Sashe 24
Alkibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana sane da maganar da sukayi da abdulyassar din kan ta jirashi zai kirata,tasan kuma tsaf bacci zai iya daukarta,don haka sai kawai taja laptop dinta 'yar qarama da abban gwammaja ya siya mata ta kunna,ta zabo daya daga cikin fina finan ciki ta kunna ta soma kalla.
Tun tana cijewa tana kallon har idanunta sukayi nauyi,batasan sadda bacci ya dauketa ba.
Sanda ta farka da sauri ta jawo waya tana dubawa,a zatonta zata samu miscal din abdulyasar din,babu miscal babu kuma saqo,ta kalli agogo,sha biyu na dare har da rabi,kenan ya saba lokacin da yace zaiyi kiran nata?,hakanan sai taji idanunta ya bushe,baccin yayi nasa guri,saita miqe ta shiga bandaki ta daura alwala,ta dawo ta tada salla.
Ta kusa kaiwa qarfe biyu saura na dare tana zaune saman abun sallahn,har bacci ya sake dibanta taji qarar wayartata,saita miqa hannu ta dauko wayar,idanunta ya sauka kan agogon qarfe biyu da rabi na dare,ga mamakinta lawal ne abokin abdulyassar yake kiran,sosai hakan ya bata mamaki,wata mummunar faduwar gaba ta ziyarceta har batasan sanda ta daga wayar ba.
Muryar lawal dince ta bayyana cikin tsantsar tashin hankali yake fadin
"Zahra....abdul ya mutu,abdul ya rasu,qarfe sha biyu na dare yayi hatsari a hanyarsa ta tafiya,Allah yayi masa cikawa a take" dif wuta ta dauke mata,saita daina jin abinda lawal din yake fada,sai wata qara dake ratsa kunnenta kamar an buga qarfe da qarfe,ita dai batasan mintinan data shafe a haka ba,batasan kuma sanda lawal ya katse nashi kiran ba,batasan yadda akai ta kai kanta dakin hajja ba,sai ganinta tayi ta fada saman hajjan tana wani irin numfashi.
A matuqar firgice hajjan ta miqe ta zauna,don dama bata jima da gama sallar dare ba ta koma ta kwanta
"Zahra'u....zahra'u!....mene ne?,innalillahi wa inna ilaihi raji'un,yi kuka....kiyi kuka zahra'u,barshi ya fito" ta fada taba danne mata qirji,ganin yadda yake sama da qasa numfashinta kuma na wahalar shaqa,cikin ikon Allah ta fusgo numfashin da qarfi sai kuma ta saki wani qaqqarfan kuka ta fada jikin hajja gaba daya ta qanqameta
"Innalillahi" hajja keta maimaitawa,cikin ikon Allah itama zahran saita kama,tsayin wasu mintuna masu tsaho sannan ta iya magana cikin sheshsheqar kuka
"Hajja.....abudul....yassar ya.....mutu,yayi hatsari baya.....n nyabar wajena,ya rasu hajja!" Ta qarashe cikin gunjin kuka.
Sosai hankalin hajjan ya tashi,ta sake qara qarfin salatinta tana kuma maimatawa,wannan dare ya zamewa zahra dare mai tsaho duhu da kuma qunci,haka suka zauna ita kuka hajja lallashi,kafin gari yakai ga wayewa tuni idanunta suka suntuma suka kumbure,qwayar idanunta dukka sun shige ciki.
Suna idar da sallar asuba hajjan ta daga waya ta kira abba yusuf,saboda abba babba baya gari,cikin lokaci qanqani ya iso,bayan su gaisa ta shaida masa zancan rasuwar
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" shima ya dinga maimaitawa
"Yanzu abinda za'ayi....inaga idan gari ya sake shaaa,ka bawa mustapha ko shamsu muqulli sukaita gidansu yaron,don hankalinta bazai taba kwanciya ba,ba zata zauna ba,in yaso idan ya dawo daga kaitan zuwa lokacin mu mun kintsa saiya miqa mu,idan mukaje saimu duka mu dawo tare,ku kuma ko zuwa yamma haka zuwa dare kwa leqa ku yiwa iyayensa maza ta'aziyya"
"To shikenan,Allah yayi masa rahama,yasa ya huta".
Da qyar hajja ta sanyata tayi wanka,ta shirya cikin doguwar riga da hijabi,duk wanda ya ganta saiya tausaya mata,saboda yadda gaba daya fuskarta ta sauya saboda kuka,ga wani irin ciwon kai daya saukar mata lokaci daya,har dan zazzabi zazzabi takeji.
Kafin su tafi saiga hafsat ta fito itama a shirye,hajja zatayi qorafin ta koma tace da ita
"Ba za'a barta ta tafi daga ita saisu umaima yara ba,na kirashi na gaya masa mutuwar,nace zan rakata yace babu damuwa"
"Khalas....shikenan" hajja ta fada sanda hafsat din ta shige motar,shamsu ya tayar da motar suka fice.
Ko a cikin motar ma dai kukan take yaqi tsaya mata,ta dora kanta saman kafadar hafsat tana shashsheqa
"Kiyi haquri zahra ki masa addu'a,a yanzu ita yafi buqata"
"Shikenan hafsa...shima ya tafi ya barni,hafsat nice mutum ta qarshe da yazo wajenta,nice mutum ta qarshe daya kira da wayarsa,ashe da yazo bankwana yazo yimin?,ashe ya tafi kenan?" Sosai ta karyarwa da hafsat zuciya,haka taci gaba da lallashinta har suka isa qofar gidan su abdulyasar da taimakon kwatance da lawal ya dinga musu.
Babu kowa qofar gidan sai daidaikin mutane,da alama an tafi kaishi makwancinsa na gaskiya,hafsat din ita ta riqe zahra har zuwa cikin gidan.
Cike gidan yake da mutane,wasu kuka wasu tagumi,hafsat ce mai qarfin halin gaidasu,sannan ta tambayi inda hajiyan abdulyassar din take,aka nuna musu wani falo dake cike da jama'a suka nufi can.
Kana kallonta zaka gane mamansa ce saboda suna kama,tana zaune saman kujera,sanye da ash din hijabi da carbi a hannunta tana ja.
Gabanta suka samu suka isa,zahran ta zube a gabanta hafsa ta zauna gefanta,hafsat ce ta fara yi mata ta'a ziyya sannan zahra cikin shaqewar murya,daga bisani hafsa tace
"Zahra ce hajiya" hafsan ta zaci zataga wani alamu na nuna kulawa ko sanayyar sanin sunan,babu wani alamu na ta gane abinda hafsan ke fada,tadai ce
"Allah sarki,mun gode Allah ya bada lada".
Zaman shuru ne yaci gaba da wanzuwa a falon,zahra na cikin hijabinta tana kuka,ganin yadda falon ke sake cika yasa hafsan ta sama musu wajen zama daga waje,abinda ta lura dashi har suka tashi hajiyan ma bata lura da tashin nasu ba,zataso tambayar zahran cewa anya sunsanta kuwa?,to amma yanayin da a yanzu take ciki ba lokaci bane na mata wannan tambayar ba.
Awa kusan guda kenan da zamansu a wajen zahra ga dubi hafsa
"Hafsa qishirwa nakeji,bazan kuma iya shan komaj cikin gidan nan ba"
"To muje waje mana mu samu wani shop ko lemo kisha" kai ta kada
"Ruwanma ya wadatar" ta fada tana miqewa da qyar
"Wash kaina" ta fada sanda ta miqe din
"Lafiya?" Hafsa ta tambayeta,saita dan ya mutsa fuska
"Mtsweww,kaina ke ciwo"
"Dole ai,wannan kukan da kikayi ai ba kadan bane"da haka suka taka zuwa wajen gidan.
A yanzun layin a dinke yake da jama'a,da alama har sun dawo kenan,haka yasa sabuwar qwalla suka zirarowa zahra,yanzu haka abdul nacan kwance,nacan kwance qasan qasa,babu kowa saishi kadai,babu kowa sai halayyarsa da ayyukansa.
"Zahra duka shagunan layin nan a rufe suke" taji hafsat na fada,kai ta gyada tana share hawayen fuskarta
"Eh na gani,amma layin nan kamar layin gidansu rabi'ah ishaq ko?,da kika tana rakoni?"
"Eh tabbas,aiga gidan nasu can ma qarshen layi"
"Yauwa,mu qarasa nasha ruwan a can kawai"
"Ok" hafsat ta fada,kai tsaye suka miqe zuwa gaba,wanda gidan ke jerin gidajen dake jikin gidansi abdulyasar din,tsakaninsu da gidansu abdulyasar din gida biyar ne kacal.
Da sallama suka shiga gidan,wata mace dake duqe bakin fanfo tana wanki ta daga kai tana amsa musu sallamar
"Ku qaraso mana" ta fada tana dagowa daga duqen da tayi.
Gaidata sukayi sannan suka shaida mata su din qawayen rabi'ah ne
"Ayyah,kuma gashi bata dade ta fita ba wallahi"murmushin qarfin hali zahra tayi
"Babu komai,dama ruwa muka shigo zamu sha_ta qarashe maganar ta duqawa kamar wadda zatayi ruku'u saboda yadda kanta keci gaba da sara mata
"To babu damuwa,bari A kawo muku" saita yi gaba daga can qarshen tsakar gidan,ta bude wani fridge dan qarami dake qasan rumfa tana cewa
"Hala daga gidan rasuwar gidan su abdul kuke?" Hafsat ce ta amsa mata
"Eh wallahi" cikin nuna jimami da alhini ta sake cewa sanda take ciro ruwan
"Ai mun tashi da tashin hankali yau,mutuwar matashi yaro,babban abun tausayin ma,yau satinsa biyu cif da kai kudin aure....." Kalma mafi girma da muni data daki zuciya da kunnuwan zahra,kalmar da taji kamar a wani mugun mafarki aka furtata,kafin ta dawo hayyacinta sautin muryar hafsat cike da zallar mamaki ta furta
"Sati biyu da kai kudin aurensa?"amsa musu tayi sanda take rufe fridge din tana dawowa zuwa garesu
"Wallahi Allah,bari kawai....daxun yarinyar da ya kaiwa kudin tazo,abun gwanin ban tausayi,bakiga kukan da take ba,tana faduwa ana dagata,dukkanmu sai data sanyamu qwalla,sai data sake saka hajiyarsa kuka sosai,qarshe kasa zama tayi sai gida aka maidata,kinga keyholder din kai kudin akan window na ma,ni ko amfani da ita bankai ga yi ba" qarashen maganar yazo dai dai da zamewar zahra daga durquson da tayi zuwa zama dabas a qasa
"La haula wala quwwata illa billah" kawai zahran ke fada cikin zuciyarta,bakinta zuwa maqogaronta ya sake bushewa raqayau kamar bata taba kurbar maqwarwa daya ta ruwa ba tunda Allah ya halicceta,tana jin sanda matar ke miqo ruwan amma saita kasa amsa,maimakon karba ma saita miqe tsaye kawai ta nufi qofa,bataga wani sauran amfanin zamanta ba kuma,tana jiyo hafsa na mata godiya gami da sallama.
Tuni ta miqi hanya ba tare dako waiwaye ba,ita kanta hafsat din sai cimmata tayi a hanyar
"Zahra....da kin tsaya ya shamsu ya dawo ya maidamu" kaita girgixa idanunta na sauka kan gungun abokan abdulyasar dake zaune qasan wata rumfa,can ta hango auwal a tsakiyarsu,wani abu ya caki zuciyarta,tsanar auwal din ta kamata,tabbas babu shakka yasan komai,yasan duk abinda ke wakana tunda amininsa ne,dashi aka hada baki,dashi aka rufeta
"Muje kawai hafsa,ma hadu a hanya" a yanayin data ga ta shiga,tasan cewa koda bayani tayi mata babu lallai ta fahinta,don haka taci gaba da binta a baya suna tafe zafin rana na dukansu.
Basuyi nisa ba suka soma jin hirar wasu mata biyu a bayansu
"Kai mutuwa....mutuwa masu gari,babu ruwanta da babba ko yaro,tsoho ko tsohuwa kawai dauka take"
"Hmmm....kedai Allah yasa mu dace,mutuwa ma irin wannan ta abdul ai tafi ratsa jiki da daga hankali,mutuwar saurayi?,sati biyu kacal da kai kudin aure ashe ba za'ayi auren ba,babu ma abu mafi tausayi irin yarinyar daya kaiwa kudin,kamar zata shide wallahi abun tausayi"
"Ai da tausayi,Allah yasa mu cika da imani".
Cak zahran da hafsan duka suka tsaya,a sace zahra ya waiwaya ta dubesu,dukkansu babu wanda tasan fuskarsa a cikinsu,suna tsaye sukazo suka giftasu,da alama ma basu ankara da tsaiwarsu ba,sukayi gaba suna ci gaba da hirarsu.
A zafafe zahra ta soma takawa tana koma zuwa layin da suka baro,hafsa ta cafki hannunta
"Ina zaki?"
"Zanyi magana da auwal" daga haka ta zame hannunta ta koma.
Suna nan inda ta barsu,harda qarin wasu abokan nashi wadanda yakanje dasu lokaci zuwa lokaci,dukkansu tasan fuskarsu sunsan fuskarta.
Tun tana cijewa tana kallon har idanunta sukayi nauyi,batasan sadda bacci ya dauketa ba.
Sanda ta farka da sauri ta jawo waya tana dubawa,a zatonta zata samu miscal din abdulyasar din,babu miscal babu kuma saqo,ta kalli agogo,sha biyu na dare har da rabi,kenan ya saba lokacin da yace zaiyi kiran nata?,hakanan sai taji idanunta ya bushe,baccin yayi nasa guri,saita miqe ta shiga bandaki ta daura alwala,ta dawo ta tada salla.
Ta kusa kaiwa qarfe biyu saura na dare tana zaune saman abun sallahn,har bacci ya sake dibanta taji qarar wayartata,saita miqa hannu ta dauko wayar,idanunta ya sauka kan agogon qarfe biyu da rabi na dare,ga mamakinta lawal ne abokin abdulyassar yake kiran,sosai hakan ya bata mamaki,wata mummunar faduwar gaba ta ziyarceta har batasan sanda ta daga wayar ba.
Muryar lawal dince ta bayyana cikin tsantsar tashin hankali yake fadin
"Zahra....abdul ya mutu,abdul ya rasu,qarfe sha biyu na dare yayi hatsari a hanyarsa ta tafiya,Allah yayi masa cikawa a take" dif wuta ta dauke mata,saita daina jin abinda lawal din yake fada,sai wata qara dake ratsa kunnenta kamar an buga qarfe da qarfe,ita dai batasan mintinan data shafe a haka ba,batasan kuma sanda lawal ya katse nashi kiran ba,batasan yadda akai ta kai kanta dakin hajja ba,sai ganinta tayi ta fada saman hajjan tana wani irin numfashi.
A matuqar firgice hajjan ta miqe ta zauna,don dama bata jima da gama sallar dare ba ta koma ta kwanta
"Zahra'u....zahra'u!....mene ne?,innalillahi wa inna ilaihi raji'un,yi kuka....kiyi kuka zahra'u,barshi ya fito" ta fada taba danne mata qirji,ganin yadda yake sama da qasa numfashinta kuma na wahalar shaqa,cikin ikon Allah ta fusgo numfashin da qarfi sai kuma ta saki wani qaqqarfan kuka ta fada jikin hajja gaba daya ta qanqameta
"Innalillahi" hajja keta maimaitawa,cikin ikon Allah itama zahran saita kama,tsayin wasu mintuna masu tsaho sannan ta iya magana cikin sheshsheqar kuka
"Hajja.....abudul....yassar ya.....mutu,yayi hatsari baya.....n nyabar wajena,ya rasu hajja!" Ta qarashe cikin gunjin kuka.
Sosai hankalin hajjan ya tashi,ta sake qara qarfin salatinta tana kuma maimatawa,wannan dare ya zamewa zahra dare mai tsaho duhu da kuma qunci,haka suka zauna ita kuka hajja lallashi,kafin gari yakai ga wayewa tuni idanunta suka suntuma suka kumbure,qwayar idanunta dukka sun shige ciki.
Suna idar da sallar asuba hajjan ta daga waya ta kira abba yusuf,saboda abba babba baya gari,cikin lokaci qanqani ya iso,bayan su gaisa ta shaida masa zancan rasuwar
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" shima ya dinga maimaitawa
"Yanzu abinda za'ayi....inaga idan gari ya sake shaaa,ka bawa mustapha ko shamsu muqulli sukaita gidansu yaron,don hankalinta bazai taba kwanciya ba,ba zata zauna ba,in yaso idan ya dawo daga kaitan zuwa lokacin mu mun kintsa saiya miqa mu,idan mukaje saimu duka mu dawo tare,ku kuma ko zuwa yamma haka zuwa dare kwa leqa ku yiwa iyayensa maza ta'aziyya"
"To shikenan,Allah yayi masa rahama,yasa ya huta".
Da qyar hajja ta sanyata tayi wanka,ta shirya cikin doguwar riga da hijabi,duk wanda ya ganta saiya tausaya mata,saboda yadda gaba daya fuskarta ta sauya saboda kuka,ga wani irin ciwon kai daya saukar mata lokaci daya,har dan zazzabi zazzabi takeji.
Kafin su tafi saiga hafsat ta fito itama a shirye,hajja zatayi qorafin ta koma tace da ita
"Ba za'a barta ta tafi daga ita saisu umaima yara ba,na kirashi na gaya masa mutuwar,nace zan rakata yace babu damuwa"
"Khalas....shikenan" hajja ta fada sanda hafsat din ta shige motar,shamsu ya tayar da motar suka fice.
Ko a cikin motar ma dai kukan take yaqi tsaya mata,ta dora kanta saman kafadar hafsat tana shashsheqa
"Kiyi haquri zahra ki masa addu'a,a yanzu ita yafi buqata"
"Shikenan hafsa...shima ya tafi ya barni,hafsat nice mutum ta qarshe da yazo wajenta,nice mutum ta qarshe daya kira da wayarsa,ashe da yazo bankwana yazo yimin?,ashe ya tafi kenan?" Sosai ta karyarwa da hafsat zuciya,haka taci gaba da lallashinta har suka isa qofar gidan su abdulyasar da taimakon kwatance da lawal ya dinga musu.
Babu kowa qofar gidan sai daidaikin mutane,da alama an tafi kaishi makwancinsa na gaskiya,hafsat din ita ta riqe zahra har zuwa cikin gidan.
Cike gidan yake da mutane,wasu kuka wasu tagumi,hafsat ce mai qarfin halin gaidasu,sannan ta tambayi inda hajiyan abdulyassar din take,aka nuna musu wani falo dake cike da jama'a suka nufi can.
Kana kallonta zaka gane mamansa ce saboda suna kama,tana zaune saman kujera,sanye da ash din hijabi da carbi a hannunta tana ja.
Gabanta suka samu suka isa,zahran ta zube a gabanta hafsa ta zauna gefanta,hafsat ce ta fara yi mata ta'a ziyya sannan zahra cikin shaqewar murya,daga bisani hafsa tace
"Zahra ce hajiya" hafsan ta zaci zataga wani alamu na nuna kulawa ko sanayyar sanin sunan,babu wani alamu na ta gane abinda hafsan ke fada,tadai ce
"Allah sarki,mun gode Allah ya bada lada".
Zaman shuru ne yaci gaba da wanzuwa a falon,zahra na cikin hijabinta tana kuka,ganin yadda falon ke sake cika yasa hafsan ta sama musu wajen zama daga waje,abinda ta lura dashi har suka tashi hajiyan ma bata lura da tashin nasu ba,zataso tambayar zahran cewa anya sunsanta kuwa?,to amma yanayin da a yanzu take ciki ba lokaci bane na mata wannan tambayar ba.
Awa kusan guda kenan da zamansu a wajen zahra ga dubi hafsa
"Hafsa qishirwa nakeji,bazan kuma iya shan komaj cikin gidan nan ba"
"To muje waje mana mu samu wani shop ko lemo kisha" kai ta kada
"Ruwanma ya wadatar" ta fada tana miqewa da qyar
"Wash kaina" ta fada sanda ta miqe din
"Lafiya?" Hafsa ta tambayeta,saita dan ya mutsa fuska
"Mtsweww,kaina ke ciwo"
"Dole ai,wannan kukan da kikayi ai ba kadan bane"da haka suka taka zuwa wajen gidan.
A yanzun layin a dinke yake da jama'a,da alama har sun dawo kenan,haka yasa sabuwar qwalla suka zirarowa zahra,yanzu haka abdul nacan kwance,nacan kwance qasan qasa,babu kowa saishi kadai,babu kowa sai halayyarsa da ayyukansa.
"Zahra duka shagunan layin nan a rufe suke" taji hafsat na fada,kai ta gyada tana share hawayen fuskarta
"Eh na gani,amma layin nan kamar layin gidansu rabi'ah ishaq ko?,da kika tana rakoni?"
"Eh tabbas,aiga gidan nasu can ma qarshen layi"
"Yauwa,mu qarasa nasha ruwan a can kawai"
"Ok" hafsat ta fada,kai tsaye suka miqe zuwa gaba,wanda gidan ke jerin gidajen dake jikin gidansi abdulyasar din,tsakaninsu da gidansu abdulyasar din gida biyar ne kacal.
Da sallama suka shiga gidan,wata mace dake duqe bakin fanfo tana wanki ta daga kai tana amsa musu sallamar
"Ku qaraso mana" ta fada tana dagowa daga duqen da tayi.
Gaidata sukayi sannan suka shaida mata su din qawayen rabi'ah ne
"Ayyah,kuma gashi bata dade ta fita ba wallahi"murmushin qarfin hali zahra tayi
"Babu komai,dama ruwa muka shigo zamu sha_ta qarashe maganar ta duqawa kamar wadda zatayi ruku'u saboda yadda kanta keci gaba da sara mata
"To babu damuwa,bari A kawo muku" saita yi gaba daga can qarshen tsakar gidan,ta bude wani fridge dan qarami dake qasan rumfa tana cewa
"Hala daga gidan rasuwar gidan su abdul kuke?" Hafsat ce ta amsa mata
"Eh wallahi" cikin nuna jimami da alhini ta sake cewa sanda take ciro ruwan
"Ai mun tashi da tashin hankali yau,mutuwar matashi yaro,babban abun tausayin ma,yau satinsa biyu cif da kai kudin aure....." Kalma mafi girma da muni data daki zuciya da kunnuwan zahra,kalmar da taji kamar a wani mugun mafarki aka furtata,kafin ta dawo hayyacinta sautin muryar hafsat cike da zallar mamaki ta furta
"Sati biyu da kai kudin aurensa?"amsa musu tayi sanda take rufe fridge din tana dawowa zuwa garesu
"Wallahi Allah,bari kawai....daxun yarinyar da ya kaiwa kudin tazo,abun gwanin ban tausayi,bakiga kukan da take ba,tana faduwa ana dagata,dukkanmu sai data sanyamu qwalla,sai data sake saka hajiyarsa kuka sosai,qarshe kasa zama tayi sai gida aka maidata,kinga keyholder din kai kudin akan window na ma,ni ko amfani da ita bankai ga yi ba" qarashen maganar yazo dai dai da zamewar zahra daga durquson da tayi zuwa zama dabas a qasa
"La haula wala quwwata illa billah" kawai zahran ke fada cikin zuciyarta,bakinta zuwa maqogaronta ya sake bushewa raqayau kamar bata taba kurbar maqwarwa daya ta ruwa ba tunda Allah ya halicceta,tana jin sanda matar ke miqo ruwan amma saita kasa amsa,maimakon karba ma saita miqe tsaye kawai ta nufi qofa,bataga wani sauran amfanin zamanta ba kuma,tana jiyo hafsa na mata godiya gami da sallama.
Tuni ta miqi hanya ba tare dako waiwaye ba,ita kanta hafsat din sai cimmata tayi a hanyar
"Zahra....da kin tsaya ya shamsu ya dawo ya maidamu" kaita girgixa idanunta na sauka kan gungun abokan abdulyasar dake zaune qasan wata rumfa,can ta hango auwal a tsakiyarsu,wani abu ya caki zuciyarta,tsanar auwal din ta kamata,tabbas babu shakka yasan komai,yasan duk abinda ke wakana tunda amininsa ne,dashi aka hada baki,dashi aka rufeta
"Muje kawai hafsa,ma hadu a hanya" a yanayin data ga ta shiga,tasan cewa koda bayani tayi mata babu lallai ta fahinta,don haka taci gaba da binta a baya suna tafe zafin rana na dukansu.
Basuyi nisa ba suka soma jin hirar wasu mata biyu a bayansu
"Kai mutuwa....mutuwa masu gari,babu ruwanta da babba ko yaro,tsoho ko tsohuwa kawai dauka take"
"Hmmm....kedai Allah yasa mu dace,mutuwa ma irin wannan ta abdul ai tafi ratsa jiki da daga hankali,mutuwar saurayi?,sati biyu kacal da kai kudin aure ashe ba za'ayi auren ba,babu ma abu mafi tausayi irin yarinyar daya kaiwa kudin,kamar zata shide wallahi abun tausayi"
"Ai da tausayi,Allah yasa mu cika da imani".
Cak zahran da hafsan duka suka tsaya,a sace zahra ya waiwaya ta dubesu,dukkansu babu wanda tasan fuskarsa a cikinsu,suna tsaye sukazo suka giftasu,da alama ma basu ankara da tsaiwarsu ba,sukayi gaba suna ci gaba da hirarsu.
A zafafe zahra ta soma takawa tana koma zuwa layin da suka baro,hafsa ta cafki hannunta
"Ina zaki?"
"Zanyi magana da auwal" daga haka ta zame hannunta ta koma.
Suna nan inda ta barsu,harda qarin wasu abokan nashi wadanda yakanje dasu lokaci zuwa lokaci,dukkansu tasan fuskarsu sunsan fuskarta.