Sashe 10
Alkibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hafsa ce ta shigo tana dariya abunta riqe da hijabi tana qoqarin sawa,da alama daga waje ta baro abunda ya bata dariyar,sam bata lura da yanayin da innawuro ke ciki ba sai dataji tana kiran sunanta da wata iriyar shaqaqqiyar murya tana yafitota da hannu.
Qarasowa tayi tana dubanta,ba wanda ya iya magana cikinsu sai wayar da zahra ta miqa mata cikin rawar murya tana cewa
"Dubamin don Allah.....dai dai idanuna suke ganemin?" Hannu tasa ta karbi wayar,hoto daya tak ta kalla saita koma saman qafafunta ta zauna itama tana ci gaba da kallon hotonan cikin matuqar mamaki da sanyin jiki,kalamanta a sanyaye qwarai tace
"Nura ne zahra,nuraddeen dinki fa" rasa abu na gaba daya kamata tayi tayi,sai kawai tasa dukka tafin hannunta biyu ta rufe fuskarta dasu kamar wadda bata da muradin ganin duk wani haske dake cikin duniya,tana jin kamar ana yamutsa qwaqwalwarta,daidai sanda salma ta shigo,da sauri hafsat tace
"Yauwa,zo kigani don Allah,zoki tayani gani" da hanzari salman ta qaraso tana amsar wayar daga hannun hafsat.
Wani ashar salman ta dura,da yake itadin batakai haqurin hafsat ba,ta lalubi waje ta zauna tana cewa
"Meke shurin faruwa kenan zahra?laaa,kinga ana goge hotunan daga status.....sunyi disappearing gaba daya"ta fada tana kallon hafsat tare da nuna mata wayar
"Tabbas gogesu akayi,don ba'afi minti goma da dorasu ba,bajci ace har lokacin saukarsu yayi ba,me nuraddeen ke nufi?" Tambayar da bata da amsarta data cilla mata ita ta sanyata sakin wani irin kuka me ciwo,kukan daya daga hankalinsu gaba daya,lokacinne yasira itama ta sako kai,cikin yanayi na tsoro ta isa wajensu tana tambayarsu abinda ke faruwa,basu kai ga bata amsa ba kira ya shigo wayar zahran,duk da bata duba tasan me kiran,salma cikin fushi tace
"Bari na daga naji dan gidan marasa mutuncin me zaice?"kai hafsa da yasira wadda batasan ma ainihin meke faruwa ba suka daga mata,ta daga wayar ta sakata a handfree tayi shuru ba tare data ce komai ba,muryar nuradden ta bayyana
"Dear.....don Allah karki hukunci da abinda bakisan ainihin menene ba,ki bani dama inyi miki bayani pls"
"Ai karka damu,saqone ka bayar ya kuma iske inda kakeso ya iske,yo meye kuma wani abun damuwa a ciki?,kaci gaba da shagalinka kawai,amma ka sani,indai da haqqin zahra a wuyanka Allah saiya mata sakayya"
"Ki tsaya kiji don Allah,wacece?,hafsat ce ko yusra?"
"Ban sani ba dan gaba da rainin hankali,karka sake kiran wannan number" qit daga haka ta katse wayar,wanda kafin ta kuma cewa komai wani kiran ya sake biyo baya,haka suka sanya wayar gaba kowa ya rasa abun tabukawa,yanata faman kira ba qaqqautawa kamar yadda zahra ke kuka itama babu qaqqautawa,yasira ce ta karbi wayar daga qarshe bayan sun zayyana mata abinda ke faruwa ta kasheta gaba daya,har cikin zuciyarta tana jin wani irin suya da bacin rai,wannan wacce iriyar yaudara ce haka kai tsaye ta rashin mutunci da cin fuska,yana sane ma yayi posting hotunan a status dinsa?,abinda yafi tsaya musu a rai kenan.
Su hudun gaba daya suka hadu suna bata baki,harda nadiya data shigo daga qarshe gami da maimaita zancan cike da mamaki,don dukkansu bama su ba kusan kowa yasan da zaman nuraddeen a matsayin wanda zahra inna wuro ta tsaids zata aura,abun yazo musu matuqa a ba zata.
Ita kadai tasan yanayin data tsinci kanta da zuciyarta a ciki,wani yanayi da tun tasowarta bata taba jin irinsa ba saiyau,jin lamarin take kamar a mafarki,wai ita?,nuradden?,wanne irin abu haka tayi masa dafa cancanci irin wannan yaudarar mai ciwo?,har yana da bakin cewa ta saurareshi?,ta jima cikin wannan rudun,daga qarshe taji babu abinda take da buqata illa kadaicewa tayi kukanta ita kadai ko hakan zai sa ta samu gurbin da zata zuqi numfashi yakai har zuciya da hunhunta,tana jin kamar numfashinta zai katse ne.
Yanayin yadda suka shigarwa hajja zahran na kuka lullube da fuskarta ya sanyata miqewa da sauri cikin firgita tana tambayar
"Kai...meye haka?,lafiya?" Itakam zahra bata iya tsaiwa ba saita wuce kawai zuwa daki,waje ta laluba ta kwanta gami da sake rushewa da sabon kuka.
Bayan minti biyu tajiyo muryar hajja na rafka salati da salallami,da alama sun gama gaya mata komai,sai kawai taja filo ta rufe kanta tana sake fashewa da wani irin kuka,tanajin sanyi na ratsa gabbanta,kafin kace meye wannan zazzabi ya rafketa.
Ba'a rufa awa guda ba hajjan ta shigo dakin
"Takwara.....kukan kike har yanzu?" Ta fadi tana qarasawa inda take kwancen,ta saka hannu ta yaye abun rufar tana kamo hannunta
"La'ilaha ilallahu,ke tashi,kwanciya kikayi xaki kashe kanki,kinji yadda jikinki ya rine da zazzabi?" Cikin daren dukka hankalin hajjan ya tashi,wanda hakan yasa hankalin yaranta su abba babba suma ya tashin,ta matsa lallai lallai saida su shamsu suka dau mota suka kaita asibiti,wanda basu dawo ba sai wajen sha biyu da rabi na dare saboda yadda zazzabin ya mata mugun kamu ya sanya suka dan riqeta sai daya sauka jikinta yadan daidaita.
Washegari duka tana kwance a daki,ko falo baga fito ba bare taga hasken rana,tana kwance tana bitar duka rayuwarsu ita da nuraddeen,bataga ta inda ta gaza ba da xai gujeta,bata ga me ta masa da zai saka mata d a wannan ba.
Duk yadda hajja taso ta fito da ita ta xauna koda a falo ne amma taqi,hankalinta kaf nakan zahran,duk bayan wasu mintuna saita leqo dubata,dukka jama'ar gidan kowa ya shigo ya dubata babba da yaro,amma banda mutum biyu,ummanta dai tasan kara ce da kawaici ya hanata leqoww,don koda hajja ma ta aika mata cewa tayi ace tana gaidata kawai,data sake aikawa sai tace ai tasan tana wajenta babu komai,shi kuwa dayan dama bashi a lissafinta,tama manta dashi cikin jerin jama'ar gidan.
Hajja da kanta ta yiwa abban gwammaja waya sanda yace zaya aiko a maidasu makaranta ita da hasina ta shaida masa bata da lafiya,a barta koda zuwa satin sama ne idan ta sake murmurewa,ya mata sannu da jiki,ya kuma ce zaisa a shaida hukumar makarantar idan ankai hasinan.
Sai da akayi kwanaki biyar da komawa makarantar sannan ta soma jin qwarin jikinta,don ta tattara dukkan wasu lamura na nuraddeen tayi qoqarin yin watsi dasu,a yadda ta lissafa kwanaki uku kenan da daurin aurensa,yana can wala'alla shida amaryarsa cikin farinciki,yama manta da lamarinta,hakan ya sanya washegari da azahar tayi wanka da ruwa mai dumi sosai,tasha dukka magungunanta,ta shirya cikin atamfa riga da zani sannan ta fito falon.
"Yauwa,ko kefa?" Hajja data taras zaune cikin falon ta fada cikin farinciki,tana kallon yadda zahran tadan fada,hancinta da fuskarta suka qara qara tsaho.
Mirmushi tadan yiwa hajja,cikin qarfin hali ta tsokaneta
"Ashe kina tsoro kada na mutu na barki"
"Zaki fara ko?" Hajjan ta fada tana watsa mata daquwa,dai dai sanda inna gaje ta fito daga kitchen zuwa falon
"Aah,ma sha Allah uwar masu gida jiki yayi kyau"
"Eh wallahi inna gaje" ta fada tana dan murmushi
"Alhamdulillahi,mun godewa Allah,Allah ya qara lafiya"
"Amin inna,akwai abinci ne?" Zahran ta tambaya
"Eh yanzu aka gama na rana...bari a zuba miki" inna gaje ta fada tans komawa kitchen din,sai zahran ta bita a baya ta amso abincin ta dawo inda ta tashi ta zauna
"Wannan abincin kamar na wasan yara wuro?" Hajja ta fada tana duban plate din
"Ya isheni hajja" saita qyaleta,tayi bismillah ta fara ci,lokaci lokaci idanunta nakan tv dake aiki.
Sallamar abubakar ce ta karade falon,abubakar shine yaro na farko a sassansu,daga shi sai ita,sai sauran qannenta maza guda biyu,sulaiman da yusuf,sai mace daya ilham,akwai tazarar shekara kusan biyar tsakaninta da abubakar,hakan ya wanzar da girmamawa sosai tsakaninsu,don haka umminsu ta tarbiyyancesu da bawa na gaba dasu girma.
"Maraba da saddiqu.....saukar yaushe?" Hajja ta fada tana dariya
"Ko minti biyu banyi da shigowa gidan ba" ya fada rabin hankalinsa nakan zahra data aje cokalin hannunta tana qoqarin gaidashi
"Lafiya lau...." Ya amsa a taqaice ya dora da
"Me kike a gida,duk 'yan makaranta sun koma makaranta?" Kafin hajja takai ga bada amsa an sake sallama cikin falon,muryarsa ta cika wani irin sauti mai sanyi,saidai tana cike da wani kwarjini mai ratsa kunne.
"Sannu da zuwa yaya" abubakar saddiq ya fada cikin salo na girmamawa,fuskarsa washe da fara'a
"Malam.....kana lafiya?" Ya fada yana miqawa saddiq hannunsa dake daure da wani rantsatsen agogo ruwan zaiba,wanda ya dace da lafiyayyar fatarsa da hutu da kuma kwanciyar hankali ya ratsata.
Da sauri sadiq ya miqa masa nasa hannun sukayi musabaha,saiya soma qoqarin zama hannun kujera yana gaida hajja cikin girmamawa,don shi sam baya wasan jika da kaka da ita,ta amsa cikin kulawa,don shi dinma dan gaban goshinta ne,sakamakon sunan maigidanta da yaci,sannan ta dora da fadin
"Kamar tare kuke da sadiq?" Yana dan latsa wayar hannunsa yace
"Tun dazun na shigo,na shiga ciki ne nadan huta"
"Auto ma sha Allah,ya aikin,da fatan an samu abinda ake bida?"
"Alhmdlh" ya fada hade da ajiyar zuciya yana maida wayarsa aljihun lafiyayyen trouser din jikinsa,wanda kallo daya zaka masa kasan me tsada ne,hakanan mai kayan yasan takan kaya masu aji.
Ido suka hada da xahra,kamar zaiyi magana sai kuma ya janye idanunsa duka cikin sakan biyu,ya harde hannayensa a qirji yana duban hajja dakewa sadiq bayanin dalilin xamanta a gidan,cikin sauri tace
"Ina yini" can qasa ya amsa kamar yadda ya saba
"Wallahi yaron ya bani mamaki,a haka kamar na Allah ashe bana arziqi bane,yaudara ce kawai ta kawoshi,yau ne mafa kawai na samu kanta ta fito falo ta zauna" ta qarashe zancan cikin nuna jimamai qwarai kan fuskarta idanunta kuma saman fuskar haidar,wanda ya dauke kansa zuwa yanzu daga kansu kamar ma baisan me ake ba.
Ajiyar zuciya sadiq yayi
"To Allah ya kyauta ya rufa asiri,abinda ya faru ya riga daya faru,sai kiyi qoqarin komawa makaranta.....hajja bari naje mu gaisa da sauran mutanen gidan,ummi ce kawai tasan da shigowata,zuwa anjima zan dawo abani abinda aka ragemin"
"Ka taho dai da abinda ka kawomin" dariya ya saki kana ya juya ya fice daga falon.
Qarasowa tayi tana dubanta,ba wanda ya iya magana cikinsu sai wayar da zahra ta miqa mata cikin rawar murya tana cewa
"Dubamin don Allah.....dai dai idanuna suke ganemin?" Hannu tasa ta karbi wayar,hoto daya tak ta kalla saita koma saman qafafunta ta zauna itama tana ci gaba da kallon hotonan cikin matuqar mamaki da sanyin jiki,kalamanta a sanyaye qwarai tace
"Nura ne zahra,nuraddeen dinki fa" rasa abu na gaba daya kamata tayi tayi,sai kawai tasa dukka tafin hannunta biyu ta rufe fuskarta dasu kamar wadda bata da muradin ganin duk wani haske dake cikin duniya,tana jin kamar ana yamutsa qwaqwalwarta,daidai sanda salma ta shigo,da sauri hafsat tace
"Yauwa,zo kigani don Allah,zoki tayani gani" da hanzari salman ta qaraso tana amsar wayar daga hannun hafsat.
Wani ashar salman ta dura,da yake itadin batakai haqurin hafsat ba,ta lalubi waje ta zauna tana cewa
"Meke shurin faruwa kenan zahra?laaa,kinga ana goge hotunan daga status.....sunyi disappearing gaba daya"ta fada tana kallon hafsat tare da nuna mata wayar
"Tabbas gogesu akayi,don ba'afi minti goma da dorasu ba,bajci ace har lokacin saukarsu yayi ba,me nuraddeen ke nufi?" Tambayar da bata da amsarta data cilla mata ita ta sanyata sakin wani irin kuka me ciwo,kukan daya daga hankalinsu gaba daya,lokacinne yasira itama ta sako kai,cikin yanayi na tsoro ta isa wajensu tana tambayarsu abinda ke faruwa,basu kai ga bata amsa ba kira ya shigo wayar zahran,duk da bata duba tasan me kiran,salma cikin fushi tace
"Bari na daga naji dan gidan marasa mutuncin me zaice?"kai hafsa da yasira wadda batasan ma ainihin meke faruwa ba suka daga mata,ta daga wayar ta sakata a handfree tayi shuru ba tare data ce komai ba,muryar nuradden ta bayyana
"Dear.....don Allah karki hukunci da abinda bakisan ainihin menene ba,ki bani dama inyi miki bayani pls"
"Ai karka damu,saqone ka bayar ya kuma iske inda kakeso ya iske,yo meye kuma wani abun damuwa a ciki?,kaci gaba da shagalinka kawai,amma ka sani,indai da haqqin zahra a wuyanka Allah saiya mata sakayya"
"Ki tsaya kiji don Allah,wacece?,hafsat ce ko yusra?"
"Ban sani ba dan gaba da rainin hankali,karka sake kiran wannan number" qit daga haka ta katse wayar,wanda kafin ta kuma cewa komai wani kiran ya sake biyo baya,haka suka sanya wayar gaba kowa ya rasa abun tabukawa,yanata faman kira ba qaqqautawa kamar yadda zahra ke kuka itama babu qaqqautawa,yasira ce ta karbi wayar daga qarshe bayan sun zayyana mata abinda ke faruwa ta kasheta gaba daya,har cikin zuciyarta tana jin wani irin suya da bacin rai,wannan wacce iriyar yaudara ce haka kai tsaye ta rashin mutunci da cin fuska,yana sane ma yayi posting hotunan a status dinsa?,abinda yafi tsaya musu a rai kenan.
Su hudun gaba daya suka hadu suna bata baki,harda nadiya data shigo daga qarshe gami da maimaita zancan cike da mamaki,don dukkansu bama su ba kusan kowa yasan da zaman nuraddeen a matsayin wanda zahra inna wuro ta tsaids zata aura,abun yazo musu matuqa a ba zata.
Ita kadai tasan yanayin data tsinci kanta da zuciyarta a ciki,wani yanayi da tun tasowarta bata taba jin irinsa ba saiyau,jin lamarin take kamar a mafarki,wai ita?,nuradden?,wanne irin abu haka tayi masa dafa cancanci irin wannan yaudarar mai ciwo?,har yana da bakin cewa ta saurareshi?,ta jima cikin wannan rudun,daga qarshe taji babu abinda take da buqata illa kadaicewa tayi kukanta ita kadai ko hakan zai sa ta samu gurbin da zata zuqi numfashi yakai har zuciya da hunhunta,tana jin kamar numfashinta zai katse ne.
Yanayin yadda suka shigarwa hajja zahran na kuka lullube da fuskarta ya sanyata miqewa da sauri cikin firgita tana tambayar
"Kai...meye haka?,lafiya?" Itakam zahra bata iya tsaiwa ba saita wuce kawai zuwa daki,waje ta laluba ta kwanta gami da sake rushewa da sabon kuka.
Bayan minti biyu tajiyo muryar hajja na rafka salati da salallami,da alama sun gama gaya mata komai,sai kawai taja filo ta rufe kanta tana sake fashewa da wani irin kuka,tanajin sanyi na ratsa gabbanta,kafin kace meye wannan zazzabi ya rafketa.
Ba'a rufa awa guda ba hajjan ta shigo dakin
"Takwara.....kukan kike har yanzu?" Ta fadi tana qarasawa inda take kwancen,ta saka hannu ta yaye abun rufar tana kamo hannunta
"La'ilaha ilallahu,ke tashi,kwanciya kikayi xaki kashe kanki,kinji yadda jikinki ya rine da zazzabi?" Cikin daren dukka hankalin hajjan ya tashi,wanda hakan yasa hankalin yaranta su abba babba suma ya tashin,ta matsa lallai lallai saida su shamsu suka dau mota suka kaita asibiti,wanda basu dawo ba sai wajen sha biyu da rabi na dare saboda yadda zazzabin ya mata mugun kamu ya sanya suka dan riqeta sai daya sauka jikinta yadan daidaita.
Washegari duka tana kwance a daki,ko falo baga fito ba bare taga hasken rana,tana kwance tana bitar duka rayuwarsu ita da nuraddeen,bataga ta inda ta gaza ba da xai gujeta,bata ga me ta masa da zai saka mata d a wannan ba.
Duk yadda hajja taso ta fito da ita ta xauna koda a falo ne amma taqi,hankalinta kaf nakan zahran,duk bayan wasu mintuna saita leqo dubata,dukka jama'ar gidan kowa ya shigo ya dubata babba da yaro,amma banda mutum biyu,ummanta dai tasan kara ce da kawaici ya hanata leqoww,don koda hajja ma ta aika mata cewa tayi ace tana gaidata kawai,data sake aikawa sai tace ai tasan tana wajenta babu komai,shi kuwa dayan dama bashi a lissafinta,tama manta dashi cikin jerin jama'ar gidan.
Hajja da kanta ta yiwa abban gwammaja waya sanda yace zaya aiko a maidasu makaranta ita da hasina ta shaida masa bata da lafiya,a barta koda zuwa satin sama ne idan ta sake murmurewa,ya mata sannu da jiki,ya kuma ce zaisa a shaida hukumar makarantar idan ankai hasinan.
Sai da akayi kwanaki biyar da komawa makarantar sannan ta soma jin qwarin jikinta,don ta tattara dukkan wasu lamura na nuraddeen tayi qoqarin yin watsi dasu,a yadda ta lissafa kwanaki uku kenan da daurin aurensa,yana can wala'alla shida amaryarsa cikin farinciki,yama manta da lamarinta,hakan ya sanya washegari da azahar tayi wanka da ruwa mai dumi sosai,tasha dukka magungunanta,ta shirya cikin atamfa riga da zani sannan ta fito falon.
"Yauwa,ko kefa?" Hajja data taras zaune cikin falon ta fada cikin farinciki,tana kallon yadda zahran tadan fada,hancinta da fuskarta suka qara qara tsaho.
Mirmushi tadan yiwa hajja,cikin qarfin hali ta tsokaneta
"Ashe kina tsoro kada na mutu na barki"
"Zaki fara ko?" Hajjan ta fada tana watsa mata daquwa,dai dai sanda inna gaje ta fito daga kitchen zuwa falon
"Aah,ma sha Allah uwar masu gida jiki yayi kyau"
"Eh wallahi inna gaje" ta fada tana dan murmushi
"Alhamdulillahi,mun godewa Allah,Allah ya qara lafiya"
"Amin inna,akwai abinci ne?" Zahran ta tambaya
"Eh yanzu aka gama na rana...bari a zuba miki" inna gaje ta fada tans komawa kitchen din,sai zahran ta bita a baya ta amso abincin ta dawo inda ta tashi ta zauna
"Wannan abincin kamar na wasan yara wuro?" Hajja ta fada tana duban plate din
"Ya isheni hajja" saita qyaleta,tayi bismillah ta fara ci,lokaci lokaci idanunta nakan tv dake aiki.
Sallamar abubakar ce ta karade falon,abubakar shine yaro na farko a sassansu,daga shi sai ita,sai sauran qannenta maza guda biyu,sulaiman da yusuf,sai mace daya ilham,akwai tazarar shekara kusan biyar tsakaninta da abubakar,hakan ya wanzar da girmamawa sosai tsakaninsu,don haka umminsu ta tarbiyyancesu da bawa na gaba dasu girma.
"Maraba da saddiqu.....saukar yaushe?" Hajja ta fada tana dariya
"Ko minti biyu banyi da shigowa gidan ba" ya fada rabin hankalinsa nakan zahra data aje cokalin hannunta tana qoqarin gaidashi
"Lafiya lau...." Ya amsa a taqaice ya dora da
"Me kike a gida,duk 'yan makaranta sun koma makaranta?" Kafin hajja takai ga bada amsa an sake sallama cikin falon,muryarsa ta cika wani irin sauti mai sanyi,saidai tana cike da wani kwarjini mai ratsa kunne.
"Sannu da zuwa yaya" abubakar saddiq ya fada cikin salo na girmamawa,fuskarsa washe da fara'a
"Malam.....kana lafiya?" Ya fada yana miqawa saddiq hannunsa dake daure da wani rantsatsen agogo ruwan zaiba,wanda ya dace da lafiyayyar fatarsa da hutu da kuma kwanciyar hankali ya ratsata.
Da sauri sadiq ya miqa masa nasa hannun sukayi musabaha,saiya soma qoqarin zama hannun kujera yana gaida hajja cikin girmamawa,don shi sam baya wasan jika da kaka da ita,ta amsa cikin kulawa,don shi dinma dan gaban goshinta ne,sakamakon sunan maigidanta da yaci,sannan ta dora da fadin
"Kamar tare kuke da sadiq?" Yana dan latsa wayar hannunsa yace
"Tun dazun na shigo,na shiga ciki ne nadan huta"
"Auto ma sha Allah,ya aikin,da fatan an samu abinda ake bida?"
"Alhmdlh" ya fada hade da ajiyar zuciya yana maida wayarsa aljihun lafiyayyen trouser din jikinsa,wanda kallo daya zaka masa kasan me tsada ne,hakanan mai kayan yasan takan kaya masu aji.
Ido suka hada da xahra,kamar zaiyi magana sai kuma ya janye idanunsa duka cikin sakan biyu,ya harde hannayensa a qirji yana duban hajja dakewa sadiq bayanin dalilin xamanta a gidan,cikin sauri tace
"Ina yini" can qasa ya amsa kamar yadda ya saba
"Wallahi yaron ya bani mamaki,a haka kamar na Allah ashe bana arziqi bane,yaudara ce kawai ta kawoshi,yau ne mafa kawai na samu kanta ta fito falo ta zauna" ta qarashe zancan cikin nuna jimamai qwarai kan fuskarta idanunta kuma saman fuskar haidar,wanda ya dauke kansa zuwa yanzu daga kansu kamar ma baisan me ake ba.
Ajiyar zuciya sadiq yayi
"To Allah ya kyauta ya rufa asiri,abinda ya faru ya riga daya faru,sai kiyi qoqarin komawa makaranta.....hajja bari naje mu gaisa da sauran mutanen gidan,ummi ce kawai tasan da shigowata,zuwa anjima zan dawo abani abinda aka ragemin"
"Ka taho dai da abinda ka kawomin" dariya ya saki kana ya juya ya fice daga falon.