Sashe 61
Alkibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tayi mamakin yadda yake tafe cikin ruwan,yana riqe da lema yana kare mata ruwan,shi kuma ruwan yana dukansa kamar bai damu bama,hakanan taji ta kasa daurewa,kamar idan tayi shuru bata kyauta ba,cikin sanyin murya tace
"Da ka saka lemar kai a kanka....ni wannan bargon zai qarasa dani ba tare dana jiqe ba"
"Kada ki damu,an koya mana tsaiwa cikin ruwa da rana kona awanni nawan ne ba tare da mun gaji ba....." Kai ta jinjina tana ci gaba da tafiya yana biye da ita.
Suna zuwa bakin sassan hajjan ya zuge lemarsa ya juya abinsa,saita tsinci kanta da cewa
"Na gode" juyowa yayi kawai ya kalleta sannan yayi gaba,sai dataga bacewarsa cikin ruwan dake sauka farfajiyar gidan sannan ta taka ta shige sassan hajjan.
A falo ta tadda tsohuwar tana shan kunun tsamiya,ta rasa qaunarta da kunun tsamiya,saita bita da kallo sanda take sauke bargon daga kanta,can cikin ranta taji tausayin haidar din,daga yadda ya amsata tasan yaji zafi ne,to amma koma meye tafison sai an aiwatar da komai daya kamata sannan,yadda hankalin kowa zaifi kwanciya,ta tar cikin gidansa,an rakata kamar kowacce mace,ko a baya ma data barsu tayi yaqinin ransu babu komai a ciki,babu wannan abun data gani yana yawo yanzu cikin idanuwansu a da din (hmmm to hajja,Allah yasa dai burin naki ya cika na miqa zahra'u dakinta).
Dakinta ta wuce ta canza kaya,ta dawo falo taci abinci,bata jima ba taji bacci na ziyartar idanunta don haka ta wuce dakinta abinta tabar hajja da husna da ilham,wanda suma wani lokaci nan wajenta suke kwana,abba babba ya tsara hakan,saboda yace zahra'un idan ta tafi xa'a bar hajjan ita kadai ne a sassan,kuma ko yanzun ma idan ta tafi makaranta wajen nata babu kowa,shi yasa suka yo qaura suka dawo,dama kuma sunfi son nan din.
*_BAYAN KWANAKI BIYU_*
Kwanaki biyu kenan da dawowarsa,qarfe sha daya saura na safe ya shigo sassan hajjan,a lokacin abba babba abba yusuf da abban tsakiya duka suna falon hajjan,zahra na kitchen tana wanke kwanukan data hada musu breakfast,don tun safe sukazo suna ta lissafi,na haqqin Allah da za'a fitar cikin kudin hajja da ake juya mata,lokacin fiddawa yayi.
Tunda ta gama ta zuba masa nasa a fulasan da ake zuba masa kamar koda yaushe,kwanaki biyu kenan tun randa ruwan saman ya tareta hajjan bata sake bari taje din ba,saidai ta bayar a kai masa kamar yadda ya fada,ita kam zahra nata idanu ne,saboda tasan halin hajjan,katafila ce sarkin aiki,takan kowa take bi idan aikinta ya tashi.
A ladace ya cire takalmansa ya qaraso gabansu ya tsugunna,daya bayan daya ya gaidasu,yaji dadin samunsu a tare,tunda yaje bai samesu a sassansu ba dama
"A kawo maka abincinne?" Hajja ta tambayeshi,tunda ta lura kwana biyu wani shareta yake,tun ranar nan,itakam ko a jikinta,tunda tasan koma meye qarshe shi zaifi kowa mora
"A'ah...zanyi magana idan za'a kawomin din....magaa nakeso muyi dama" abbansa ne ya daga kai ya dubeshi yana ninke takardar daya gama rubutu akai,abba yusuf ne ya amsa
"To Allah yasa lafiya" qasaitaccen murmushin nan nashi na gefan baki yayi sannan yace
"Lafiya lau abba.....cikin yarjewar ubangiji inason satin nan da zamu shiga in sha Allah mu wuce umara,nida hajja da abba na.....da kuma mama" Wani farinciki ne ya bayyana sosai saman fuskar hajja,burinta a duniya kenan ta koma qasa mai tsarki,duk da cewa taje har sau biyu,hajji daya umara daya,amma wajene da babu musulmin da bazaiso ya dawwama ma a can ba,lallai ba shakka haidar din wata kyautar Allah ce cikin iyalinta,soyayyar da yake mata mahaifi da mahaifiyarsa kai dama ahalinsa gaba daya abarso a sameta ce cikin zuciyar kowanne daga cikin dangi,don samun dorewar qaunar juna da danqon zumunta.
Kowanne a parlour din son barka yake gami da sanya masa albarka,tare da yaba wannan namijin qoqarin sa yayi
"naso ace na qara da abban tsakiya da abba yusuf,to amma kudin hannuna sun qare,ba zasu isa ayi komai na mutum biyu ba,amma in sha Allah sune a lissafina na gaba" nunawa sukayi babu komai,su da dan uwan nasu duka abu dayane,sannan suna da yaqinin da yardar Allah shi mai kai kowa ne cikin dangi idan da halin yiwuwar hakan.
Sun dan jima anan suna tattaunawa cike da farinciki,kafin daga bisani suyiwa hajja sallama kowa ya nufi wajen neman kudinsa,sai falon ya rage daga hajjan sai haidar din,sai kuma zahra dake kitcehn tana dora abincin rana kawai don idan ta zauna ta huta gaba daya,inna gaje ciwon qafa ya hanata zuwa aiki tun shekaran jiya.
Kira hajjan ta qwalawa zahra tace ta fito da abincin haidar,ta zata kai masa za'ayi,batayi tunanin yana falon ba don haka ta fito gaba gadi haka abunta,wata straight gown ce a jikinta,wadda tayi mata das a jikinta.
Da kallo ya bita bayan ta gaidashi ta aje masa abincin ta koma,suna hada ido da hajja ya hade rai tsam sannan yace
"Yanzun haka take yawo anan?"
"To uban mutane,sai akayi yaya?ni bama wannan ba,tafiyar nan da zahra'u ya dace ayita,don baka je dakin Allah haka ziqau ba,kabar kyautar da yayi maka a gida ba" kallonta yayi ya soma zuba abincin yau da kanshi ba tare daya nema wani ya zuba masa ba
"Yanzu dai babu kudi hannuna,saidai nan gaba idan Allah yayi" hade ranta tayi sosai
"Eh na sani ai ubana.....ni zan biya mata da kaina,saboda haka a sama mata komai da komai,idanma za'a dage tafiyar sai lokacin data samu to a dage din" baice mata komai ba,dama kuma tasan halinta ba zaya tanka ba,don haka taci gaba da sabgarta kawai,tana ta kiran 'yan uwa daya kamata su sani tana gaya musu batun biya mata umarar,abun mamaki kuma don iya qarfa qarfa irin na hajja sai take hadawa da zahra kan harda ita za'a tafin,shidai yana zaune yana cin abinci yana kuma kallon ikon Allah,zahra kuwa na kitchen bata ma san wainar da ake toyawa ba.
Sai da ya gama cin abincinsa sannan ya miqe ya fice,dole zaiyi maganin hajja,zai kawo qarshen wannan mulkin mallakar nata,zata ga nasa qarfin ikon akan aurensa,don haka tun a motarsa driver na jansa ya kira anty alawiyya.
Bayan sun gama gaisawa tayi masa godiya da addu'ar qaruwar aziqi kan umarar da ya biyawa iyayensu saiyayi mata maganar da ita ta sanya ya kiratan
"Kaya nakeso a hadamin,irin wanda ake hadawa amare a akwati" dariya ce taso kubce mata amma ta danne,don kada tayi dariyar ta jama kanta jagwal,duk da cewa ita ke gaba dashi
"Ohkey.....lefe kenan....kaman na nawa?,kuma akwati nawa?"
"Akwati bakwai is okey,nayi hidima da kudaden hannuna....amma banison kaya low quality please,designers kumadd high quality"
"In sha Allah babu matsala"
"Please su zama ready kafin na dawo"
"To shikenan....babu damuwa" saiya yanke wayar ya aje gefa,ya maida idanunsa kan titunan da suke wucewa.
23/10/2021, 08:50 - 馃憤馃徎馃憤馃徎: 40
Wayar ya sake jawowa,wata number ya sake laluba,wanda suke masa aikin ginin filin da ya siya a nan,yadan jima da siyan filin,tun farkon fara aikinsa ya hada albashinsa ya siya,hakanan da kadan da kadan ake aikin gininsa,yadda zaifi masa sauqi bazai wahala ko ya kashe kudi masu yawa ba lokaci guda,zuwa yanzu ginin yayi nisa qwarai,don abinda ya rage ma sauran abubuwan da ba'a rasa bane,da farko yayi niyyar ma ya kammala gidan ya saida,amma da yayi tunani sai yaga,bashi da mazauni kenan duk sanda yazo ganin gida saidai a cikin gidansu,auren da aka daura masa da zahra yasa ya fasa saidashin kwata kwata,saboda koba zahra ba dama dole zaiyi aure,idan kuma yayi auren zai dawwama zuwa gidansu ya zauna?,dole yana buqatar muhalli.
Da kamfanin yayi magana,ya shaida musu abinda yake da buqata cikin gidan,suka gaya masa kudinsa da zaya bayar,yayi musu alqawarin turawa zuwa qarshen wata,a sannan suna can basu dawo ba kenan a yadda ya lissafa,yana saka ran kuma kafin su dawo din an kammala komai,saiya aje wayarsa yana ci gaba da lissafe lissafensa cikin ransa,zuciyarsa fes,yana jin wata nutsuwa da sukuni suna ratsashi.
******** **** ********
Bai sakewa hajja zancan tafiyar zahran ba,kamar yadda bai amshi kudinta ba,tayi tunanin waskewa yakeson yi,saita matsa da mita da qorafi,sai ranar daya sameta zaune ya miqa mata komai da komai na tafiyar zahran da aka kammala bayan an dage tasu tafiyar da sati daya.
Kwalla ce ta qwacewa hajjan,abinda bai taba zaton gani daga idanunta ba,duka shida zahra dake zaune a gefanta suka zuba mata ido,jikinsu duka yayi sanyi
"Allah yayi maka albarka,ubangiji yaci gaba da gin riqo da hannayenka,Allah ya kula maka da rayuwarka,yadda kake taimakon al'ummar annabi kake kula da iyayenka da 'yan uwanka....Allah yayi maka kyakkyawan sakamako,haidar....kaida zahra Allah shine shaida....kaf cikin jikokina babu wadanda suka shiga raina kamar yaku,hakan ya sanya nan duniya tun kuna da qanana bani da burin daya wuce Allah ya hada kanku kuso juna ku zama miji da mata,sai wani al'amari me daure kai ya soma gudana a tsakaninku,amma hikima ta ubangiji da baya maida addu'ar bawansa,sai gashi ya kawo hadin aurenku ta fuskar dani kaina ban tsammata ba.....haidar....ga zahra nan,a yau zan baka amanarta...ka riqe amanar zahra,kai da ita duka nasan halayenku...hakan ya sanya nake da yaqinin dukkanku kun dace da junanku,zaku gasgata abinda nake fada din,zahra,haidar yayanki ne kuma mijinki,ki bishi ki masa biyayya,ki masa biyayya kamar yadda musulunci ya tanada,Allah ya albarkaci rayuwarku" cikin sanyin jiki dukkansu suka amsa da amin,saita miqawa zahra passport din hannunta
"Zaki tafi umara tare damu,mijinki ya biya miki" kamar a mafarki taji fitar furucin daga bakin hajjan,saita daskare a zaune tana jujjuya passport din,yau itace zata qasa me tsarki ta qarqashin ya haidar din?,mutumin da take masa kallon mara qaunarta,wanda bayason yaga suna farinciki da walwala?,mutumin da take kiranshi da mara ALKIBLA?,mai baudadden hali,wanda sam ALKIBLARSU bata zo daya ba,ashe ta sanadinsa zata je taga ma'aiki?sai qwalla ta cika mata idanu,ta sake matsawa kusa dasu muryarta na rawa saboda farinciki
"Na gode,Allah ya saka da alkhairi,ya qara budi,ubangiji ya biya da jannatulfirdaus" idanunsa ya lumshe yana jin dadin muryarta hade da dadin addu'ar data yi masa ya amsa da
"Amin".
"Da ka saka lemar kai a kanka....ni wannan bargon zai qarasa dani ba tare dana jiqe ba"
"Kada ki damu,an koya mana tsaiwa cikin ruwa da rana kona awanni nawan ne ba tare da mun gaji ba....." Kai ta jinjina tana ci gaba da tafiya yana biye da ita.
Suna zuwa bakin sassan hajjan ya zuge lemarsa ya juya abinsa,saita tsinci kanta da cewa
"Na gode" juyowa yayi kawai ya kalleta sannan yayi gaba,sai dataga bacewarsa cikin ruwan dake sauka farfajiyar gidan sannan ta taka ta shige sassan hajjan.
A falo ta tadda tsohuwar tana shan kunun tsamiya,ta rasa qaunarta da kunun tsamiya,saita bita da kallo sanda take sauke bargon daga kanta,can cikin ranta taji tausayin haidar din,daga yadda ya amsata tasan yaji zafi ne,to amma koma meye tafison sai an aiwatar da komai daya kamata sannan,yadda hankalin kowa zaifi kwanciya,ta tar cikin gidansa,an rakata kamar kowacce mace,ko a baya ma data barsu tayi yaqinin ransu babu komai a ciki,babu wannan abun data gani yana yawo yanzu cikin idanuwansu a da din (hmmm to hajja,Allah yasa dai burin naki ya cika na miqa zahra'u dakinta).
Dakinta ta wuce ta canza kaya,ta dawo falo taci abinci,bata jima ba taji bacci na ziyartar idanunta don haka ta wuce dakinta abinta tabar hajja da husna da ilham,wanda suma wani lokaci nan wajenta suke kwana,abba babba ya tsara hakan,saboda yace zahra'un idan ta tafi xa'a bar hajjan ita kadai ne a sassan,kuma ko yanzun ma idan ta tafi makaranta wajen nata babu kowa,shi yasa suka yo qaura suka dawo,dama kuma sunfi son nan din.
*_BAYAN KWANAKI BIYU_*
Kwanaki biyu kenan da dawowarsa,qarfe sha daya saura na safe ya shigo sassan hajjan,a lokacin abba babba abba yusuf da abban tsakiya duka suna falon hajjan,zahra na kitchen tana wanke kwanukan data hada musu breakfast,don tun safe sukazo suna ta lissafi,na haqqin Allah da za'a fitar cikin kudin hajja da ake juya mata,lokacin fiddawa yayi.
Tunda ta gama ta zuba masa nasa a fulasan da ake zuba masa kamar koda yaushe,kwanaki biyu kenan tun randa ruwan saman ya tareta hajjan bata sake bari taje din ba,saidai ta bayar a kai masa kamar yadda ya fada,ita kam zahra nata idanu ne,saboda tasan halin hajjan,katafila ce sarkin aiki,takan kowa take bi idan aikinta ya tashi.
A ladace ya cire takalmansa ya qaraso gabansu ya tsugunna,daya bayan daya ya gaidasu,yaji dadin samunsu a tare,tunda yaje bai samesu a sassansu ba dama
"A kawo maka abincinne?" Hajja ta tambayeshi,tunda ta lura kwana biyu wani shareta yake,tun ranar nan,itakam ko a jikinta,tunda tasan koma meye qarshe shi zaifi kowa mora
"A'ah...zanyi magana idan za'a kawomin din....magaa nakeso muyi dama" abbansa ne ya daga kai ya dubeshi yana ninke takardar daya gama rubutu akai,abba yusuf ne ya amsa
"To Allah yasa lafiya" qasaitaccen murmushin nan nashi na gefan baki yayi sannan yace
"Lafiya lau abba.....cikin yarjewar ubangiji inason satin nan da zamu shiga in sha Allah mu wuce umara,nida hajja da abba na.....da kuma mama" Wani farinciki ne ya bayyana sosai saman fuskar hajja,burinta a duniya kenan ta koma qasa mai tsarki,duk da cewa taje har sau biyu,hajji daya umara daya,amma wajene da babu musulmin da bazaiso ya dawwama ma a can ba,lallai ba shakka haidar din wata kyautar Allah ce cikin iyalinta,soyayyar da yake mata mahaifi da mahaifiyarsa kai dama ahalinsa gaba daya abarso a sameta ce cikin zuciyar kowanne daga cikin dangi,don samun dorewar qaunar juna da danqon zumunta.
Kowanne a parlour din son barka yake gami da sanya masa albarka,tare da yaba wannan namijin qoqarin sa yayi
"naso ace na qara da abban tsakiya da abba yusuf,to amma kudin hannuna sun qare,ba zasu isa ayi komai na mutum biyu ba,amma in sha Allah sune a lissafina na gaba" nunawa sukayi babu komai,su da dan uwan nasu duka abu dayane,sannan suna da yaqinin da yardar Allah shi mai kai kowa ne cikin dangi idan da halin yiwuwar hakan.
Sun dan jima anan suna tattaunawa cike da farinciki,kafin daga bisani suyiwa hajja sallama kowa ya nufi wajen neman kudinsa,sai falon ya rage daga hajjan sai haidar din,sai kuma zahra dake kitcehn tana dora abincin rana kawai don idan ta zauna ta huta gaba daya,inna gaje ciwon qafa ya hanata zuwa aiki tun shekaran jiya.
Kira hajjan ta qwalawa zahra tace ta fito da abincin haidar,ta zata kai masa za'ayi,batayi tunanin yana falon ba don haka ta fito gaba gadi haka abunta,wata straight gown ce a jikinta,wadda tayi mata das a jikinta.
Da kallo ya bita bayan ta gaidashi ta aje masa abincin ta koma,suna hada ido da hajja ya hade rai tsam sannan yace
"Yanzun haka take yawo anan?"
"To uban mutane,sai akayi yaya?ni bama wannan ba,tafiyar nan da zahra'u ya dace ayita,don baka je dakin Allah haka ziqau ba,kabar kyautar da yayi maka a gida ba" kallonta yayi ya soma zuba abincin yau da kanshi ba tare daya nema wani ya zuba masa ba
"Yanzu dai babu kudi hannuna,saidai nan gaba idan Allah yayi" hade ranta tayi sosai
"Eh na sani ai ubana.....ni zan biya mata da kaina,saboda haka a sama mata komai da komai,idanma za'a dage tafiyar sai lokacin data samu to a dage din" baice mata komai ba,dama kuma tasan halinta ba zaya tanka ba,don haka taci gaba da sabgarta kawai,tana ta kiran 'yan uwa daya kamata su sani tana gaya musu batun biya mata umarar,abun mamaki kuma don iya qarfa qarfa irin na hajja sai take hadawa da zahra kan harda ita za'a tafin,shidai yana zaune yana cin abinci yana kuma kallon ikon Allah,zahra kuwa na kitchen bata ma san wainar da ake toyawa ba.
Sai da ya gama cin abincinsa sannan ya miqe ya fice,dole zaiyi maganin hajja,zai kawo qarshen wannan mulkin mallakar nata,zata ga nasa qarfin ikon akan aurensa,don haka tun a motarsa driver na jansa ya kira anty alawiyya.
Bayan sun gama gaisawa tayi masa godiya da addu'ar qaruwar aziqi kan umarar da ya biyawa iyayensu saiyayi mata maganar da ita ta sanya ya kiratan
"Kaya nakeso a hadamin,irin wanda ake hadawa amare a akwati" dariya ce taso kubce mata amma ta danne,don kada tayi dariyar ta jama kanta jagwal,duk da cewa ita ke gaba dashi
"Ohkey.....lefe kenan....kaman na nawa?,kuma akwati nawa?"
"Akwati bakwai is okey,nayi hidima da kudaden hannuna....amma banison kaya low quality please,designers kumadd high quality"
"In sha Allah babu matsala"
"Please su zama ready kafin na dawo"
"To shikenan....babu damuwa" saiya yanke wayar ya aje gefa,ya maida idanunsa kan titunan da suke wucewa.
23/10/2021, 08:50 - 馃憤馃徎馃憤馃徎: 40
Wayar ya sake jawowa,wata number ya sake laluba,wanda suke masa aikin ginin filin da ya siya a nan,yadan jima da siyan filin,tun farkon fara aikinsa ya hada albashinsa ya siya,hakanan da kadan da kadan ake aikin gininsa,yadda zaifi masa sauqi bazai wahala ko ya kashe kudi masu yawa ba lokaci guda,zuwa yanzu ginin yayi nisa qwarai,don abinda ya rage ma sauran abubuwan da ba'a rasa bane,da farko yayi niyyar ma ya kammala gidan ya saida,amma da yayi tunani sai yaga,bashi da mazauni kenan duk sanda yazo ganin gida saidai a cikin gidansu,auren da aka daura masa da zahra yasa ya fasa saidashin kwata kwata,saboda koba zahra ba dama dole zaiyi aure,idan kuma yayi auren zai dawwama zuwa gidansu ya zauna?,dole yana buqatar muhalli.
Da kamfanin yayi magana,ya shaida musu abinda yake da buqata cikin gidan,suka gaya masa kudinsa da zaya bayar,yayi musu alqawarin turawa zuwa qarshen wata,a sannan suna can basu dawo ba kenan a yadda ya lissafa,yana saka ran kuma kafin su dawo din an kammala komai,saiya aje wayarsa yana ci gaba da lissafe lissafensa cikin ransa,zuciyarsa fes,yana jin wata nutsuwa da sukuni suna ratsashi.
******** **** ********
Bai sakewa hajja zancan tafiyar zahran ba,kamar yadda bai amshi kudinta ba,tayi tunanin waskewa yakeson yi,saita matsa da mita da qorafi,sai ranar daya sameta zaune ya miqa mata komai da komai na tafiyar zahran da aka kammala bayan an dage tasu tafiyar da sati daya.
Kwalla ce ta qwacewa hajjan,abinda bai taba zaton gani daga idanunta ba,duka shida zahra dake zaune a gefanta suka zuba mata ido,jikinsu duka yayi sanyi
"Allah yayi maka albarka,ubangiji yaci gaba da gin riqo da hannayenka,Allah ya kula maka da rayuwarka,yadda kake taimakon al'ummar annabi kake kula da iyayenka da 'yan uwanka....Allah yayi maka kyakkyawan sakamako,haidar....kaida zahra Allah shine shaida....kaf cikin jikokina babu wadanda suka shiga raina kamar yaku,hakan ya sanya nan duniya tun kuna da qanana bani da burin daya wuce Allah ya hada kanku kuso juna ku zama miji da mata,sai wani al'amari me daure kai ya soma gudana a tsakaninku,amma hikima ta ubangiji da baya maida addu'ar bawansa,sai gashi ya kawo hadin aurenku ta fuskar dani kaina ban tsammata ba.....haidar....ga zahra nan,a yau zan baka amanarta...ka riqe amanar zahra,kai da ita duka nasan halayenku...hakan ya sanya nake da yaqinin dukkanku kun dace da junanku,zaku gasgata abinda nake fada din,zahra,haidar yayanki ne kuma mijinki,ki bishi ki masa biyayya,ki masa biyayya kamar yadda musulunci ya tanada,Allah ya albarkaci rayuwarku" cikin sanyin jiki dukkansu suka amsa da amin,saita miqawa zahra passport din hannunta
"Zaki tafi umara tare damu,mijinki ya biya miki" kamar a mafarki taji fitar furucin daga bakin hajjan,saita daskare a zaune tana jujjuya passport din,yau itace zata qasa me tsarki ta qarqashin ya haidar din?,mutumin da take masa kallon mara qaunarta,wanda bayason yaga suna farinciki da walwala?,mutumin da take kiranshi da mara ALKIBLA?,mai baudadden hali,wanda sam ALKIBLARSU bata zo daya ba,ashe ta sanadinsa zata je taga ma'aiki?sai qwalla ta cika mata idanu,ta sake matsawa kusa dasu muryarta na rawa saboda farinciki
"Na gode,Allah ya saka da alkhairi,ya qara budi,ubangiji ya biya da jannatulfirdaus" idanunsa ya lumshe yana jin dadin muryarta hade da dadin addu'ar data yi masa ya amsa da
"Amin".