Sashe 67
Alkibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Qarar da wayarsa tayi ita ta katse masa tunaninsa,sai daya miqa hannu sosai sannan ya iya lalubota,saboda fadawa da tayi gefan gado,yana duba sunan yaga hajja ce,saiya sauke zahran yaja mata bargo ya lullube mata jikinta,ya zura qafafunsa qasan gadon sannan ya amsa wayar
"Wai ina kuka tsaya ne haidar?,baka duba lokacine?,kusan awa uku?,hafsa tace a hanya kuka sauketa,kuna ina ne?" Ya bude baki zaiyi magana sai yaji muryar tasa a dakushe take,don haka ya danyi gyaran murya
"Banason qaniya....ka bude baki kayimin magana"
"Muna gidanmu.....,gobe ko jibi zamu shigo mu sake yi muku ban gajiya"
"Gidanku?,wanne gidan naku"
"Gida na na gaida gida dubu" salati hajja ta saki tana sallallami,jin haka sai kawai ya datse wayar,yama kasheta gaba daya,ya tashi ya lalubo wayar zahran itama ya kasheta,ya hadasu gaba daya ya watsa cikin sif sannan ya wuce bandaki yana murmushi qasan ransa,yasan za'asha daru da rigima,tana can qila ta tadawa kowa hankali,shikam bazai dauki wannan gantali da aure da hajjan keta yi musu ba,ana masa wasa da hankali kamar zahran bata gama zama mallakinsa ba.
Kamar kuwa yadda yace din,kwanansu uku cikin gidan su kadai,babu abinda suke banda morewa amarcinsu,gami da sake dasawa juna sabo da shaquwa mai qarfi a tsakaninsu,cikin kwanakin zahran tayi mugun sabo da soyayyarsa,wadda ya dinga koyar da ita salo salo cikin dabara da tsabar qwarewa,sau tari takan saki baki tana tambayar kanta
"Da gaske ya haidar ne wanann?" Duk inda ta motsa yana maqale da ita,tare suke komai,girki gyaran gidan,wanke wanke,kai hatta ma wanka bai bari ta shiga ita daya,idan ko ta sake tayi ita kadai to tayi aikin banza,don sai ta sake,suna aikin yana tsokanarta,wasan guje guje sam batasan a inda ya koya ba,ya qware a sosai a tsokana,idan mamaki ya cikata ta saki baki da ido tana kallonsa,saiya hure mata ido da iskar bakinsa,wani lokacin kuma saiya hade bakinsu waje guda,yace bari ya rage mata mamakin da takeyi,saiya tsotsi lips dinta iya son ranshi sannan ya saketa,ya dubeta yace
"Kairukum kairukum li ahlihi,wa'ana kairukum li ahly. 禺賷乇賰賲 禺賷乇賰賲 賱丌賴賱賴 賵丕賳丕 禺賷乇賰賲 賱丌賴賱賷,annabi yace mafi alkhairinku shine mafi alkhairinku ga iyalansa,sai annabi da kansa yace nine mafi alkhairinku ga iyalina,yana taya iyalansa dukka ayyukan gida da kika sani....ni din waye da bazanyi koyi da wanda akayi duniya da lahira saboda shi ba?" Maganganunsa sunyi matuqar burgeta ba kadan ba,da gaske ne duk wanda ya hukunta wani mutum bisa wai wai ko kuma kallonsa da yake daga nesa ba tare da ya mu'amalanceshi ba,zai aikata babban kuskure,ashe kalar abinda umminta keta mata kwadayi kenan?,lallai uwa uwa ce,a kowanne hali makomar rayuwar ahalinta na nan cikin ranta,komai runtsi komai wuya,Aliyyu miji ne 蓷aya da 蓷aya,mai tarin nagartar da kaso mafi yawa daga cikin mazan yanzu suka rasa irinta
(Idan baki samu ba,saiki roqi Allah ya gyara miki dabi'ar naki mijin,ya zama me koyi da sunnar ma'aiki,idan kuma kin samu,saiki godewa Allah,kuma kada kiyi wasa da damarki,koki wofantar da baiwar da Allah yayi miki,idan budurwa ce ke....kina da sauran dama,ki fidda so ko burgewar dukkan wani qyale qyalen duniya daga ranki,ki tsayawa sallar dare,kiyita gayawa ubangiji da roqarsa ya zaba miki miji na gari,ba mai arziqi ko kyau ba,miji na gari ya wuce dukkan wani irin nau'in miji daya mallaki dukiya kyau mulki ko sarauta,miji na gari shine abu mafi tsada da daraja cikin rayuwar diya mace kaf!!!,da zarar kin dace dashi,tofa matar du wani mai mulki kudi kyau ko sarauta saidai ta biyoki a baya,matuqar itama ba katari tayi da irin naki mijin ba,ubangiji ya wadata qannenmu 'yan uwanmu da 'ya'yanmu da nagartattun maza馃げ馃徑馃げ馃徑馃げ馃徑,dama daukacin matan musulmi gaba daya).
Cikon kwana na hudun suka shirya wajen sha biyu saura suka nufi gida,duk a kunyace take,saboda batasan da wacce fuska zata kalli jama'ar gidan nasu ba,musamman mama da umminta,har gwara hajja an saba gauraya.
Sai da suka shiga kowanne sashe suka gaidasu sannan suka wuce sassan hajja,ga mamakinta ba wanda ya tsokanesu ko ya tada maganar,bare ya nuna yasan me ya faru,suna sallama sukaci karo da akwatuna masu azabar kyau blueblack guda takwas cas,kowacce shaqe da kaya a cikinta,wasu daga cikin 'yan uwan hajja ne suka gama kalla,da alama tafiya zasuyi ma,don har sun miqe.
Ango da amarya suka kirayi sunansu dashi,itadai ta murmusa ta gaidasu cikin kunya,yayin da aliyyu ya fuske cikin salon miskilancin nan nasa,sai zahran ta dinga satar kallonsa ta gefan ido,ya zama aliyyun nan sak dake basu tsoro cikin gidan,suna hada ido ya kashe mata idonsa daya,ya mata nuni data rage kallonsa,yana taba zuciyarsa,saita janye idanun nata tana sakin murmushi,dai dai nan suka hada ido da hajja wadda ta gama sallama da baqinta suka fice
"Sannunku marasa kunya feqaqqu....bari na fara da babban rasa kunya beran tankan.....kaga....hade girar gefe da gefanka ba zasu tsoratani ko su hanani cima mutunci ba.....da zaka daukemin yarinya ka kaita gidanka da kanka anyi biki ne?,ko ce maka akayi ma ciniki ya fada ne?,ance maka ta gama zama taka?,aro ne na shekara daya shine zaka zaqewa mutane....." Tana tsaka da bambaminta ya miqe yana cusa wayarsa aljihun wandonsa
"Don Allah ki hutama ranki.....don ciniki ya dade da fadawa....ki godewa Allah da bata shigo tana miki amai bama....idan sadakinne ya miki kadan ki fadi dame kikeso a qara yawanshi" baki ta kama tana zare ido,yana ganin haka yasan ya soma maganin rigimar hajjan,saiya juya ya fara takawa zai fita daga falon,ba tare daya ma kalli kayan lefen da yasan shi ya bayar aka hadashi ba,duk da yaga akwati daya ta dadu akwai,har zai fita saiya waiwayo,xahra nata danne dariyarta,hajja na tsaye inda take tana binsa da kallo
"Kuma ga amanar matata nan....quda idan ya tabata saina ciki tara"
"Haidar....aliyyu,dani kake maganar" ta fada cikin daga murya sanda yake ficewa daga falon,cikin ransa tana qyaqyacewa da dariyar abinda ya yiwa hajja.
Guri ta samu tana zama tana hade ranta tsaf,duk da cewa zallar farinciki ne qasan ranta me tarin yawa,already sun riga sun gama magana dasu abba babba kan abarsu tunda har sun hada kansu sunma wuce gidansu,shi dama taron biki al'adace kawai,tunda an qulla auren yadda musulunci yace,kuma jama'a sun shaida shikenan
"Gafara kika tsareni da ido mara kunya....ja'ira kamar ba kece nan kamar zaki mutu ba saboda mun aura miki shi,ashe lambu lambu kikayi,qiris kike jira" wannan karon dariyarta kubcewa tayi,sai kuma tayi saurin mazewa
"To tunda nafi qarfina aina haqura na zauna ko?,badai za'a ce banyi biyayya ba" murmushi ne ya qwacewa hajjan itama,tasa hannu tana daga kayan,don ita duk yadda ake kallon lefan bata samu gani ba saboda gajiyar tafiya da take tare da ita,sai yanzu tadan samu ta warware.
Zahra dai bata sanya hannu ba har hajjan ta gama kalla tana daga gefe a zaune,har saida hajjan da kanta tace ta matso ta gani mana,saita girgiza kai alamun a'ah,hakan saiya burge hajjan,duk da cewa an riga da an zama daya,amma har yau akwai abubuwan da zahran ke kunyar yinsu,ba kamar 'yammatan yanzun ba,da wata ma randa za'a kawo lefan tana gidansu,masu kawowa ko qofar gida basa gama kaiwa take tsallen albarka ta fito aci gaba da gani da ita,tana gani tana comment,tana hanawa a tattaba mata wasu abubuwan,Allah ya kyauta.
*_BAYAN KWANAKI BIYU_*
Walima gagaruma haidar din ya shirya a sabon gidan nasu,ranar walimar aka taho mata da akwatunan lefanta,saiya zamana kamar itace a madadin yinin biki,sosai aka ci aka sha,aka gabatar da wa'azi da nasihohi ga mata kan zamantakewar auratayya,wadda ta ratsa zukatan mata da dama,dangi sosai suka halatta,gidan yayi cikar kwari,saidai anyi taro lafiya an kuma watse lafiya.
Rayuwa suka ci gaba da gudanarwa mai cike da tsantsar soyayya da qauna ta kwatance,idanu ko wanxuwar wani a waje baya hanasu nunawa junansu zallar son da sukewa juna,mutane da dama na mamakin haidar din,saboda kowa ya sanshi da miskilancinsa ya sanshi,sai gashi lokaci daya zahra ta sukurkutashi.
Tako wanne fanni yana jin zahran ta cancanci ayi mata kowanne iri so,don dan xamansu da 'yan satittika yasa ya gama fahimtar wacce irin macace ita,ta dauki dukka halayen umminta wajen biyayya wa miji da iya kula dashi,wani irin salo da yake da tabbacin wasunsu ta samosu ne daga wajen hajja,wanda sau tari akwai lokuttan da zai samesu suna hira da ita,tana bata labarin yadda mata ada ke biyayyawa miji ba irin matan yanzu ba.
8:30 pm
A nutse take kai kawo tsakanin kitchen da parlour tana shirya masa abinci,duk inda ta gifta idanunshi yana kanta,shigar da tayin ta dauki hankalinsa matuqa da gaske,duk sanda xata gifta saita bar masa qamshinta,bai taba zaton mata nada son turare haka ba sai da zahran ta kasance matarsa.
Plates ne na qarshe data ajjiye,sai itama ta samu waje tana niyyar xama,hannunsa ya miqa mata yana lumshe ido,ba bata lokaci ta saka hannu nata cikin nasa,hakan ya bashi damar jawota jikinsa,yayi mata mazauni saman cinyarsa,hannayensa ya sanya dukka yana yawo dasu saman jikinta,bata hanashi ba,saboda tasan abinda yafiso kenan,saima ta kwantar da kan nata saman kafadarshi,lungu da saqo na jikinta yake bi yana sansana,tsahon wani lokaci sannan ta kira sunanshe cikin wata lallausar murya
"Hubby na...."
"Makaranta fa....exam ta kusa" shuru ne ya biyo baya,har sai daya kammala abinda ya soma din,saiya dubeta da lumsassun idanunsa da suka jirkice suka qara qanqancewa
"Bana jin xan qyaleki ke kadai xahraty.....zamu tsara komai mu fuskanci komai tare,zamuyi karatun jarrabawa tare,zan kaiki ki dinga zanawa muna dawowa gida tare....nasararki nasara tace,amma da zarar kin kammala,zamu koma abuja,zan koma bakin aikina,yanzun hutun aikin da mukajeyi nake mora,sai kuma yazomin a daidai,Allah ya sanyawa hutun albarka....na mallaki xahrata a cikin sa,ta xama haidar....haidar ya zama zahransa" murmushi tayi,ta juyo gareshi,ta saka hannayenta duka biyun ta saqalo wuyansa,fuskarta dab da tashi
"Na gode sosai da wannan sadaukarwa daka yimin....ina fata ni da kai zamu dawwama a haka,na gode sosai" ta qarasa fada tana hade fuskarsu waje daya,sai kuwa ya sake kai mata cafka,cikin sauri ta zame tana cewa
"Abinci yallabai.....ayimin afuwa a fara cin abinci" ta fada tana saluting nashi kamar yadda sukewa manyansu,idanunsa ya lumshe a kanta sannan ya budesu yana fidda murmushi,yana so tana kuma burgeshi duk sanda ta tsaya gabanshi haka ta qame tayi saluting nashi,bai taba ganin kyau ko burgewa a irin wannan gaisuwar ba sai da zahranshi ta fara yi masa irinta,shima maida mata yayi yana murmushi,har ta zauna bai dauke idanunsa daga kanta ba.
"Wai ina kuka tsaya ne haidar?,baka duba lokacine?,kusan awa uku?,hafsa tace a hanya kuka sauketa,kuna ina ne?" Ya bude baki zaiyi magana sai yaji muryar tasa a dakushe take,don haka ya danyi gyaran murya
"Banason qaniya....ka bude baki kayimin magana"
"Muna gidanmu.....,gobe ko jibi zamu shigo mu sake yi muku ban gajiya"
"Gidanku?,wanne gidan naku"
"Gida na na gaida gida dubu" salati hajja ta saki tana sallallami,jin haka sai kawai ya datse wayar,yama kasheta gaba daya,ya tashi ya lalubo wayar zahran itama ya kasheta,ya hadasu gaba daya ya watsa cikin sif sannan ya wuce bandaki yana murmushi qasan ransa,yasan za'asha daru da rigima,tana can qila ta tadawa kowa hankali,shikam bazai dauki wannan gantali da aure da hajjan keta yi musu ba,ana masa wasa da hankali kamar zahran bata gama zama mallakinsa ba.
Kamar kuwa yadda yace din,kwanansu uku cikin gidan su kadai,babu abinda suke banda morewa amarcinsu,gami da sake dasawa juna sabo da shaquwa mai qarfi a tsakaninsu,cikin kwanakin zahran tayi mugun sabo da soyayyarsa,wadda ya dinga koyar da ita salo salo cikin dabara da tsabar qwarewa,sau tari takan saki baki tana tambayar kanta
"Da gaske ya haidar ne wanann?" Duk inda ta motsa yana maqale da ita,tare suke komai,girki gyaran gidan,wanke wanke,kai hatta ma wanka bai bari ta shiga ita daya,idan ko ta sake tayi ita kadai to tayi aikin banza,don sai ta sake,suna aikin yana tsokanarta,wasan guje guje sam batasan a inda ya koya ba,ya qware a sosai a tsokana,idan mamaki ya cikata ta saki baki da ido tana kallonsa,saiya hure mata ido da iskar bakinsa,wani lokacin kuma saiya hade bakinsu waje guda,yace bari ya rage mata mamakin da takeyi,saiya tsotsi lips dinta iya son ranshi sannan ya saketa,ya dubeta yace
"Kairukum kairukum li ahlihi,wa'ana kairukum li ahly. 禺賷乇賰賲 禺賷乇賰賲 賱丌賴賱賴 賵丕賳丕 禺賷乇賰賲 賱丌賴賱賷,annabi yace mafi alkhairinku shine mafi alkhairinku ga iyalansa,sai annabi da kansa yace nine mafi alkhairinku ga iyalina,yana taya iyalansa dukka ayyukan gida da kika sani....ni din waye da bazanyi koyi da wanda akayi duniya da lahira saboda shi ba?" Maganganunsa sunyi matuqar burgeta ba kadan ba,da gaske ne duk wanda ya hukunta wani mutum bisa wai wai ko kuma kallonsa da yake daga nesa ba tare da ya mu'amalanceshi ba,zai aikata babban kuskure,ashe kalar abinda umminta keta mata kwadayi kenan?,lallai uwa uwa ce,a kowanne hali makomar rayuwar ahalinta na nan cikin ranta,komai runtsi komai wuya,Aliyyu miji ne 蓷aya da 蓷aya,mai tarin nagartar da kaso mafi yawa daga cikin mazan yanzu suka rasa irinta
(Idan baki samu ba,saiki roqi Allah ya gyara miki dabi'ar naki mijin,ya zama me koyi da sunnar ma'aiki,idan kuma kin samu,saiki godewa Allah,kuma kada kiyi wasa da damarki,koki wofantar da baiwar da Allah yayi miki,idan budurwa ce ke....kina da sauran dama,ki fidda so ko burgewar dukkan wani qyale qyalen duniya daga ranki,ki tsayawa sallar dare,kiyita gayawa ubangiji da roqarsa ya zaba miki miji na gari,ba mai arziqi ko kyau ba,miji na gari ya wuce dukkan wani irin nau'in miji daya mallaki dukiya kyau mulki ko sarauta,miji na gari shine abu mafi tsada da daraja cikin rayuwar diya mace kaf!!!,da zarar kin dace dashi,tofa matar du wani mai mulki kudi kyau ko sarauta saidai ta biyoki a baya,matuqar itama ba katari tayi da irin naki mijin ba,ubangiji ya wadata qannenmu 'yan uwanmu da 'ya'yanmu da nagartattun maza馃げ馃徑馃げ馃徑馃げ馃徑,dama daukacin matan musulmi gaba daya).
Cikon kwana na hudun suka shirya wajen sha biyu saura suka nufi gida,duk a kunyace take,saboda batasan da wacce fuska zata kalli jama'ar gidan nasu ba,musamman mama da umminta,har gwara hajja an saba gauraya.
Sai da suka shiga kowanne sashe suka gaidasu sannan suka wuce sassan hajja,ga mamakinta ba wanda ya tsokanesu ko ya tada maganar,bare ya nuna yasan me ya faru,suna sallama sukaci karo da akwatuna masu azabar kyau blueblack guda takwas cas,kowacce shaqe da kaya a cikinta,wasu daga cikin 'yan uwan hajja ne suka gama kalla,da alama tafiya zasuyi ma,don har sun miqe.
Ango da amarya suka kirayi sunansu dashi,itadai ta murmusa ta gaidasu cikin kunya,yayin da aliyyu ya fuske cikin salon miskilancin nan nasa,sai zahran ta dinga satar kallonsa ta gefan ido,ya zama aliyyun nan sak dake basu tsoro cikin gidan,suna hada ido ya kashe mata idonsa daya,ya mata nuni data rage kallonsa,yana taba zuciyarsa,saita janye idanun nata tana sakin murmushi,dai dai nan suka hada ido da hajja wadda ta gama sallama da baqinta suka fice
"Sannunku marasa kunya feqaqqu....bari na fara da babban rasa kunya beran tankan.....kaga....hade girar gefe da gefanka ba zasu tsoratani ko su hanani cima mutunci ba.....da zaka daukemin yarinya ka kaita gidanka da kanka anyi biki ne?,ko ce maka akayi ma ciniki ya fada ne?,ance maka ta gama zama taka?,aro ne na shekara daya shine zaka zaqewa mutane....." Tana tsaka da bambaminta ya miqe yana cusa wayarsa aljihun wandonsa
"Don Allah ki hutama ranki.....don ciniki ya dade da fadawa....ki godewa Allah da bata shigo tana miki amai bama....idan sadakinne ya miki kadan ki fadi dame kikeso a qara yawanshi" baki ta kama tana zare ido,yana ganin haka yasan ya soma maganin rigimar hajjan,saiya juya ya fara takawa zai fita daga falon,ba tare daya ma kalli kayan lefen da yasan shi ya bayar aka hadashi ba,duk da yaga akwati daya ta dadu akwai,har zai fita saiya waiwayo,xahra nata danne dariyarta,hajja na tsaye inda take tana binsa da kallo
"Kuma ga amanar matata nan....quda idan ya tabata saina ciki tara"
"Haidar....aliyyu,dani kake maganar" ta fada cikin daga murya sanda yake ficewa daga falon,cikin ransa tana qyaqyacewa da dariyar abinda ya yiwa hajja.
Guri ta samu tana zama tana hade ranta tsaf,duk da cewa zallar farinciki ne qasan ranta me tarin yawa,already sun riga sun gama magana dasu abba babba kan abarsu tunda har sun hada kansu sunma wuce gidansu,shi dama taron biki al'adace kawai,tunda an qulla auren yadda musulunci yace,kuma jama'a sun shaida shikenan
"Gafara kika tsareni da ido mara kunya....ja'ira kamar ba kece nan kamar zaki mutu ba saboda mun aura miki shi,ashe lambu lambu kikayi,qiris kike jira" wannan karon dariyarta kubcewa tayi,sai kuma tayi saurin mazewa
"To tunda nafi qarfina aina haqura na zauna ko?,badai za'a ce banyi biyayya ba" murmushi ne ya qwacewa hajjan itama,tasa hannu tana daga kayan,don ita duk yadda ake kallon lefan bata samu gani ba saboda gajiyar tafiya da take tare da ita,sai yanzu tadan samu ta warware.
Zahra dai bata sanya hannu ba har hajjan ta gama kalla tana daga gefe a zaune,har saida hajjan da kanta tace ta matso ta gani mana,saita girgiza kai alamun a'ah,hakan saiya burge hajjan,duk da cewa an riga da an zama daya,amma har yau akwai abubuwan da zahran ke kunyar yinsu,ba kamar 'yammatan yanzun ba,da wata ma randa za'a kawo lefan tana gidansu,masu kawowa ko qofar gida basa gama kaiwa take tsallen albarka ta fito aci gaba da gani da ita,tana gani tana comment,tana hanawa a tattaba mata wasu abubuwan,Allah ya kyauta.
*_BAYAN KWANAKI BIYU_*
Walima gagaruma haidar din ya shirya a sabon gidan nasu,ranar walimar aka taho mata da akwatunan lefanta,saiya zamana kamar itace a madadin yinin biki,sosai aka ci aka sha,aka gabatar da wa'azi da nasihohi ga mata kan zamantakewar auratayya,wadda ta ratsa zukatan mata da dama,dangi sosai suka halatta,gidan yayi cikar kwari,saidai anyi taro lafiya an kuma watse lafiya.
Rayuwa suka ci gaba da gudanarwa mai cike da tsantsar soyayya da qauna ta kwatance,idanu ko wanxuwar wani a waje baya hanasu nunawa junansu zallar son da sukewa juna,mutane da dama na mamakin haidar din,saboda kowa ya sanshi da miskilancinsa ya sanshi,sai gashi lokaci daya zahra ta sukurkutashi.
Tako wanne fanni yana jin zahran ta cancanci ayi mata kowanne iri so,don dan xamansu da 'yan satittika yasa ya gama fahimtar wacce irin macace ita,ta dauki dukka halayen umminta wajen biyayya wa miji da iya kula dashi,wani irin salo da yake da tabbacin wasunsu ta samosu ne daga wajen hajja,wanda sau tari akwai lokuttan da zai samesu suna hira da ita,tana bata labarin yadda mata ada ke biyayyawa miji ba irin matan yanzu ba.
8:30 pm
A nutse take kai kawo tsakanin kitchen da parlour tana shirya masa abinci,duk inda ta gifta idanunshi yana kanta,shigar da tayin ta dauki hankalinsa matuqa da gaske,duk sanda xata gifta saita bar masa qamshinta,bai taba zaton mata nada son turare haka ba sai da zahran ta kasance matarsa.
Plates ne na qarshe data ajjiye,sai itama ta samu waje tana niyyar xama,hannunsa ya miqa mata yana lumshe ido,ba bata lokaci ta saka hannu nata cikin nasa,hakan ya bashi damar jawota jikinsa,yayi mata mazauni saman cinyarsa,hannayensa ya sanya dukka yana yawo dasu saman jikinta,bata hanashi ba,saboda tasan abinda yafiso kenan,saima ta kwantar da kan nata saman kafadarshi,lungu da saqo na jikinta yake bi yana sansana,tsahon wani lokaci sannan ta kira sunanshe cikin wata lallausar murya
"Hubby na...."
"Makaranta fa....exam ta kusa" shuru ne ya biyo baya,har sai daya kammala abinda ya soma din,saiya dubeta da lumsassun idanunsa da suka jirkice suka qara qanqancewa
"Bana jin xan qyaleki ke kadai xahraty.....zamu tsara komai mu fuskanci komai tare,zamuyi karatun jarrabawa tare,zan kaiki ki dinga zanawa muna dawowa gida tare....nasararki nasara tace,amma da zarar kin kammala,zamu koma abuja,zan koma bakin aikina,yanzun hutun aikin da mukajeyi nake mora,sai kuma yazomin a daidai,Allah ya sanyawa hutun albarka....na mallaki xahrata a cikin sa,ta xama haidar....haidar ya zama zahransa" murmushi tayi,ta juyo gareshi,ta saka hannayenta duka biyun ta saqalo wuyansa,fuskarta dab da tashi
"Na gode sosai da wannan sadaukarwa daka yimin....ina fata ni da kai zamu dawwama a haka,na gode sosai" ta qarasa fada tana hade fuskarsu waje daya,sai kuwa ya sake kai mata cafka,cikin sauri ta zame tana cewa
"Abinci yallabai.....ayimin afuwa a fara cin abinci" ta fada tana saluting nashi kamar yadda sukewa manyansu,idanunsa ya lumshe a kanta sannan ya budesu yana fidda murmushi,yana so tana kuma burgeshi duk sanda ta tsaya gabanshi haka ta qame tayi saluting nashi,bai taba ganin kyau ko burgewa a irin wannan gaisuwar ba sai da zahranshi ta fara yi masa irinta,shima maida mata yayi yana murmushi,har ta zauna bai dauke idanunsa daga kanta ba.