← Book details Alkibla Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 20 OF 70

Sashe 20

Alkibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Hafsat ce,saita saki murmushi najin dadin ganin kiran 'yar uwartata
"Aini nayi fushi wallahi,babu abinda zakice dani" hafsan ta fada zahra na daga wayar
"Wayyo Allah na,me kuma nayi?"
"Au baki ma sani ba?,to bari na gaya miki,kinga na farko tunda mukayi aure zuwanki gidajenmu baifi a qirga ba,kowa qorafi yakeyi,na biyu kuma bani da lafiya,kowa yazo ya dubani,wasu sun kirani amma keda ya haidar baku zo ba banga kiranku ba,to wai don Allah meye marabarki da ya aliyyun ma?"
"Na yarda na miki laifi,amma ki daina hadani da wannan dagen....sannan kimin uzuri,rashin zuwa na gidanku wallahi hafsat makaranta ce,kuma kin sani,sannan lalurarki ni dana dawo babu wanda ya gayamin baki da lafiya"
"Eh ai saboda ansan ma ba zuwa zakiyi ba" murmushi tayi mai sauti
"Kiyi haquri....haba hansatuwa,aiba haka tsakaninmu,in sha Allah gobe ko jibi zaki ganni,kuma wannan karon bazan koma ba saina jewa kowa na kashe mitarku,ke ina tunanin ma da qyar idan ba strike za'a tafi ba wani satin,kinga idan hakan ta faru kwana daya daya zanwa kowa"
"Heee....na dai jiki kawai,a samu kizo dinma"
"Waima meya sameki?" Zahran ta fada tana qunshe dariya cikin salon tsokana saita dora da
"Kodai an gamu ne?"
"An gamu dake ba....idan kinzo kya gani"......

Tana tsaka da wannan maganar idanunta sukayi arba dasu,matasa ne su uku tsaye a gabanta sun tare hanyarta,saita sauke wayar da sauri daga kunnenta ba tare data samu sukunin yin sallama da hafsat ba
"Bani wayata!" Daya daga cikinsu ya fada cikin gadara yana miqa mata hannu,kai ka rantse da Allah wayar tasa ce,mamaki da tsoro ya sanyata tsaiwa tana kallonsu,daya daga cikinsu ya daka mata tsawa yana daga rigarsa ya zaro wuqa daga qugunsa
"Zaki miqo ko sai na farke miki ciki anan!" Kalaman da suka sake kadata kenan,ta miqa hannu zata basu wayar,dai dai sanda hasken mota ya dallaresu,ba tare da sun tsaya bi takan wayar ba suka ranta ana kare.

Tana tsaye a nan sannu a hankali motar ta qaraso,babban mutum ne a ciki,don ya kusa haifarta
"Garin yaya suka tareki?,maza ki wuce kibar wajen nan"
"To baba na gode" ta fada a tsorace tana yin gaba,saidai ko taku goma batayi ba taji magana a bayanta.

Tana waiwayawa sukayi arba dashi
"Karki tsorata,muje na rakaki,ina daga can baya na hangi meya faru" matashin ya fada,saita danji nutsuwa,don haka tabi bayanshi har suka sake gangarowa bakin titi sosai
"Al'ummarmu ta lalace ta zama wata irin al'umma,tarbiyya tayi qaranci,daba sata fashi da makami,garkuwa da mutane fyade da sauran munanan ayyuka,gaba daya su suka cika al'ummarmu suke mana barazanar rushewarta,gaba daya matsalar an rasa makamarta,saidai abu daya ne,duk wannan matsalar tushenta da asalinta gidan aure ne" kai ta gyada cike da gamsuwa,kalamansa sun dace da mutum mai hankali irinsa,wannan dalili ya sanya taji tsoron da takeji ya sake raguwa,hankalinta ya dan kwanta,daidai lokacin da wata adaidaita ta nufosu babu kowa a ciki ya tsaidata,sannan ya waiwaya yana tambayar zahran ina ta nufa tace mishi gadon qaya,shi kuma ya shaidawa mai napep din.

Sai data shiga sannan yace
"Abokina nima bari na zauna gefanka,tunda duka hanyace,idan ka sauketa ka qarasa dani tal'udu"
"To ba damuwa master,shigo mana" ya fada yana dan gyara masa gefansa.

Tunda suka shiga kusan zancan yadda arewa kullum ke tabarbarewa yakeyi,wanda wannan yana daya daga cikin abinda ke ciwa zahra tuwo a qwarya,wanda takejin inama ita marubuciya ce?,inama ace zata iya rubutu,tabbas da alqalaminta zai sauka ne tsakiyar arewa,kuma kan 'yan arewa,yadda muka share baki muna bacci har yaqi ya cimmana har saman gadajen baccinmu,yadda shugabanninmu da wakilanmu suka zama lusarai,'yan son kai da son zuciya,suka zama kamar aladu marasa kishin kansu ma bare na jama'ar da suke wakilta,indai zasu cika aljihunansu da kudi,indai ba zasu talauta ba,yadda muma muka zama masu matacciyar zuciya,muka saida mutunci qima daraja martaba da kwarjini irin na arewa da 'ya'yanta,kuma har gobe baccin muke ci gaba dayi,mun kasa tunanin kanmu,anata tsere mana ana mana fintikau,an raina mu bayan mun wuce raini,munfi qarfin raini da dukkan wani qasqanci,muna kashe junanmu,muna talauta kanmu,muna dakushe tattalin arziqin yankinmu,bayan mune ZUCIYAR NIGERIA din ma gaba daya,wannan shine babban tunanin zahra akoda yaushe.

"Wanne layi zaki shiga?" Taji ya tambaya,saita nunawa mai napep din har suka qarasa qofar gidansu sannan ta sauka,tana niyyar biyan mai abun hawan yace
"A'ah hajjaju ki barshi,inason in samu ladan"
"Na gode" ta fada kawai ta fada gida,don har yanzu tsoron data shiga dazu bai saketa ba,batasan sanda suka bar qofar gidan ba.

Sanda ta shiga gida ta gayawa hajja sallallami ta saka
"To alhmdlh da ubangiji ya tsare,shi yasa fa ba'a son fitar daren nan,shi kuma daya kawoki har nan Allah ya saka masa da alkhairi.....oh ni fatima,wannan lalacewar tarbiyya ubangiji yayi mana magani,shekara kusan saba'in a duniya amma baka daina ganin abubuwa iri iri ba" dariya zahra tayi
"Wa zaice kin shekara saba'in din hajja?,don dai kawai kinqi aure ne,kin dage sai a lahira idan kin hadu da tsoho alu"
"Kyaci gidanku idan na miqe na sameki,saina gwada miki tsohon qashi" zahran na dariya ta wuce dakinta,cikin ranta tana godewa Allah daya kubutar da ita,sai kuma ta tuna da mutumin da suka sauketa yanzun qofar gida,lallai yana da tunani mai kyau
"Allah ka gyara mana yankinmu dama qasarmu baki daya" ta furta a sarari tana cire daurin dankwalinta zuwa kayanta ma gaba daya ta fada bandaki don ta watsa ruwa ko zata ji dadin jikinta,kafin kuma ga fita ta nemi abincin dare,don tasan tuni gaje ta gama.
23/10/2021, 08:40 - 馃憤馃徎馃憤馃徎: 13
*OUM DUFAIL!!*
_GIDAN ADO 茦AWA DA KECE RAINI_馃拕馃拝馃徑

_OUM DUFAIL ta tanadar muku dukkan nau'in kayayyakin gyaran fata gashi dama jiki gaba daya ZAHIRINKI DA BA茒ININKI samfurin MAIDA TSOHUWA YARINYA_

*kayayyakinmu sune kamar haka*

FACE AND BODY SCRUB=2500(300ml)
Face and body mango butter=3k (250ml)
Face cream= 1800
Corretor oil/vitamin C oil=2k
Fairness skin lotion= 2500
Hot chocolate skin lotion 2500
Serum (for Nuckles )2k
Nuckles cream (stubborn)3500
Mix fruits Arabian black =soap 1800
Mix fruit glycerine soap =1900
Beetroot=1900
Coconut, milk,egg..face soap=1200
Lavender mix fruit soap =1800
Body wash =1500
cleanser=1600
Hair spray =700
Hair oil =1500
Hair relaxer =700
Hair butter 1700
Shampoo =1500
Breast=oil 2k powder 2k
Strech marks cream= 2k
Beetroot pink lips =700
Baby care soap glycerine=1k
Baby care butter =1500
Shea butter baby soap =700
Tsumin tula =2200
Tsumin zinariya =1200
Sliming tea =1500
Amarya set =25k
Liquid Arabian black soap =1900
Cleansing water =1500

*Ku dubamu a handle namu na Facebook da Instagram*
Ummu Dufail

*ko ta number wayarmu kamar haka*

07067943479

*_muna turawa kowacce jaha dake fadin nigeria da yardar Allah_*

*_INGANCI DA RAHUSA SHINE TAKENMU_*馃馃従馃馃従馃馃従
_____________________________

Kusan ta mance da abdulyasar gaba daya,don a qalla an kusa sati da wani yammaci akace ana sallama da ita,tayi mamaki sosai don a yanzu tasan bata da appointment da wani kan zaizo nemanta,har ta aika yaron tace masa yaje yace bata nan hajja ta tsaidashi,tace
"kace masa tana zuwa" fuska tadan bata tana duban hajja
"Nifa wallahi hajja ban san waye ba,da kin barshi kawai ya tafi"
"A'ah,ai baza'ayi haka ba,idan kuma shine mijin auren fa kika koreshi?" Saita dan buga qafa kadan tana turo baki,sannan ta miqe ta nufi daki.

Ganin doguwar riga ce a jikinta mai dogon hannu,kuma budadde ne dinkin babu ta inda ya kama jikinta saita sanya qaramin mayafi tayi rolling dashi sannan ta fito.

Yana jikin katangar gidan a jingine tayi sallama,da murmushi a fuskarsa ya dago yana amsawa,sai a sannan ta gane waye,saita dan sake masa fuska kadan suka gaisawa.

"Hala baki gane waye ba" dan qaramin murmushi tayi
"Na gane mana,sunanka ne kawai ban sani ba"
"Nima haka,ai anmin rowar suna,har muka rabu banji sunan malamar ba,shi yasa yanzu nayo tattaki nazo naji daga bakinta....nidai sunana abdulyasar......" Daga nan yayi mata bayanin kansa,itama bataqi ba ta gaya mishi sunanta,sannan ya gabatar mata da abinda ya kawoshi,ya kuma dora da cewa
"Ni da gaske nazo,kuma da gaske nake,ina fatan babu wani a gabana,kuma babu wanda ya rigani?" Murmushi kawai tayi ba tare data bashi amsa ba,dai dai sanda motar haidar ta danno layin,ta kuma qaraso gaban gidan,yayi horn mai gadi ya bude masa ya shige,da alama yau ya dawo yazo hutune kamar yadda yakanyi kusan duk qarshen wata.

Tasan halin ya haidar din duk da bata ga alamun ya ganta ba,amma gudun faruwar wani abu yasa tayi masa sallama ta shige gida,bayan ya nace ya amshi lambarta.
Chapter 20 · 0% Book details