddy ka ga..."

Tas! Daddy ya ɗauke fuskarta da mari, kafin Ruƙayya ta yi motsi ya sake sauke mata wani. Rai a ɓace ya ce.
"Don ba ki da mutumci matar tawa uwarki za ta saka ki daka? Ni za ku wulaƙanta saboda rashin tarbiyya."

"Ai ba ita ba ce har da Hajiyan, kuma wallahi sai ka rama mini ko ni na rama." Shukura ta faɗa a shagwaɓe. Daga Mommy har Ruƙayya ɗagowa suka yi suna kallon Shukura, ta fakaici idon Daddy ta sakar musu gwalo sai kuma ta sake fashewa da kuka.

"Ni ba zan rama miki ba, sai dai ki rama da kanki."
Daddy ya faɗa yana matsawa gefe. Babu ko kunya Shukura ta matso da niyyar yi wa Mommy mari a fuska. Ruƙayya ce ta sha gaban Mommy, fuska a haɗe tana wurgawa Shukura mugun kallo.

"Za ki matsa ta rama marin da uwarki ta yi mata ko sai ranki ya ɓaci?" Daddy ya buga wa Mami tsawa. Zuciya a ƙeƙashe ta ce.
"Duk wani hukunci da za ta yi ta sauke shi a kaina, amma idan ta sake ta É—ora hannu a jikin mahaifiyata wallahi za ta gane kurenta." Cikin zafin zuciya Daddy ya sake marin Ruayya ya ce.
"Haka Karima ta gurɓata tarbiyyarku ban sani ba? Ba za ki matsa ba sai na sumar da ke."

"Ko za ka kashe ni Daddy ba zan bari wannan matsiyarciyar ta mari mahaifiyata ba." Ruƙayya ta faɗa zuciyarta a dake, don a yadda take ji a ranta komai za ta iya aikatawa a kan mahaifiyarta. Tana nan tsaye Daddy ya rufe ta da duka, amma taurin kai irin na Ruƙayya ya sa ta ƙi motsawa daga wurin. Kuka Mommy ta saka, ta janye Ruƙayya ta ce.
"Ba sai ka illata mini yarinya ba, za mu tattara mu bar maka gidanka." Fisge Ruƙayya Daddy ya yi, a zuciye ya dubi Mommy kamar zai kai mata duka ya ce.

"Kada ki sake shiga tsakanina da 'yata idan ina hukuntata. Idan ba haka ba wallahi ranki zai yi mummunan ɓaci." A daidai lokacin Haidar ya shiga, jin abin da ake tattaunawa ya sa ransa ɓaci. Shukura ta sake fasa wani sabon kukan ta ce.
Chapter 18 · 0% Book details