Sashe 68
Alkibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kamar yadda ya fada din kuwa tare suka tsara komai,kamar yadda yake kama mata aikin gida haka yake tayata karatun jarrabawar,bata taba tunanin haidar din gifted bane,mai matuqar ganewa tarin basira da kuma dabarun koyar da karatu,bata taba marmarin karatu ba,bata taba jin karatun jarrabawa me dadi ba,wanda babu ginsa ko qasawa a ciki ba sai wannan karon,yasan tarin abubuwa game da abinda ta karanta din,idan tace ta gaji yasan yadda zai mata ta samu relief su dora daga inda suka tsaya,su huta suyi bacci su tashi suci gaba,yace so yake ta fita da sakamako mai kyau wanda zata bar tarihin cikin makarantar,kamar yadda shima yabar tarihi cikin tashi makarantar daya gama.
*_BAYAN WASU KWANAKI_*
Yana tsaye daga saman dining yana hada musu tea shi da ita a cup biyu,yanayi yana duba agogo,a shirye yake tsaf cikin wata dakakkiyar shadda sabuwa fil ruwan zuma,wanda saida aka sha daru shida zahran tashi kafin ya yarda ya sanyata,shiri ne na tafiyarsu jarabawa a rana ta farko,ya sake daga kansa yana duban hanya,sai gata ta fito dauke da plate a hannunta,sanye take da wani lafiyayyen lace itama ruwan zuma,dinkin riga da plain zani,sabida yace bai yarda ta saka skert ba.
Duban fuskarta yake sosai,tana tahowa inda yake din tana yatsina fuska
"Yau wani laziness kikeji hubby,kodai exam dince tun kafin a fara take bugunki?,karki fa damu,ina da zato mai qarfi a kanki,kisa a ranki an gamata kawai" ajjiye plate din tayi a gabansa,ta hade hannayenta waje guda 馃檹馃徑
"Bani da haufi tsoro ko shakka indai sojana yana kusa....mutumin dake iya kula da qasarsa ma bare ni mutum daya?,....na yadda da kaifin basirarsa,hakanan inda malami ne shi xaiyi wuya a sami malami kamarsa kaf qarninsa kuwa,koda bayan mutuwarsa ne da shekara dari" wani kallo ya kafeta dashi,yana jin kamar ya hadiyeta,gwana ce wajen iya tsara kalaman da zasu tafi da hankalin dukkan mai hankali,ya rasa amsar da zai bata illa tukuicin lallausan murmushinsa,wanda ya jima yana shaida mata ya tanadeshi ne kawai saboda ita,ta kuma yarda da hakan dari bisa dari,don takanyi mamakin yadda yake komawa zakin gaske a gaban duk wata mace koma bayanta,hatta da qannensa shakkar nan tasa tana cikin zukatansu
"Kawai dai qwan nan ne,tunda na fara soyashi zuciyata ke tashi...." Ta amsa mishi tambayarsa ta farko sanda take daukar cup din tea din daya miqa mata,idanu ya kuma zura mata yana karantarta sanda take kurbar tea din,har sai data lura,saita dage masa girarta dukka biyun,alamun tambayar lafiya?
"Anya ko hubby....anya ban jefa qwallona a raga ba?" Ido ta fiddo tana aje cup din
"Bana tunanin haka.....haba watanmu nawa sojana....kawai ko a gida banson qarnin qwai,kuma ko xanci ma saina yanka wadatacciyar albasa akai nake ci" kafadunsa ya dage yana bude plate din chips da qwan data aje masa
"Ohkey....amma ko chips din ai kyaci ko?" Fuska ta kyabe cike da shagwaba tana maqale kafada
"Nifa qamshinsu ya gama cikamin ciki.....saidai ka taimaka ka siyamin meatpie a wannan gurinnnnn" dariya taso bashi,tunda ya taba siya mata meatpie din ta maqale masa,saiya maqale kafada shima
"Naqi wayon,saidai idan kin yarda nima....." Qarshen zancan ya furta mata qasa qasa,sarai ta gane abinda yake fada,saita sakar masa kukan shagwaba,ta dauke hand bag dinta dake gabansa ta sauko daga dining din tana diddira qafa,dariya sosai yakeyi shima,ya aje abincin ya biyo bayanta.
Har suka je suka dawo yana tattalinta,suna gama exam din ta zagaya inda ya zauna zaman jiranta ta sameshi,bata yarda kowa ya biyota ba,ya gama ganeta amma tana togewa,kishinsa take hakan ya sanya bata hada kowa dashi.
Da taimakon Allah da kuma agazawar haidar din ta kammala jarrabawar cikin babbar nasara,babu qunci ko takura ko wahala mai yawa,wanda dalibi ke tsintar kansa a duk yayin jarrabawa,wanda tasan cewa sirrin hakan na tattare ne da dafawar haidar din.
Ta yadda da cewa samun masoyin gaskiya babban dace ne a rayuwa,hakanan rashin sa'a a soyayya kada ya sanya mace ta yanke tsammani da samun haske kuma mabudin yayewar dukkan matsalarta,abu daya ake buqata shine,ki sake hankalta a yayin da duk wata qaddara ta sameki ko kika aikata kuskure,kiyi qoqarin zama me kamewa,ki ninki zurfin dora abubuwanki saman sikeli da mizani fiye da ko yaushe,sannan ki zafafa da addu'a,babu ji babu gani,babu daga qafa babu hutu.
Imani da qaddararta da tayi,ta karbeta hannu bibbiyu,ta kuma tsarkake zuciyarta,ta riqe mutuncinta da mutuncin gidansu,ta kuma yi biyayya ga magabatanta shi yasa Allah ya dubeta yayi mata musaya mafi alkhairi,ba shakka yaudara nada zafi da ciwo,tana da qarfin da zatayi barazana ga rayuwar wanda aka yiwa ita,saidai kuma girman ubangiji ya shafe komai,qudirarsa da alkhairinsa kan bayinsa yawa ne dashi,koda yaushe ko godewa ubangiji bisa kowacce irin nau'in qaddarar daya tsagawa rayuwarka,tayi maka dadi ko bata yi maka ba,wannan shike nuni da cikar imanin bawa.
Randa sukayi paper din qarshe ta dinga jin jikinta sama sama,haka dai ta daure akayi sallama da qawaye da abokan karatu,ko cikin mota ma cikin seat ta lafewa haidar din,daya tambaya tace babu komai gajiya ce,bai gasgatata ba amma ya qyaleta,saboda ya lura kaman batason magana ne,zatonsa bai tabbata ba sai da suka bude falo zasu shiga,saita tafi luu zata fadi ya tarota,ya qarasar da ita saman kujera yana mata sannu,gaba daya ya rude cikin qanqanin lokaci,ruwa ya bata mai sanyi tasha,sai numfashinta ya koma normal
"Sannu"
"Lafiyata qalau" tayi qarfin halin fada,saboda zallar damuwar data hanga tattare dashi
"No hubby....baki da lafiya" don kada tayi masa musu kota bata masa lokacima yasa bai tsaya sauraren kalaman bakinta ba ya dauketa cak sai bandaki,ya ajjiyeta sannan ya tara mata ruwan wanka
"Ki wanka na baki minti goma,zan shirya na kaiki kiga likita" saiya fiddo mata towel soson wanka da sabulun wankan ya aje mata,sannan yaja mata qofar ya rufe,saiya wuce daya bandakin shima.
Idanu ya zuba mata sanda ta gama shirin ta fito,saiya riqe hannunta sosai
"Duk yadda kika kai ga boyemin baki da lafiya hubby bazai boyu ba,kin manta ne,ni dake ruhi daya ne yake rayuwa a gangar jiki guda biyu?" Murmushi ta sakar masa,saiya karata da jikinsa suna takawa a hankali yana sake gaya mata wasu kalaman da suka sanyata sakin ajiyar zuciya a jejjere.
A qalla ya kusa minti talatin zaune shida ita cikin motar riqe da hannayenta yana jero mata kalaman nuna zallar qauna da godiya a gareta,tun lokacin da likitan ya shaida masa tana dauke da juna biyu gaba daya yayi wani irin rudewa,ko a yanzun ma hawaye zahran ke futarwa,saboda kalaman da yake amfani dasu a kanta sun girmi kanta,kalamaine da take da cikakken yaqinin ba kowacce mace bace Allah yake mata baiwa da samun mijin da zai furta mata su ba
"Gobe as early as possible zamu wuce abuja...thank god kin gama abinda ya zaunar damu,kinji kuma yace kin da buqatar cikakken hutu,so zan buqaci hajja kawai ta bamu baba gaje mu wuce da ita....but...banda fadar dalili,don i sure tsaf hajja zata hanani tafiya dake" dariya sosai ya bata data tuna da hajjansu,hajiya hajja,ayi tsiya ayi dadi,tana sonsu tana tattalinsu,amma idan tsiyarta ta tashi har su saita dandana musu.
Kamar yadda ya tsara kuwa tun a daren ya gama hada musu abinda yasan suna da buqata,ba wasu kaya bane masu yawa,tunda komai a kwai a can,ya kira hajja yace baba gaje ta shirya gobe zata rakasu abuja,ta fara masa tambayoyi yace ta bari idan yazo gobe zasuyi magana,ranar kusan kwanan zaune yayi,rabi bacci rabi idanunsa biyu,duk sadda ya farka saiya tuna cewa wai shima ya kusa zama uba?.
Qarfe bakwai a gidan tayi musu
"Wai tafiya abujan na meye haka saikun daukemin gaje kuma?" Zahra ce ta marairaice fuska
"Haba hajja,can dinfa babu dadi wallahi xaman shuru" waiwayawa tayi ta dubeta
"To ba sai ya barki nan ba,ya dinga zuwa?" Baki zahra ta tura
"Habba hajja...a'ah wallahi,ni mijina zanbi"
"Na shiga uku ni fatsima.....yau naga abinda yafi xare tsayi.....innawuro ni kike gayawa haka kanki tsaye." Ilham da husna me zasuyi in banda dariya,baba gaje dake tsaye a gefe tana tayasu,shikam haidar dama bai shigo ba yana wajensu abba babba suna gaisawa,daga can ya tsaya wajen ummi don bincika me dame take da buqata,duk da bata rasa komai,amma bakan baisa ya daina hidima gareta ba,kwata kwacin yadda zaiyima gidansu.
Yana shigowa kuwa tace
"Kama hannun matarka ku ficemin,Allah ya kiyaye hanya,nikam yanzu kunfi qarfina,Allah rabamu qalau" yasan wata tsiyar aka tufka sai baice komai ba banda dariya da yake dannewa,amma ya godewa Allah da hajjan bata harbo jirginsu ba,haka suka fice bayan sunwa kowa sallama.
Shida ita a baya suka zauna,don bazai iya juriyar awanni suna waje daya amma ba ita a gefansa ba,baba gaje da driver suna gidan gaba,hakan ya baiwa zahra damar kwanciya sosai bisa jikinsa,don sam bata jin qwarin jikinta,shi kuma ya tattarota cikin jikin nasa sosai,ya gyara mata yadda zata fi jin dadin kwanciyar.
Tun basuyi nisa ba kiran hajja ya shigo wayarshi
"Anya lafiya zahra'u kuwa take?,ni sai da kuka wuce naga yanayinta baiyimin ba" cikin dakiyar nan tasa yace
"Lafiya take hajja....wani abu ya faru ne?"
"Um um....amma kawai sai nakega kamar me yaron ciki....koma meye ne ka kula da ita da kyau,sannan idan akwai wani abu da baku gane mishi ba kayi hanzarin dawomin da ita gida....kana jina?"
"In sha Allah hajja"
"Allah yayi muku albarka,ya albarkaci rayuwarku,ya tsare dukkan abunqi"
"Amin amin,Allah ya qara girma da shekaru masu albarka" ya fada cikin jin dadi,har kullum yana ganin girma da qimar tsohuwar,saboda zallar qauna da take nuna musu shi da soulmate dinsa.
Zuwansu da baba gajen ba qaramin ma'ana yayi ba,domin itama ta hangi abinda hajjan ta hanga,duk da basu gaya mata ba,don haka bata barin zahran tayi komai,komai na gidan ta dauke shi,ita kanta zahran ba qaramin dadin zama da baba gajen takeyi ba,tana debe mata kewa,hakanan duk randa ta tashi jikin babu dadi zata gaya mata wani abu da zatayi wanda zaisa taji sauqi da qwarin jikin nata.
Ta fannin haidar kuwa ta samu dukkan wata kulawa taimako da qwarin gwiwa a matsayinta na mace mai haihuwar fari wadda batasan yadda abun yake ba,shi kansa bai barinta tayi wani abu da zai wahalar da ita,ta kowanne fanni ta zama 'yar lele ta gaske.
*_BAYAN WASU KWANAKI_*
Yana tsaye daga saman dining yana hada musu tea shi da ita a cup biyu,yanayi yana duba agogo,a shirye yake tsaf cikin wata dakakkiyar shadda sabuwa fil ruwan zuma,wanda saida aka sha daru shida zahran tashi kafin ya yarda ya sanyata,shiri ne na tafiyarsu jarabawa a rana ta farko,ya sake daga kansa yana duban hanya,sai gata ta fito dauke da plate a hannunta,sanye take da wani lafiyayyen lace itama ruwan zuma,dinkin riga da plain zani,sabida yace bai yarda ta saka skert ba.
Duban fuskarta yake sosai,tana tahowa inda yake din tana yatsina fuska
"Yau wani laziness kikeji hubby,kodai exam dince tun kafin a fara take bugunki?,karki fa damu,ina da zato mai qarfi a kanki,kisa a ranki an gamata kawai" ajjiye plate din tayi a gabansa,ta hade hannayenta waje guda 馃檹馃徑
"Bani da haufi tsoro ko shakka indai sojana yana kusa....mutumin dake iya kula da qasarsa ma bare ni mutum daya?,....na yadda da kaifin basirarsa,hakanan inda malami ne shi xaiyi wuya a sami malami kamarsa kaf qarninsa kuwa,koda bayan mutuwarsa ne da shekara dari" wani kallo ya kafeta dashi,yana jin kamar ya hadiyeta,gwana ce wajen iya tsara kalaman da zasu tafi da hankalin dukkan mai hankali,ya rasa amsar da zai bata illa tukuicin lallausan murmushinsa,wanda ya jima yana shaida mata ya tanadeshi ne kawai saboda ita,ta kuma yarda da hakan dari bisa dari,don takanyi mamakin yadda yake komawa zakin gaske a gaban duk wata mace koma bayanta,hatta da qannensa shakkar nan tasa tana cikin zukatansu
"Kawai dai qwan nan ne,tunda na fara soyashi zuciyata ke tashi...." Ta amsa mishi tambayarsa ta farko sanda take daukar cup din tea din daya miqa mata,idanu ya kuma zura mata yana karantarta sanda take kurbar tea din,har sai data lura,saita dage masa girarta dukka biyun,alamun tambayar lafiya?
"Anya ko hubby....anya ban jefa qwallona a raga ba?" Ido ta fiddo tana aje cup din
"Bana tunanin haka.....haba watanmu nawa sojana....kawai ko a gida banson qarnin qwai,kuma ko xanci ma saina yanka wadatacciyar albasa akai nake ci" kafadunsa ya dage yana bude plate din chips da qwan data aje masa
"Ohkey....amma ko chips din ai kyaci ko?" Fuska ta kyabe cike da shagwaba tana maqale kafada
"Nifa qamshinsu ya gama cikamin ciki.....saidai ka taimaka ka siyamin meatpie a wannan gurinnnnn" dariya taso bashi,tunda ya taba siya mata meatpie din ta maqale masa,saiya maqale kafada shima
"Naqi wayon,saidai idan kin yarda nima....." Qarshen zancan ya furta mata qasa qasa,sarai ta gane abinda yake fada,saita sakar masa kukan shagwaba,ta dauke hand bag dinta dake gabansa ta sauko daga dining din tana diddira qafa,dariya sosai yakeyi shima,ya aje abincin ya biyo bayanta.
Har suka je suka dawo yana tattalinta,suna gama exam din ta zagaya inda ya zauna zaman jiranta ta sameshi,bata yarda kowa ya biyota ba,ya gama ganeta amma tana togewa,kishinsa take hakan ya sanya bata hada kowa dashi.
Da taimakon Allah da kuma agazawar haidar din ta kammala jarrabawar cikin babbar nasara,babu qunci ko takura ko wahala mai yawa,wanda dalibi ke tsintar kansa a duk yayin jarrabawa,wanda tasan cewa sirrin hakan na tattare ne da dafawar haidar din.
Ta yadda da cewa samun masoyin gaskiya babban dace ne a rayuwa,hakanan rashin sa'a a soyayya kada ya sanya mace ta yanke tsammani da samun haske kuma mabudin yayewar dukkan matsalarta,abu daya ake buqata shine,ki sake hankalta a yayin da duk wata qaddara ta sameki ko kika aikata kuskure,kiyi qoqarin zama me kamewa,ki ninki zurfin dora abubuwanki saman sikeli da mizani fiye da ko yaushe,sannan ki zafafa da addu'a,babu ji babu gani,babu daga qafa babu hutu.
Imani da qaddararta da tayi,ta karbeta hannu bibbiyu,ta kuma tsarkake zuciyarta,ta riqe mutuncinta da mutuncin gidansu,ta kuma yi biyayya ga magabatanta shi yasa Allah ya dubeta yayi mata musaya mafi alkhairi,ba shakka yaudara nada zafi da ciwo,tana da qarfin da zatayi barazana ga rayuwar wanda aka yiwa ita,saidai kuma girman ubangiji ya shafe komai,qudirarsa da alkhairinsa kan bayinsa yawa ne dashi,koda yaushe ko godewa ubangiji bisa kowacce irin nau'in qaddarar daya tsagawa rayuwarka,tayi maka dadi ko bata yi maka ba,wannan shike nuni da cikar imanin bawa.
Randa sukayi paper din qarshe ta dinga jin jikinta sama sama,haka dai ta daure akayi sallama da qawaye da abokan karatu,ko cikin mota ma cikin seat ta lafewa haidar din,daya tambaya tace babu komai gajiya ce,bai gasgatata ba amma ya qyaleta,saboda ya lura kaman batason magana ne,zatonsa bai tabbata ba sai da suka bude falo zasu shiga,saita tafi luu zata fadi ya tarota,ya qarasar da ita saman kujera yana mata sannu,gaba daya ya rude cikin qanqanin lokaci,ruwa ya bata mai sanyi tasha,sai numfashinta ya koma normal
"Sannu"
"Lafiyata qalau" tayi qarfin halin fada,saboda zallar damuwar data hanga tattare dashi
"No hubby....baki da lafiya" don kada tayi masa musu kota bata masa lokacima yasa bai tsaya sauraren kalaman bakinta ba ya dauketa cak sai bandaki,ya ajjiyeta sannan ya tara mata ruwan wanka
"Ki wanka na baki minti goma,zan shirya na kaiki kiga likita" saiya fiddo mata towel soson wanka da sabulun wankan ya aje mata,sannan yaja mata qofar ya rufe,saiya wuce daya bandakin shima.
Idanu ya zuba mata sanda ta gama shirin ta fito,saiya riqe hannunta sosai
"Duk yadda kika kai ga boyemin baki da lafiya hubby bazai boyu ba,kin manta ne,ni dake ruhi daya ne yake rayuwa a gangar jiki guda biyu?" Murmushi ta sakar masa,saiya karata da jikinsa suna takawa a hankali yana sake gaya mata wasu kalaman da suka sanyata sakin ajiyar zuciya a jejjere.
A qalla ya kusa minti talatin zaune shida ita cikin motar riqe da hannayenta yana jero mata kalaman nuna zallar qauna da godiya a gareta,tun lokacin da likitan ya shaida masa tana dauke da juna biyu gaba daya yayi wani irin rudewa,ko a yanzun ma hawaye zahran ke futarwa,saboda kalaman da yake amfani dasu a kanta sun girmi kanta,kalamaine da take da cikakken yaqinin ba kowacce mace bace Allah yake mata baiwa da samun mijin da zai furta mata su ba
"Gobe as early as possible zamu wuce abuja...thank god kin gama abinda ya zaunar damu,kinji kuma yace kin da buqatar cikakken hutu,so zan buqaci hajja kawai ta bamu baba gaje mu wuce da ita....but...banda fadar dalili,don i sure tsaf hajja zata hanani tafiya dake" dariya sosai ya bata data tuna da hajjansu,hajiya hajja,ayi tsiya ayi dadi,tana sonsu tana tattalinsu,amma idan tsiyarta ta tashi har su saita dandana musu.
Kamar yadda ya tsara kuwa tun a daren ya gama hada musu abinda yasan suna da buqata,ba wasu kaya bane masu yawa,tunda komai a kwai a can,ya kira hajja yace baba gaje ta shirya gobe zata rakasu abuja,ta fara masa tambayoyi yace ta bari idan yazo gobe zasuyi magana,ranar kusan kwanan zaune yayi,rabi bacci rabi idanunsa biyu,duk sadda ya farka saiya tuna cewa wai shima ya kusa zama uba?.
Qarfe bakwai a gidan tayi musu
"Wai tafiya abujan na meye haka saikun daukemin gaje kuma?" Zahra ce ta marairaice fuska
"Haba hajja,can dinfa babu dadi wallahi xaman shuru" waiwayawa tayi ta dubeta
"To ba sai ya barki nan ba,ya dinga zuwa?" Baki zahra ta tura
"Habba hajja...a'ah wallahi,ni mijina zanbi"
"Na shiga uku ni fatsima.....yau naga abinda yafi xare tsayi.....innawuro ni kike gayawa haka kanki tsaye." Ilham da husna me zasuyi in banda dariya,baba gaje dake tsaye a gefe tana tayasu,shikam haidar dama bai shigo ba yana wajensu abba babba suna gaisawa,daga can ya tsaya wajen ummi don bincika me dame take da buqata,duk da bata rasa komai,amma bakan baisa ya daina hidima gareta ba,kwata kwacin yadda zaiyima gidansu.
Yana shigowa kuwa tace
"Kama hannun matarka ku ficemin,Allah ya kiyaye hanya,nikam yanzu kunfi qarfina,Allah rabamu qalau" yasan wata tsiyar aka tufka sai baice komai ba banda dariya da yake dannewa,amma ya godewa Allah da hajjan bata harbo jirginsu ba,haka suka fice bayan sunwa kowa sallama.
Shida ita a baya suka zauna,don bazai iya juriyar awanni suna waje daya amma ba ita a gefansa ba,baba gaje da driver suna gidan gaba,hakan ya baiwa zahra damar kwanciya sosai bisa jikinsa,don sam bata jin qwarin jikinta,shi kuma ya tattarota cikin jikin nasa sosai,ya gyara mata yadda zata fi jin dadin kwanciyar.
Tun basuyi nisa ba kiran hajja ya shigo wayarshi
"Anya lafiya zahra'u kuwa take?,ni sai da kuka wuce naga yanayinta baiyimin ba" cikin dakiyar nan tasa yace
"Lafiya take hajja....wani abu ya faru ne?"
"Um um....amma kawai sai nakega kamar me yaron ciki....koma meye ne ka kula da ita da kyau,sannan idan akwai wani abu da baku gane mishi ba kayi hanzarin dawomin da ita gida....kana jina?"
"In sha Allah hajja"
"Allah yayi muku albarka,ya albarkaci rayuwarku,ya tsare dukkan abunqi"
"Amin amin,Allah ya qara girma da shekaru masu albarka" ya fada cikin jin dadi,har kullum yana ganin girma da qimar tsohuwar,saboda zallar qauna da take nuna musu shi da soulmate dinsa.
Zuwansu da baba gajen ba qaramin ma'ana yayi ba,domin itama ta hangi abinda hajjan ta hanga,duk da basu gaya mata ba,don haka bata barin zahran tayi komai,komai na gidan ta dauke shi,ita kanta zahran ba qaramin dadin zama da baba gajen takeyi ba,tana debe mata kewa,hakanan duk randa ta tashi jikin babu dadi zata gaya mata wani abu da zatayi wanda zaisa taji sauqi da qwarin jikin nata.
Ta fannin haidar kuwa ta samu dukkan wata kulawa taimako da qwarin gwiwa a matsayinta na mace mai haihuwar fari wadda batasan yadda abun yake ba,shi kansa bai barinta tayi wani abu da zai wahalar da ita,ta kowanne fanni ta zama 'yar lele ta gaske.