Sashe 69
Alkibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Hajja batasan da zaman cikin ba,sai sanda ya samu hutu na sati guda,yace su shirya suje kanon su roqi hajja tabar musu baba gaje,a lokacin cikin nata ya shiga wata na uku,kuma ga duk mutum mai saurin tsinkaye da daukar haske zai fahimci akwai ciki tare da zahran,tayi wani kyau,hakanan ta sake cika,fatarta ta qara haske,sau tari haidar kan sanyata gaba da tsokana,ya hanata sakat,bini bini yana shafa fatarta,idan tayi qorafi sai yace
"Ke dince ki qara wani kyau,fatarki kamar atafa,karfa nan gaba na soma kasa gane hanyar fita daga gida,ko naje nayi shirme gaban manya ki jawomin hukunci" saita tureshi tana tura baki,sabida ita gani take kamar tsokanarta yake,don rannan daya goyata ya zagaya da ita cewa yayi ta sauka,ta fara ninka nauyinta,sai data dinga masa kukan wasa sannan kuma ya lalace wajen lallashi da bata haquri,ire iren yanayin rayuwarsu kenan,idan ka ganshi a cikin gida saika rantse da Allah ba ALIYYU MAS'UD DABO bane,sojan nan daya kasance dodon 'yan ta'adda da marasa gaskiya dake cikin qasar nan,idan ka ganshi a waje sanye da kaki ba zaka ce zaka sameshi a haka cikin gida ba.
*_BAYAN WATA TARA_*
Tsaye suke cikin dakin hajja,taja rungume cikin jikinsa saidai ya rungumeta ne ta bayanta saboda tsinin cikinta wanda ya dora dukka hannayensa biyu akai,yana jin yadda yaron cikinta ke motsawa,kai kace zai fasa cikin ne ya fito,bai dauke hannun ba har sai daya tsagaita da motsin,suka saki ajiyar zuciya shida ita a tare,sannan ya juyo da ita suna fuskantar juna.
Tausayinya yakeji fiye da kima,koda can shi mutum ne mai tsananin tausayin mace,macen ma ace mai juna biyu,yau saiga abuj cikin gidansa,a jikin mace mafi soyuwa duk duniya a wajensa baya ga iyayensa
"Banda hajja ce hubby duk duniya babu wanda ya isa ya sanyani na wani kawoki wankan gida" murmushi ta saki,ta sanya hannunta tana shafan kwantaccen gashin fuskarsa da ko yaushe yake qara masa kyau da kwarjini
"Kasan dai hajja ta fimu damuwa da kwanunanmu....sannan tun ban dade da shiga third trimester dina ba tace ka dawo dani gida,yanzu idan baka kawoni ba zataga cewa kamar bata isa damu bane,bayan ina da tabbacin cewa tayi hakanne saboda amfanin kanmu" fuskarta ya riqe tsakiyar hannunsa,ya matso da ita dab da tashi,cikin softness yace
"Hubby....inason in zama mutum na farko da zaya dauki 'yarshi" yatsanta ta dora saman lips dinsa tana cewa
"Shshshs.....point of correction.....soja nakeso na haifa,jarumi kamar kai....mai kuma kama dakai" dagowa yayi yana murmushi,ya kama hannayenta duka ya riqe cikin hannunsa
"Little zahra ni kuma nakeso.....kuma inaji a jikina itace"
"Ok....ok,ba anyi yarjejeniya ba akan a bari har sai ranan?,duk wanda yayi wining zai zaba abinda yakeso mutum ya bashi..."
"Yes hubby" ya fada yana lakace hancinta,saita jefa masa harara
"Ka takurawa hancin nan nawa" dariya sosai ya saki yana cewa
"Ya qara kyau ne,kamar na dauke kayana na tafi dashi" tasan cewa girma ya qara fiye dana da,amma ba zai taba fitowa ya gaya mata hakan ba,saidai kullum idan ya dameshi da cewa hancinta yayi qato ko yayi muni sai yace mata suyi musanye da nata,ko ta bashi kayanshi yana so shi a haka.
Rigima ta soma yi masa kan ta gane dariya yake mata saboda tayi muni,lallashin duniya taqi shuru saboda bai daina dariyar badai,har sai da hajja tazo ta tankada qeyarsa sannan aka samu salama.
Tana zama saqonsa yana shigowa wayar tata
_zan qara kwana daya ko Allah zaisa ina da rabon ganin baby na,but please kada ki sanarwa kowa_
Idanu ta zaro cike da mamakinsa,muhimmin taro suke dashi da mr president a jibi amma yace bazai tafi ba,saita koma daki ta kirashi tana son tayi convincing dinsa kan ya tafi saboda muhimmancin taron amma fur yaqi,dole ta rabu dashi,ya daddogara ta dawo falo saboda ciwon mara da baya da yaketa tsunkulinta.
A falon tayi kwanciyarta suna hira da hajja,jifa jifa tana cije lebe idan aka mintsineta,saita dinga mamaki,don bata taba ciwon mara haka mai naci ba kamar nayau,ana mintsinarta amma da tayi daya biyu uku a rana shikenan sai washegari,amma nayau din yaqi barinta batasan dalili ba.
Ciwon bayan da taji yana yawa saita koma daki da niyyar kwanciya ko zai ragu,saidai tana shiga kamar an dado ciwon ne,tayi tayi ta zauna ta kasa qafarta ta riqe gam,dole ta dinga qwalawa hajja kira,sai gata bagatatan ba shiri.
Tuni ta fahimci haihuwa ce,ta aika umaima ta kira mata mamarta matar abban tsakiya,ta sanya ilham kuma ta shiga tsohon dakin zahran ta dauko kayan da aka ware don tafiya asibiti.
Kafin ilham ta dauko kayan maman umaima ta qaraso ciwon ya ta'azzaran mata,ta kasa tafiya bare akai ga batun zuwa asibiti,don haka hajja tace adan dakata ko zai lafa mata sai a tafin,saidai ina,gaba kawai ciwon yakeyi,wanda harta kasa jure masa tana neman taimako,baba gaje da kuma hajjan su suka riqeta lokacin da suka fahimci haihuwar tazo gadan gadan,cikin ikon Allah da taimakon addu'a cikin mintunan da basu wuce uku ba kukan jariri ya karade sassan hajjan gaba daya.
Kusan tare suka saki ajiyar zuciya ita da hajjan,farinciki mara misaltuwa ya sauka a zukatansu gaba daya,hajjan ce da kanta,duk da tsufa ta dauke yaron daketa watsal watsal cikin qazantar da suka fito tare yana canyara kuka,ta kasa daurewa saidata rungumeshi cikin jikinta qwalla na gangarowa daga idanunta
"Alhamdulillah....alhamdulillah" shine kawai abinda yake fita daga bakinta,sannan ta qarasa dab da zahran ta dora mata yaron saman cikinta tana shafa sumar kanta
"Sannu takwarata,sannu da qoqari,barka da arziqi" saita lumshe idanunta cikin matuqar jin kunya,gefe guda na zuciyarta farinciki na mamayeta,idanunta kan fuskar yaron,fuskar da ko ba'a wanketa ba ta bayyana kamar ya Aliyyunta daya dauko,sak shi,kamar kaki yayi ya aje,take wata qauna irin wadda ubangiji S W T yake dasawa a zukatan bayinsa tsakanin uwa da 蓷a ta fara kwaranya a zuciyarta.
Kafin kace meye wannan labarin haihuwar ya zaga gidan,tuni aka soma gyaran zahran da jaririnta,cikin qasa da awa guda tayi wankanta da ruwan dumi,an goge yaron da kyau,an gyara mata dakin hajjan yadda zai dace da yanayin jaririn,hajjan tasa an dora mata kunu bayan ta soma da bata tea mai uban kauri da bournvita saboda ruwan nono.
Sau wajen biyar yana attempting bude gidan nasa ya shiga sai yaja tsaki ya fasa,yayi imanin koda ya shiga baqiqqirin gidan zai masa,bazai ma iya zama ba,saboda babu fitilar gidan,daga qarshe kamar wanda ake umarta,yaji kawai zuciyarsa ta yanke masa ya koma gidan hajjan ya wuni da zahran,idan yaso idan dare yayi ma ya bude tsohon dakinsa na gidan yayi kwanciyarsa,duk da babu komai yanzun a dakin sai katifa,ya tabbatar sai yafi samun relief akan ya kasance tana nesa dashi.
Tunda ya doso gidan yaji gabansa yana faduwa,sanda shamsu ya bude masa qofar gidan ya ga kamar yanason magana dashi,amma bai tsaya ba sai daya isa inda suke aje motocinsu,yana kashe motar kuma yayi sassan hajjan.
Sanda ya shigo yayi dai dai da lokacin da jaririn ke kukan neman nono,baba gaje na kan zahran tana gwada mata yadda ake feeding yaro,tana ta dariyar rashin sabo irin na zahra
"Saiko kin dage,don na fuskanci me gidan nawa acici ne".
Tuntube ya kusa ci da filallukan falon hajjan saboda yadda zuciyarsa ta bashi amsar zahransa ce ta haihu yana qaryatata,banda ingarma ne kuma tsayayye da faduwa zaiyi qasa warwas,ko takan hajjan dake masa magana baibi ba yayi inda yaji kukan na fitowa wato dakin gadon hajjan.
Kyakkyawan gani kuwa idanunsa suka masa,zahransa rungume da kyakkyawan baby cikin jikinta tana shayar dashi,idanunta a runtse da alama ta jin zafin yadda yake tsotso ne,tashi guda tayi wani mugun kyau,fatarta kamar an qara mata sinadaran kyau,baisan ya isa garesu ba saida yaji muryar baba gaje dake fita tana cewa
"A barshi yasha sosai kafin a cireshi,ruwan maman sai yafi saurin zuwa,idan kin gama saiki magana zaku asibiti su sake tabbatar da lafiyarki"
"Ke dince ki qara wani kyau,fatarki kamar atafa,karfa nan gaba na soma kasa gane hanyar fita daga gida,ko naje nayi shirme gaban manya ki jawomin hukunci" saita tureshi tana tura baki,sabida ita gani take kamar tsokanarta yake,don rannan daya goyata ya zagaya da ita cewa yayi ta sauka,ta fara ninka nauyinta,sai data dinga masa kukan wasa sannan kuma ya lalace wajen lallashi da bata haquri,ire iren yanayin rayuwarsu kenan,idan ka ganshi a cikin gida saika rantse da Allah ba ALIYYU MAS'UD DABO bane,sojan nan daya kasance dodon 'yan ta'adda da marasa gaskiya dake cikin qasar nan,idan ka ganshi a waje sanye da kaki ba zaka ce zaka sameshi a haka cikin gida ba.
*_BAYAN WATA TARA_*
Tsaye suke cikin dakin hajja,taja rungume cikin jikinsa saidai ya rungumeta ne ta bayanta saboda tsinin cikinta wanda ya dora dukka hannayensa biyu akai,yana jin yadda yaron cikinta ke motsawa,kai kace zai fasa cikin ne ya fito,bai dauke hannun ba har sai daya tsagaita da motsin,suka saki ajiyar zuciya shida ita a tare,sannan ya juyo da ita suna fuskantar juna.
Tausayinya yakeji fiye da kima,koda can shi mutum ne mai tsananin tausayin mace,macen ma ace mai juna biyu,yau saiga abuj cikin gidansa,a jikin mace mafi soyuwa duk duniya a wajensa baya ga iyayensa
"Banda hajja ce hubby duk duniya babu wanda ya isa ya sanyani na wani kawoki wankan gida" murmushi ta saki,ta sanya hannunta tana shafan kwantaccen gashin fuskarsa da ko yaushe yake qara masa kyau da kwarjini
"Kasan dai hajja ta fimu damuwa da kwanunanmu....sannan tun ban dade da shiga third trimester dina ba tace ka dawo dani gida,yanzu idan baka kawoni ba zataga cewa kamar bata isa damu bane,bayan ina da tabbacin cewa tayi hakanne saboda amfanin kanmu" fuskarta ya riqe tsakiyar hannunsa,ya matso da ita dab da tashi,cikin softness yace
"Hubby....inason in zama mutum na farko da zaya dauki 'yarshi" yatsanta ta dora saman lips dinsa tana cewa
"Shshshs.....point of correction.....soja nakeso na haifa,jarumi kamar kai....mai kuma kama dakai" dagowa yayi yana murmushi,ya kama hannayenta duka ya riqe cikin hannunsa
"Little zahra ni kuma nakeso.....kuma inaji a jikina itace"
"Ok....ok,ba anyi yarjejeniya ba akan a bari har sai ranan?,duk wanda yayi wining zai zaba abinda yakeso mutum ya bashi..."
"Yes hubby" ya fada yana lakace hancinta,saita jefa masa harara
"Ka takurawa hancin nan nawa" dariya sosai ya saki yana cewa
"Ya qara kyau ne,kamar na dauke kayana na tafi dashi" tasan cewa girma ya qara fiye dana da,amma ba zai taba fitowa ya gaya mata hakan ba,saidai kullum idan ya dameshi da cewa hancinta yayi qato ko yayi muni sai yace mata suyi musanye da nata,ko ta bashi kayanshi yana so shi a haka.
Rigima ta soma yi masa kan ta gane dariya yake mata saboda tayi muni,lallashin duniya taqi shuru saboda bai daina dariyar badai,har sai da hajja tazo ta tankada qeyarsa sannan aka samu salama.
Tana zama saqonsa yana shigowa wayar tata
_zan qara kwana daya ko Allah zaisa ina da rabon ganin baby na,but please kada ki sanarwa kowa_
Idanu ta zaro cike da mamakinsa,muhimmin taro suke dashi da mr president a jibi amma yace bazai tafi ba,saita koma daki ta kirashi tana son tayi convincing dinsa kan ya tafi saboda muhimmancin taron amma fur yaqi,dole ta rabu dashi,ya daddogara ta dawo falo saboda ciwon mara da baya da yaketa tsunkulinta.
A falon tayi kwanciyarta suna hira da hajja,jifa jifa tana cije lebe idan aka mintsineta,saita dinga mamaki,don bata taba ciwon mara haka mai naci ba kamar nayau,ana mintsinarta amma da tayi daya biyu uku a rana shikenan sai washegari,amma nayau din yaqi barinta batasan dalili ba.
Ciwon bayan da taji yana yawa saita koma daki da niyyar kwanciya ko zai ragu,saidai tana shiga kamar an dado ciwon ne,tayi tayi ta zauna ta kasa qafarta ta riqe gam,dole ta dinga qwalawa hajja kira,sai gata bagatatan ba shiri.
Tuni ta fahimci haihuwa ce,ta aika umaima ta kira mata mamarta matar abban tsakiya,ta sanya ilham kuma ta shiga tsohon dakin zahran ta dauko kayan da aka ware don tafiya asibiti.
Kafin ilham ta dauko kayan maman umaima ta qaraso ciwon ya ta'azzaran mata,ta kasa tafiya bare akai ga batun zuwa asibiti,don haka hajja tace adan dakata ko zai lafa mata sai a tafin,saidai ina,gaba kawai ciwon yakeyi,wanda harta kasa jure masa tana neman taimako,baba gaje da kuma hajjan su suka riqeta lokacin da suka fahimci haihuwar tazo gadan gadan,cikin ikon Allah da taimakon addu'a cikin mintunan da basu wuce uku ba kukan jariri ya karade sassan hajjan gaba daya.
Kusan tare suka saki ajiyar zuciya ita da hajjan,farinciki mara misaltuwa ya sauka a zukatansu gaba daya,hajjan ce da kanta,duk da tsufa ta dauke yaron daketa watsal watsal cikin qazantar da suka fito tare yana canyara kuka,ta kasa daurewa saidata rungumeshi cikin jikinta qwalla na gangarowa daga idanunta
"Alhamdulillah....alhamdulillah" shine kawai abinda yake fita daga bakinta,sannan ta qarasa dab da zahran ta dora mata yaron saman cikinta tana shafa sumar kanta
"Sannu takwarata,sannu da qoqari,barka da arziqi" saita lumshe idanunta cikin matuqar jin kunya,gefe guda na zuciyarta farinciki na mamayeta,idanunta kan fuskar yaron,fuskar da ko ba'a wanketa ba ta bayyana kamar ya Aliyyunta daya dauko,sak shi,kamar kaki yayi ya aje,take wata qauna irin wadda ubangiji S W T yake dasawa a zukatan bayinsa tsakanin uwa da 蓷a ta fara kwaranya a zuciyarta.
Kafin kace meye wannan labarin haihuwar ya zaga gidan,tuni aka soma gyaran zahran da jaririnta,cikin qasa da awa guda tayi wankanta da ruwan dumi,an goge yaron da kyau,an gyara mata dakin hajjan yadda zai dace da yanayin jaririn,hajjan tasa an dora mata kunu bayan ta soma da bata tea mai uban kauri da bournvita saboda ruwan nono.
Sau wajen biyar yana attempting bude gidan nasa ya shiga sai yaja tsaki ya fasa,yayi imanin koda ya shiga baqiqqirin gidan zai masa,bazai ma iya zama ba,saboda babu fitilar gidan,daga qarshe kamar wanda ake umarta,yaji kawai zuciyarsa ta yanke masa ya koma gidan hajjan ya wuni da zahran,idan yaso idan dare yayi ma ya bude tsohon dakinsa na gidan yayi kwanciyarsa,duk da babu komai yanzun a dakin sai katifa,ya tabbatar sai yafi samun relief akan ya kasance tana nesa dashi.
Tunda ya doso gidan yaji gabansa yana faduwa,sanda shamsu ya bude masa qofar gidan ya ga kamar yanason magana dashi,amma bai tsaya ba sai daya isa inda suke aje motocinsu,yana kashe motar kuma yayi sassan hajjan.
Sanda ya shigo yayi dai dai da lokacin da jaririn ke kukan neman nono,baba gaje na kan zahran tana gwada mata yadda ake feeding yaro,tana ta dariyar rashin sabo irin na zahra
"Saiko kin dage,don na fuskanci me gidan nawa acici ne".
Tuntube ya kusa ci da filallukan falon hajjan saboda yadda zuciyarsa ta bashi amsar zahransa ce ta haihu yana qaryatata,banda ingarma ne kuma tsayayye da faduwa zaiyi qasa warwas,ko takan hajjan dake masa magana baibi ba yayi inda yaji kukan na fitowa wato dakin gadon hajjan.
Kyakkyawan gani kuwa idanunsa suka masa,zahransa rungume da kyakkyawan baby cikin jikinta tana shayar dashi,idanunta a runtse da alama ta jin zafin yadda yake tsotso ne,tashi guda tayi wani mugun kyau,fatarta kamar an qara mata sinadaran kyau,baisan ya isa garesu ba saida yaji muryar baba gaje dake fita tana cewa
"A barshi yasha sosai kafin a cireshi,ruwan maman sai yafi saurin zuwa,idan kin gama saiki magana zaku asibiti su sake tabbatar da lafiyarki"