Sashe 14
Alkibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Randa wata mardiyya taso takalarta da fada akan sir nasir din abun mamaki ya bata da dariya,don itadai tasan babu komai tsakaninsu daya wuce alaqar malami da dalibi,saitaqi biye mata,ta dinga dariya kan abinda ta fada din,saidai kafin sukai ga rubuta jarrabawa su tafi gida hutu tuni ya bayyanar mata da soyayyarshi.
Da farko tayi dari dari da abun,saboda wasu dalilai da suka hada da dokar makaranta,tsoron abinda ya faru tsakaninta da nuraddeen da kuma sa'idon dalibai,amma daga baya data zauna tayi nazari,ta fuskanci dukka halaye da dabi'un malam nasir din masu kyau ne,sannan ita kanta bawai bata sonshi ba kamar yadda ba zata ce wai tana sonshi kai tsaye ba,amma a qalla a yanzu suna gab da shiga ss 3,wanda ba zasu wuce wata 9 ba zasuyi candy,kuma kafin suyi candy dinne kowacce wanda zata aura zai gabatar da kanshi da magabantansa asan dashi,suna gama makaranta kuma sai maganar aure,tana ga mafi kyau shine ta bashi dama su fukanci juna,ba lallai abinda ya farun ya kuma maimaita kanshi,da wannan tunanin ta soma dan bashi dama kadan,duk da ta gaya masa abu mafi kyau ya bari suyi hutu ta koma gida tukunna,shima hakan ya masa,saboda haka bai zura jiki da yawa ba,ya bari har zuwa sanda suka gama jarabawar suka koma gida sannan ya fara kafa kanshi a zuciyar zahra din.
Cikin wani lokaci taqaitacce ya samawa kansa wajen zama,saboda mutum ne daya qware wajen iya tsara lafazi da iya jan hankali,uwa uba kuma iya ado,yana da faran faran,sa'annan da kansa ga buqaci ya gaisa da hajja tukunna kafin su abba,ta bashi dama suka gaisa,sai gashi cikin lokaci kadan kamar sun dade da hajjan,saboda ita dinma tana da son jama'a da saurin sabo.
Abinda yasa ta kuma sakewa dashi shine,akwai sanayya tsakaninsa da salim dan abban gwammaja yayan umminta,bai kuma fadi wani aibu ko mummunan hali tattare dashi ba,hakan yasa ta sake jin cewa ta samu abokin rayuwa kamar sauran 'yan uwanta......
_to masu karatu.....ya zata kaya?,muje zuwa,mu hadu gobe da izinin ubangiji_馃檹馃徑馃檹馃徑馃檹馃徑
23/10/2021, 08:38 - 馃憤馃徎馃憤馃徎: 09
*OUM DUFAIL!!*
_GIDAN ADO 茦AWA DA KECE RAINI_馃拕馃拝馃徑
_OUM DUFAIL ta tanadar muku dukkan nau'in kayayyakin gyaran fata gashi dama jiki gaba daya ZAHIRINKI DA BA茒ININKI samfurin MAIDA TSOHUWA YARINYA_
*kayayyakinmu sune kamar haka*
FACE AND BODY SCRUB=2500(300ml)
Face and body mango butter=3k (250ml)
Face cream= 1800
Corretor oil/vitamin C oil=2k
Fairness skin lotion= 2500
Hot chocolate skin lotion 2500
Serum (for Nuckles )2k
Nuckles cream (stubborn)3500
Mix fruits Arabian black =soap 1800
Mix fruit glycerine soap =1900
Beetroot=1900
Coconut, milk,egg..face soap=1200
Lavender mix fruit soap =1800
Body wash =1500
cleanser=1600
Hair spray =700
Hair oil =1500
Hair relaxer =700
Hair butter 1700
Shampoo =1500
Breast=oil 2k powder 2k
Strech marks cream= 2k
Beetroot pink lips =700
Baby care soap glycerine=1k
Baby care butter =1500
Shea butter baby soap =700
Tsumin tula =2200
Tsumin zinariya =1200
Sliming tea =1500
Amarya set =25k
Liquid Arabian black soap =1900
Cleansing water =1500
*Ku dubamu a handle namu na Facebook da Instagram*
Ummu Dufail
*ko ta number wayarmu kamar haka*
07067943479
*_muna turawa kowacce jaha dake fadin nigeria da yardar Allah_*
*_INGANCI DA RAHUSA SHINE TAKENMU_*馃馃従馃馃従馃馃従
_____________________________
*_BAYAN SATI BIYU_*
Karfe goma na safe ta kammala duk wani aiki da xata yiwa hajja,kasancewar idan tana nan ita da baba gaje suke mata duk wani aiki,koda taje da niyyar yiwa umminta wani abu takance ta bari taje ta yiwa hajjan,ita ilham zatayi mata wato qanwarta.
Tana gaban madubi tana shafa ma take tunanin zuwa gidan abban gwammaja wajen hasina,amma kuma daxun sir nasir yace mata zaya zo ganinta,tana mamakin yadda baya gajiya da jinta ko ganinta,har kunya yakan bata wani lokaci,ta samu tattali da kulawa wadda ta dara ta nuraddeen,sai a yanzu take ganin ma nuraddeen kamar shidin ba komai bane bai iya komai ba akan nasir din,ita kadai wani lokaci idan ta tunashi da kulawarsa gareta takan saki murmushi.
Cikin doguwar rigar swiss atampha cotton ta shirya mai yarfin stone a jiki,tana tsaka da fesa turare bayan ta taje gashinta ta daure wanda takeson hasina ta mata kitso taji hajja na qwala mata kira,saita aje turaren ta dauki dankwalinta a hannu ta fito.
Ita da abban tsakiya ne,sai haidar dake kallon labarai a VOA,yadda sojoji suka samu nasara a jahar borno cikin satin kan yaqi da 'yan ta'addan boko haram yana kuma magana da abban tsakiyan.
Da sauri ta ware dankwalinta ta daura tana qarasawa inda suke,Allah yasa bai ganta ba,shida abban ta gaida sannan ta maida hankalinta ga hajja dake mata bayanin
"Hadowa Aliyyu abincin kari maza da sauri....." Daga haka ta waiwaya tana mita
"Ku hakannan kuke bakuson cin abinci musamman da safe,koda yaushe sai an tilasta muku kuke ganewa....tafiya daga nan har dawakin kudu amma ciki babu komai,haka zaka tuqa iyayen naka kaje ka kasa qarasa tuqin saboda yunwa......tsabar zumudin zakayi sabon aure?" Kansa ya shafa yana cewa
"Kamar ba namiji ba?,karki.manta soja nake hajja.....nakan iya kwana uku banci ba wani lokacin sama da haka ma idan wani aikin ya taso mana".
Baki zahran ta tabe tana shigewa kitchen,cikin ranta tana fadin
"Ni ki qyaleshi kawai hajja ya tafin haka....yanzu da wahala yaci abincin nan baice wani abu ba akai sarkin qaqale" haka nan ta hada musu abincin daidai yadda zai ishesu shida abban tsakiya,ta isa falon ta dire musu tayi komawarta daki.
Bata sake fitowa ba sai da taji alamun fitarsu sannan ta fito riqe da mayafinta,sai data shiga kitchen ta hada kayan nata karin sannan ta dawo falon ta zauna kusa da hajja,tana tsaka da cin abincin hajjan tace
"Ina tunanin kafin ku koma makaranta fa iyayenku zasu nemi ganawa da magabatan samarinku,saboda yayanku ya tada maganar aurensa,yanzu haka can suka nufa garinsu yarinyar" duban hajjan tayi tana cin abincinta
"Shi zai kaisu da kanshi kenan?"
"Eh" ta bata amsa tana dauko remote don ta canza tasha,saita tabe baki
"Ey...da yake shi idanunsa da kwalli ai ba laifi bane,inda kaine da ka shiga uku" duka hajjan ta kai mata ta kuma sameta,ta gantsare tana cewa
"Wayyo Allah na.....hajja saikin karyani tukunna?"
"Eh gwara ai na karya ki din....tunda ke baki gajiya da dan banzan qorafi,zancan da ake miki daban wanda kike daban"
"Shikenan tunda haka kika ce,kullum nice me laifi" daga haka ta miqe da farantin a hannunta ta wuce kitchen tana zumbura baki,ta ajjiye sannan ta fito ta yafa mayafinta
"Zan wuce hajja" tayi maganar da alamun jin haushi har yanzu akan fuskarta,kudi hajjan ta miqa mata tana gaya mata kada tayi dare.
Kamar yadda hajjan tace kuwa a ranar akaje dawakin tofa dangin mahaifiyar Aliyyu haidar ko ince zaki aka tambaya masa aurenta hannun iyayenta da suke kawunnai a wajensa,mahaifinta qanine ga mahaifiyarsa,ba tare da wani bata lokaci ba aka basu auren,tunda shima kamar d'a ne a wajensu,suka dawo cike da farinciki da murnar yadda akayi komai cikin girma da karamci.
Washegari abba babba ya bada sanarwar kowacce cikinsu ta yiwa maneminta magana,indai da gaske yake yazo ya gabatar da kanshi tare da magabatansa,don suna so nan da shekara daya su hada su duka a aurar,mata biyar namiji daya.
Ba bata lokaci ta shaidawa sir nasir,wanda ya bayyana murnarsa sosai fiye da zatonta,don har mamaki ta dinga yi yadda yaketa farinciki,kusan ma kamar ya fita so da daukin abun,ya kuma tabbatar mata idan basu zama na farko ko na biyu a zuwa ba.....to ba zasu zama na uku ba.
Saurayin salma shi ya fara zuwa rana daya dana yusra,bayan kwana biyu saurayin yasira da magabatansu sukazo,washegari na hafsat ya bayyana shima,a ranar ne zahra ta karbo wayarta daga gyara,wadda ta matsu qwarai ta gyara din,don tafi kyautata zaton rashin wayar ne ya hana zuwan sir nasir kamar yadda yayi alqawari,tana jonawa a chargy ta lalubo number dinsa ta kira.
Bugu daya ya dauka,sai daya saki ajiyar zuciya sannan yace
"Kin wahalar dani fa"
"Me nayi kuma?"
"Kinsan tafiya ce ta kamani zuwa garinsu mama bagtatan....sai da muka dauki hanya na dinga kiranki ban sameki ba,yanzu haka ina kan hanyar dawowa....dama cewa nayi indai harna sauka ban sameki ba gida kawai zan zarto nan na ganki,idan ba haka ba nasan naci qarya yau na iya barci" murmushi ta saki cikin jin dadin kalamanshi
"To ai gashi na kiraka,nima shurun ya bani mamaki ya kuma daga min hankali"
"An rigani zuwa kenan?,nida naci burin na zama mutum na farko saboda girmamawa a gareki....amma duk da haka bata baci ba" hira suka fara daga haka,a qalla sun kusa kwashe awa daya sannan sukayi sallama,da zummar gobe zai shigo da magabatan nasa,idan yaso ya ganta gaba daya.
Kunya yasa ta rasa yadda zata shaidawa su abban cewa nasir din zaizo,sai da gari ya waye taga indai bata fada din ba zasu fice harkokinsu,dabara ta fado mata ta shaidawa hajja,ita kuma ta gaya musu.
Saidai tana shiga falo da niyyar wucewa dakin hajjan saboda bata kai ga fitowa ba wayarta dake hannunta ta dauki kuwwa,ganin sunan nasir yasa ta samu daya daga cikin kujerun ta zauna tana amsa wayar.
Tun daga sallamarsa taji alamun muryarsa ba daidai take ba,kafin takai ga tambayarsa shiya tambayeta
"Kin gayawa su abba zuwan namu ne yau?" Kai ta kada
"A'ah,yanzu dai nake shirin gaya musun" saiya sauke ajiyar zuciya mai nauyi,cikin alamu na damuwa tace
"Lafiya?"
"Fatima.....wallahi tun jiya nake fama da mama kan maganar....ashe turani garinsu da tayi akwai yarinyar data turawa ni wata na'ima....tunda naje yarinyar take rawar kai a kaina take kuma dawainiya dani,ni ban kawo komai ba sai yanzu dana dawo na kawo wannan maganar mama da abba duka sukace basusan zance ba,sun turani naga na'ima ne don mu hada kanmu".
Kasa magana zahran tayi,tayi shuru kawai tana jin yadda zuciyarta ke bugawa,gabanta ke faduwa
"Fatima....bana gaya miki wannan maganar bane don ki saka damuwa cikin ranki ba,na gaya miki ne don kada muyi jinkiri wajen zuwa ki zaci wani abu na daban....ba abun damuwa bane,nasan yadda zan shawo kan mama in sha Allah....kuma zanzo na samu abba nayi masa bayanin komai"
"To" abinda ta iya furtawa kenan a sanyaye,sallama tayi masa da kanta,don bata da qwarin gwiwar ci gaba da hira dashi,saita zame ta kwanta kawai cikin wani irin yanayi data kasa tantance wanne iri ne,bata fatan fa rasa nasir sam,saidai kuma tanajin tsoron faruwar hakan can qasan ranta.
Da farko tayi dari dari da abun,saboda wasu dalilai da suka hada da dokar makaranta,tsoron abinda ya faru tsakaninta da nuraddeen da kuma sa'idon dalibai,amma daga baya data zauna tayi nazari,ta fuskanci dukka halaye da dabi'un malam nasir din masu kyau ne,sannan ita kanta bawai bata sonshi ba kamar yadda ba zata ce wai tana sonshi kai tsaye ba,amma a qalla a yanzu suna gab da shiga ss 3,wanda ba zasu wuce wata 9 ba zasuyi candy,kuma kafin suyi candy dinne kowacce wanda zata aura zai gabatar da kanshi da magabantansa asan dashi,suna gama makaranta kuma sai maganar aure,tana ga mafi kyau shine ta bashi dama su fukanci juna,ba lallai abinda ya farun ya kuma maimaita kanshi,da wannan tunanin ta soma dan bashi dama kadan,duk da ta gaya masa abu mafi kyau ya bari suyi hutu ta koma gida tukunna,shima hakan ya masa,saboda haka bai zura jiki da yawa ba,ya bari har zuwa sanda suka gama jarabawar suka koma gida sannan ya fara kafa kanshi a zuciyar zahra din.
Cikin wani lokaci taqaitacce ya samawa kansa wajen zama,saboda mutum ne daya qware wajen iya tsara lafazi da iya jan hankali,uwa uba kuma iya ado,yana da faran faran,sa'annan da kansa ga buqaci ya gaisa da hajja tukunna kafin su abba,ta bashi dama suka gaisa,sai gashi cikin lokaci kadan kamar sun dade da hajjan,saboda ita dinma tana da son jama'a da saurin sabo.
Abinda yasa ta kuma sakewa dashi shine,akwai sanayya tsakaninsa da salim dan abban gwammaja yayan umminta,bai kuma fadi wani aibu ko mummunan hali tattare dashi ba,hakan yasa ta sake jin cewa ta samu abokin rayuwa kamar sauran 'yan uwanta......
_to masu karatu.....ya zata kaya?,muje zuwa,mu hadu gobe da izinin ubangiji_馃檹馃徑馃檹馃徑馃檹馃徑
23/10/2021, 08:38 - 馃憤馃徎馃憤馃徎: 09
*OUM DUFAIL!!*
_GIDAN ADO 茦AWA DA KECE RAINI_馃拕馃拝馃徑
_OUM DUFAIL ta tanadar muku dukkan nau'in kayayyakin gyaran fata gashi dama jiki gaba daya ZAHIRINKI DA BA茒ININKI samfurin MAIDA TSOHUWA YARINYA_
*kayayyakinmu sune kamar haka*
FACE AND BODY SCRUB=2500(300ml)
Face and body mango butter=3k (250ml)
Face cream= 1800
Corretor oil/vitamin C oil=2k
Fairness skin lotion= 2500
Hot chocolate skin lotion 2500
Serum (for Nuckles )2k
Nuckles cream (stubborn)3500
Mix fruits Arabian black =soap 1800
Mix fruit glycerine soap =1900
Beetroot=1900
Coconut, milk,egg..face soap=1200
Lavender mix fruit soap =1800
Body wash =1500
cleanser=1600
Hair spray =700
Hair oil =1500
Hair relaxer =700
Hair butter 1700
Shampoo =1500
Breast=oil 2k powder 2k
Strech marks cream= 2k
Beetroot pink lips =700
Baby care soap glycerine=1k
Baby care butter =1500
Shea butter baby soap =700
Tsumin tula =2200
Tsumin zinariya =1200
Sliming tea =1500
Amarya set =25k
Liquid Arabian black soap =1900
Cleansing water =1500
*Ku dubamu a handle namu na Facebook da Instagram*
Ummu Dufail
*ko ta number wayarmu kamar haka*
07067943479
*_muna turawa kowacce jaha dake fadin nigeria da yardar Allah_*
*_INGANCI DA RAHUSA SHINE TAKENMU_*馃馃従馃馃従馃馃従
_____________________________
*_BAYAN SATI BIYU_*
Karfe goma na safe ta kammala duk wani aiki da xata yiwa hajja,kasancewar idan tana nan ita da baba gaje suke mata duk wani aiki,koda taje da niyyar yiwa umminta wani abu takance ta bari taje ta yiwa hajjan,ita ilham zatayi mata wato qanwarta.
Tana gaban madubi tana shafa ma take tunanin zuwa gidan abban gwammaja wajen hasina,amma kuma daxun sir nasir yace mata zaya zo ganinta,tana mamakin yadda baya gajiya da jinta ko ganinta,har kunya yakan bata wani lokaci,ta samu tattali da kulawa wadda ta dara ta nuraddeen,sai a yanzu take ganin ma nuraddeen kamar shidin ba komai bane bai iya komai ba akan nasir din,ita kadai wani lokaci idan ta tunashi da kulawarsa gareta takan saki murmushi.
Cikin doguwar rigar swiss atampha cotton ta shirya mai yarfin stone a jiki,tana tsaka da fesa turare bayan ta taje gashinta ta daure wanda takeson hasina ta mata kitso taji hajja na qwala mata kira,saita aje turaren ta dauki dankwalinta a hannu ta fito.
Ita da abban tsakiya ne,sai haidar dake kallon labarai a VOA,yadda sojoji suka samu nasara a jahar borno cikin satin kan yaqi da 'yan ta'addan boko haram yana kuma magana da abban tsakiyan.
Da sauri ta ware dankwalinta ta daura tana qarasawa inda suke,Allah yasa bai ganta ba,shida abban ta gaida sannan ta maida hankalinta ga hajja dake mata bayanin
"Hadowa Aliyyu abincin kari maza da sauri....." Daga haka ta waiwaya tana mita
"Ku hakannan kuke bakuson cin abinci musamman da safe,koda yaushe sai an tilasta muku kuke ganewa....tafiya daga nan har dawakin kudu amma ciki babu komai,haka zaka tuqa iyayen naka kaje ka kasa qarasa tuqin saboda yunwa......tsabar zumudin zakayi sabon aure?" Kansa ya shafa yana cewa
"Kamar ba namiji ba?,karki.manta soja nake hajja.....nakan iya kwana uku banci ba wani lokacin sama da haka ma idan wani aikin ya taso mana".
Baki zahran ta tabe tana shigewa kitchen,cikin ranta tana fadin
"Ni ki qyaleshi kawai hajja ya tafin haka....yanzu da wahala yaci abincin nan baice wani abu ba akai sarkin qaqale" haka nan ta hada musu abincin daidai yadda zai ishesu shida abban tsakiya,ta isa falon ta dire musu tayi komawarta daki.
Bata sake fitowa ba sai da taji alamun fitarsu sannan ta fito riqe da mayafinta,sai data shiga kitchen ta hada kayan nata karin sannan ta dawo falon ta zauna kusa da hajja,tana tsaka da cin abincin hajjan tace
"Ina tunanin kafin ku koma makaranta fa iyayenku zasu nemi ganawa da magabatan samarinku,saboda yayanku ya tada maganar aurensa,yanzu haka can suka nufa garinsu yarinyar" duban hajjan tayi tana cin abincinta
"Shi zai kaisu da kanshi kenan?"
"Eh" ta bata amsa tana dauko remote don ta canza tasha,saita tabe baki
"Ey...da yake shi idanunsa da kwalli ai ba laifi bane,inda kaine da ka shiga uku" duka hajjan ta kai mata ta kuma sameta,ta gantsare tana cewa
"Wayyo Allah na.....hajja saikin karyani tukunna?"
"Eh gwara ai na karya ki din....tunda ke baki gajiya da dan banzan qorafi,zancan da ake miki daban wanda kike daban"
"Shikenan tunda haka kika ce,kullum nice me laifi" daga haka ta miqe da farantin a hannunta ta wuce kitchen tana zumbura baki,ta ajjiye sannan ta fito ta yafa mayafinta
"Zan wuce hajja" tayi maganar da alamun jin haushi har yanzu akan fuskarta,kudi hajjan ta miqa mata tana gaya mata kada tayi dare.
Kamar yadda hajjan tace kuwa a ranar akaje dawakin tofa dangin mahaifiyar Aliyyu haidar ko ince zaki aka tambaya masa aurenta hannun iyayenta da suke kawunnai a wajensa,mahaifinta qanine ga mahaifiyarsa,ba tare da wani bata lokaci ba aka basu auren,tunda shima kamar d'a ne a wajensu,suka dawo cike da farinciki da murnar yadda akayi komai cikin girma da karamci.
Washegari abba babba ya bada sanarwar kowacce cikinsu ta yiwa maneminta magana,indai da gaske yake yazo ya gabatar da kanshi tare da magabatansa,don suna so nan da shekara daya su hada su duka a aurar,mata biyar namiji daya.
Ba bata lokaci ta shaidawa sir nasir,wanda ya bayyana murnarsa sosai fiye da zatonta,don har mamaki ta dinga yi yadda yaketa farinciki,kusan ma kamar ya fita so da daukin abun,ya kuma tabbatar mata idan basu zama na farko ko na biyu a zuwa ba.....to ba zasu zama na uku ba.
Saurayin salma shi ya fara zuwa rana daya dana yusra,bayan kwana biyu saurayin yasira da magabatansu sukazo,washegari na hafsat ya bayyana shima,a ranar ne zahra ta karbo wayarta daga gyara,wadda ta matsu qwarai ta gyara din,don tafi kyautata zaton rashin wayar ne ya hana zuwan sir nasir kamar yadda yayi alqawari,tana jonawa a chargy ta lalubo number dinsa ta kira.
Bugu daya ya dauka,sai daya saki ajiyar zuciya sannan yace
"Kin wahalar dani fa"
"Me nayi kuma?"
"Kinsan tafiya ce ta kamani zuwa garinsu mama bagtatan....sai da muka dauki hanya na dinga kiranki ban sameki ba,yanzu haka ina kan hanyar dawowa....dama cewa nayi indai harna sauka ban sameki ba gida kawai zan zarto nan na ganki,idan ba haka ba nasan naci qarya yau na iya barci" murmushi ta saki cikin jin dadin kalamanshi
"To ai gashi na kiraka,nima shurun ya bani mamaki ya kuma daga min hankali"
"An rigani zuwa kenan?,nida naci burin na zama mutum na farko saboda girmamawa a gareki....amma duk da haka bata baci ba" hira suka fara daga haka,a qalla sun kusa kwashe awa daya sannan sukayi sallama,da zummar gobe zai shigo da magabatan nasa,idan yaso ya ganta gaba daya.
Kunya yasa ta rasa yadda zata shaidawa su abban cewa nasir din zaizo,sai da gari ya waye taga indai bata fada din ba zasu fice harkokinsu,dabara ta fado mata ta shaidawa hajja,ita kuma ta gaya musu.
Saidai tana shiga falo da niyyar wucewa dakin hajjan saboda bata kai ga fitowa ba wayarta dake hannunta ta dauki kuwwa,ganin sunan nasir yasa ta samu daya daga cikin kujerun ta zauna tana amsa wayar.
Tun daga sallamarsa taji alamun muryarsa ba daidai take ba,kafin takai ga tambayarsa shiya tambayeta
"Kin gayawa su abba zuwan namu ne yau?" Kai ta kada
"A'ah,yanzu dai nake shirin gaya musun" saiya sauke ajiyar zuciya mai nauyi,cikin alamu na damuwa tace
"Lafiya?"
"Fatima.....wallahi tun jiya nake fama da mama kan maganar....ashe turani garinsu da tayi akwai yarinyar data turawa ni wata na'ima....tunda naje yarinyar take rawar kai a kaina take kuma dawainiya dani,ni ban kawo komai ba sai yanzu dana dawo na kawo wannan maganar mama da abba duka sukace basusan zance ba,sun turani naga na'ima ne don mu hada kanmu".
Kasa magana zahran tayi,tayi shuru kawai tana jin yadda zuciyarta ke bugawa,gabanta ke faduwa
"Fatima....bana gaya miki wannan maganar bane don ki saka damuwa cikin ranki ba,na gaya miki ne don kada muyi jinkiri wajen zuwa ki zaci wani abu na daban....ba abun damuwa bane,nasan yadda zan shawo kan mama in sha Allah....kuma zanzo na samu abba nayi masa bayanin komai"
"To" abinda ta iya furtawa kenan a sanyaye,sallama tayi masa da kanta,don bata da qwarin gwiwar ci gaba da hira dashi,saita zame ta kwanta kawai cikin wani irin yanayi data kasa tantance wanne iri ne,bata fatan fa rasa nasir sam,saidai kuma tanajin tsoron faruwar hakan can qasan ranta.