Sashe 47
Alkibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin wani irin expression saman fuskarta ta daga kai ta kalleshi,qwayar idanunsu suka hadu waje guda,saiya dage mata gira daya,duk da har yanzu fuskarsa a dinke take
"Yes" canza mata wajen tsaiwa yayi daga gaba zuwa gefan kafadarsa,ya zagaya hannunsa a bayanta,ya riqe side din kafadarta daya da hannunsa daya,ya soma takawa a hankali tare da ita,dole gangar jikinta ta bishi suka soma ratsa wajen,yayi da taawa ta bisu da idanu,sai taji ba zata iya bari ba,don haka ta rufa musu baya dai still tana biye dasu,duk da tayi nesa nesa dasu ba kamar dazun ba.
Gaisaw yaci gaba dayi da mutanensa,kusan duk wanda ya gansu tare saiya tsaya,duk wani taku da zasuyi jikinsu na gogar na juna,hakan ya dinga weakening dinsu gaba daya ba tare da kowa ya sani ba,wanda kafin wani lokaci zahra ta rasa duk wani qwari daga jikinta,kusan riqon da yayi mata shike riqe da gangar jikinta,wannan shine karon farko data fara raba jikinta da wani da namiji,kamar yadda shima yake karin farko a rayuwarsa.
Hakan da yayi ba qaramin kada da yawa daga mutanen da yakeson kadawar yayi ba,a hankali yaga fuskokin suna canzawa,wasu kuma suna zamewa daga wajen,ciki harda taawa din data rasa inda zata tsoma ranta,ganin har a lokacin tana cikin jikinsa,hakanan duk inda zai zagaya tana tare dashi.
Da gaske yake bazai saketa a yanzun ba,riqonshi a gareta wani abune na daban da bata saba dashi ba,so take ya saketa ko zata rage wani abun,duk inda ya dora hannunsa a jikinta tana jin saqon saukar hannun har cikin qasusuwanta,kamar wanda keda wani abu na musamman cikin tafin hannunsa
"Cikina" yaji ta furta kalmar a hankali,saiya waiwaya ya dubeta kadan,suna hada idanu saita lumshesu,sam ya zuwa yanzu batason kallon qwayar idanunsa
"Ok" ya fada bayan ya dauke idanunsa daga ka ta na wasu sakanni,a hankali yayi niyyar zameta,saita tafi talau saboda yadda da gaske qirjinta ya riqe da ciwo,bai zaci haka ba cikin zafin nama ya riqota ta dawo jikinsa
"Are you serious?"kanta ta daga masa a hankali sanda take kwance a qirjinsa tana sauke numfashi,idanunta a runtse gam,hancinta na cika da qamshin turarensa,dumin jikinsa na ratsa fuskarta,tana iya juyo bugun zuciyarsa sosai
"Ok....ok" ya fada a hankali yana dan duban fuskarta dake cikin qirjinsa yana tunanin yadda zaiyi mata zuwa mota.
"Bani hannunki" ya fada calmly cikin qarfin hali,saita miqa masa hannun ya sake matseshi cikin nasa a hankali yana jin yadda tsigar jikinsa ke tashi tun daga qwaqwalwarsa zuwa gangar jikinsa,wanda sam baisan yaushe ya samo irin wannan feeling din ba,sai suka fara takawa a nutse har zuwa bakin motar.
Ga mamakinta da kanshi ya bude mata motar ta shiga ya rufe,saiya kunna ac na motar bayan ya dage dukka glasses din sama,sannan ya rufe ya juya yana barin wajen.
Idanunta ta bude tana kallonshi ta cikin glass din motar,karon farko da yayi wani abu da za'a bashi suna da tallafi a gareta kenan,bata sani ba,kona ganin idanun mutane ne?,saita rintse idanunta tana jin yadda ciwon ke sake motsa mata,ta sauke ajiyar zuciya tana kwanciya sosai cikin kujerar tana sauke numfashin wahala,wanda batayi cikakken minti ashirin ba taji saukar wani abu,ko data bude idanunta sai taga ruwan sama ke sauka,dai dai lokacin data hangi tahowarsa cikin sassarfa da qaramar lema a hannunsa,taci gaba da kallonsa tana riqe da saman cikinta har ya iso gab da motar,saita maida idanunta ta lumshe kamar me bacci,can qasan zuciyarta tana ambaton sunan Allah.
23/10/2021, 08:46 - 馃憤馃徎馃憤馃徎: 30
A nutse ya bude murfin motar ya shiga sannan ya rufe,yana shirin saka key ya kunna motar idanunsa suka kai kanta,ya dubi yadda ta cure waje daya,sai haka ya tuna masa da zahra....lokaci na qarshe a rayuwarta daya dauketa cikin motarsa,lokacin da take nemam agaji a sanda bashi da abinda zai iyayi mata,a haka a cure waje daya a sit din da wannan zahran ke kai,sai yaji wani abu ya tsarga masa tun daga kanshi har zuwa qafafunsa,sai daya furta can qasan maqoshinsa
"La haula wala quwwata illa billah" sannan ya bude idanun nasa ya tada motar suka fice daga wajen cikin tuqi a hankali saboda yadda ruwan saman yake qara qarfi.
Sannu a hankali suke tafiya bisa titin,haka kawai ya samu kansa da waiwayawa ya dubeta lokaci zuwa lokaci,time by time takan motsa ta kuma cije labbanta saboda ciwon da take jinsa har gadon bayanta.
A qalla sun shafe kusan minti talatin sannan suka qarasa unguwar tasu,yayi horn aka bude musu ya sanya motar tishi ciki ya ajeta a wajen adana motoci na gidan,saiya kashe motar,ya zubawa waje idanu ta cikin glass din motar yana kallon yadda ruwa ke gudu yana sauka da qarfinsa,a irin wannan yanayin da lokacin zuciyarsa na masa wani irin fes,tamkar ruwan na sauka ne saman zuciyarsa,saiya sanya hannunsa ya bude murfin motar ya fita,ya ware lemar hannunsa.
A kasalance itama ta bude murfin motar ta zura qafafunta tana rufe ido saboda yadda ruwan ya soma feso mata,duk da haka bata fasa fitowar ba,don babu abinda take buqata a yanzu irin ta samu waje ta kwanta sosai ko zata rage azabar da takeji.
Qanqame jikinta tayi waje daya ta soma nufar cikin gidan,saidai batayi taku biyar cikakke ba taji an lulluba mata abu saman kafadunta.
Kanta ta dago sanda yake dora mata lemar hannunsa tsakanin hannayenta,kafin takai ga kallon qwayar idanunsa tuni yayi gaba,cikin kuma ruwan saman dake saukowa yana dukan suit din jikinsa daya cire 'yar saman ya rufa mata,mamaki ya tsaidata,sai kuma tasoma takawa itama zuwa cikin.
Kamar wanda ya tuna wani abun saiya kuma ya tsaya,sannu a hankali ta iskeshi harma ta wuceshi sannan ya rufe mata baya,tana gaba yana bayanta har suka isa qofar falon.
Zagayeta yayi ya matsa bakin qofar ya sanya key din ya bude,sai yaja baya ya tsaya,taja qafafunta ta shige,da qyar ta qarasa dakinta ta zube saman katifa tana juyi.
A qalla ta kusa minti talatin babu wani sauqi,kadaici da zama ita kadai ta qara ta'azzara mata ciwon,sai qwalla ta cika mata idanu,nan da nan suka fara gangarowa,tana rayawa a ranta inda yanzu ace tana gida babu shakka da tuni an sama mata magani,koda babu magani akwai kai kawon jama'a da zai dauke mata wani abu daga ciwon komai qanqantarsa.
A nutse yake takowa cikin falon bayan yayi wanka da ruwa me dumi sosai ya sanya kaya masu dan kauri saboda ruwan daya dakeshi daga gun ajiye mota zuwa cikin gidan,har yanzu ruwan ake tafkawa bai tsaya ba bai kuma sassauta ba,garin gaba daya ya fara daukar sanyi,saman dining ya qarasa ya samu abinci yaci,ya gama yana sauko ya nufi daki don sanyin daya soma busawar ya fara sashi jin takura,bargo kawai yake da buqatar shiga.
Har zai shige dakin nasa kuma saiya dakata
"Amanar Allah ce a hannunka" ya tuna zancan mamanshi,saiya sauya akalarshi zuwa dakin nata.
Yana shiga ya sanya hannu da sauri yana kashe fankar dake faman wulwulawa kamar babu sanyin ruwan sama,sannan ya dauki remote yayi controlling sanyin da acn ke bayarwa sa'annan ya waiwaya saman katifar dakin.
Can ya hangota cikin bargon tana mutsu mutsu,duk da baka iya ganin koda kanta
"Wayyo Allah na" daya kasa kunne yaji tana fada qasa qasa,saiya qarasa da sauri ya haura zuwa saman katifar ya tankwashe qafafunsa,sannan ya saka hannu yana yaye abun rufar dai dai sanda ta qaraso dab da ita yake zaune garin mirgin mirgin din da takeyi
"Ya Allah" ya fada a hankali yana duban yadda take riqe da qirjinta,tun asali shi mutum me mai tausayin mara lafiya,abu na farko dake daga masa hankali,lalura da kuma raunin 'ya'ya mata.
Miqewa yayi tsaye da sauri yana ciro wayarsa daga aljihunsa,idan bai manta ba ya taba zuwa hutu gida lokacin bata da lafiya irin haka,yaji hajja tana cewa ulcer ce,da alama yanzun ma itace.
Kai tsaye number jafar ya kira,bugu uku ya daga
"How far oga?" Ya fada a sake
"Nasreen tana kusa?"
"Eh....Allah yasa lafiya"
"Lafiya.....amm...." Saiya rasa sunan da xai kira zahran dashi,daga qarshe yace
"Madam ce ba lafiya,ulcer dinta ta tashi....ko zata turamin medication da zata iya sha da zasu bata relief koda zuwa safiya ne?"
"Ok hold the phone" ya fada,sai yajishi yana magana duk da baijin me yake cewa,da alama tana kusa dashi ne,tsahon second talatin sannan yaji muryar jafar din,ya gaya masa magungunan da zata sha din,ya masa godiya sannan ya kashe kiran,ya sake kiran wata number sukayi magana,ya tura sunan magugunan sannan ya katse kiran nan ma yana maida dubanda dai a kanta,har yanzu babu wani canji da sanda ya shigo,yana tuna yadda ummi ke damuwa isan bashi da lafiya,ta miqa dukkan kulawarta akanshi,ya kamata shima ko yaya a yanzu ya kamanta akan jininta,saiya koma bakin katifar yadan tsugunna,yasan cewa bataci komai ba,yakan ji wani lokacin yadda suke daga da hajja idan bata da lafiya kan cin abinci,don haka yace, mata
"Tashi ki samu wani abun kici kafin a kawo magani" kaita girgiza masa alamun ba zataci ba,saiya dan xuba mata idanu na wasu sakanni,ba tare da yace da ita komai ba ya tashi ya fice.
Kusan minti talatin ya sake dawowa dakin,hannunsa dauke da wani irin mazubin abinci mai kyau,mai dauke da tambarin wani waje,ya qarasa ya janyo table din dake dakin ya dora akai,yana shirin miqewa wayarsa ta dauki ruri,ya daga yana amsa sallamar,wanda ya aika siyo magani ne ke shaida masa dukka pharmacies din a rufe suke
"Ok....thanks" ya fada a gajarce yana katse kiran
"Tashi kici abinci" ya kuma fada yana juyawa ya fice a dakin.
Bai wuce minti biyar ba ya dawo dauke da wata butar shayi me qananun kofuna,ya ajeta inda ya aje wancar ledar a hankali yana furxar da iska daga bakinsa,saiya dubeta still dai tana kwancen bata tashi ba,sake maimaita mata yayi ta tashin,saita girgiza masa kai alamun a'a
"Ki tashi nace....ina wasa dake ne!" Ya fada a dan tsawace,wanda hakan ya tilastata yaye bargon da take ciki,hawaye ne jage jage a idanunta,da gumi daya jiqe mata fuska,da alama zazzabin daya soma rufeta ne yake sauka,saita zauna sosai ba tare data miqe din ba.
"Yes" canza mata wajen tsaiwa yayi daga gaba zuwa gefan kafadarsa,ya zagaya hannunsa a bayanta,ya riqe side din kafadarta daya da hannunsa daya,ya soma takawa a hankali tare da ita,dole gangar jikinta ta bishi suka soma ratsa wajen,yayi da taawa ta bisu da idanu,sai taji ba zata iya bari ba,don haka ta rufa musu baya dai still tana biye dasu,duk da tayi nesa nesa dasu ba kamar dazun ba.
Gaisaw yaci gaba dayi da mutanensa,kusan duk wanda ya gansu tare saiya tsaya,duk wani taku da zasuyi jikinsu na gogar na juna,hakan ya dinga weakening dinsu gaba daya ba tare da kowa ya sani ba,wanda kafin wani lokaci zahra ta rasa duk wani qwari daga jikinta,kusan riqon da yayi mata shike riqe da gangar jikinta,wannan shine karon farko data fara raba jikinta da wani da namiji,kamar yadda shima yake karin farko a rayuwarsa.
Hakan da yayi ba qaramin kada da yawa daga mutanen da yakeson kadawar yayi ba,a hankali yaga fuskokin suna canzawa,wasu kuma suna zamewa daga wajen,ciki harda taawa din data rasa inda zata tsoma ranta,ganin har a lokacin tana cikin jikinsa,hakanan duk inda zai zagaya tana tare dashi.
Da gaske yake bazai saketa a yanzun ba,riqonshi a gareta wani abune na daban da bata saba dashi ba,so take ya saketa ko zata rage wani abun,duk inda ya dora hannunsa a jikinta tana jin saqon saukar hannun har cikin qasusuwanta,kamar wanda keda wani abu na musamman cikin tafin hannunsa
"Cikina" yaji ta furta kalmar a hankali,saiya waiwaya ya dubeta kadan,suna hada idanu saita lumshesu,sam ya zuwa yanzu batason kallon qwayar idanunsa
"Ok" ya fada bayan ya dauke idanunsa daga ka ta na wasu sakanni,a hankali yayi niyyar zameta,saita tafi talau saboda yadda da gaske qirjinta ya riqe da ciwo,bai zaci haka ba cikin zafin nama ya riqota ta dawo jikinsa
"Are you serious?"kanta ta daga masa a hankali sanda take kwance a qirjinsa tana sauke numfashi,idanunta a runtse gam,hancinta na cika da qamshin turarensa,dumin jikinsa na ratsa fuskarta,tana iya juyo bugun zuciyarsa sosai
"Ok....ok" ya fada a hankali yana dan duban fuskarta dake cikin qirjinsa yana tunanin yadda zaiyi mata zuwa mota.
"Bani hannunki" ya fada calmly cikin qarfin hali,saita miqa masa hannun ya sake matseshi cikin nasa a hankali yana jin yadda tsigar jikinsa ke tashi tun daga qwaqwalwarsa zuwa gangar jikinsa,wanda sam baisan yaushe ya samo irin wannan feeling din ba,sai suka fara takawa a nutse har zuwa bakin motar.
Ga mamakinta da kanshi ya bude mata motar ta shiga ya rufe,saiya kunna ac na motar bayan ya dage dukka glasses din sama,sannan ya rufe ya juya yana barin wajen.
Idanunta ta bude tana kallonshi ta cikin glass din motar,karon farko da yayi wani abu da za'a bashi suna da tallafi a gareta kenan,bata sani ba,kona ganin idanun mutane ne?,saita rintse idanunta tana jin yadda ciwon ke sake motsa mata,ta sauke ajiyar zuciya tana kwanciya sosai cikin kujerar tana sauke numfashin wahala,wanda batayi cikakken minti ashirin ba taji saukar wani abu,ko data bude idanunta sai taga ruwan sama ke sauka,dai dai lokacin data hangi tahowarsa cikin sassarfa da qaramar lema a hannunsa,taci gaba da kallonsa tana riqe da saman cikinta har ya iso gab da motar,saita maida idanunta ta lumshe kamar me bacci,can qasan zuciyarta tana ambaton sunan Allah.
23/10/2021, 08:46 - 馃憤馃徎馃憤馃徎: 30
A nutse ya bude murfin motar ya shiga sannan ya rufe,yana shirin saka key ya kunna motar idanunsa suka kai kanta,ya dubi yadda ta cure waje daya,sai haka ya tuna masa da zahra....lokaci na qarshe a rayuwarta daya dauketa cikin motarsa,lokacin da take nemam agaji a sanda bashi da abinda zai iyayi mata,a haka a cure waje daya a sit din da wannan zahran ke kai,sai yaji wani abu ya tsarga masa tun daga kanshi har zuwa qafafunsa,sai daya furta can qasan maqoshinsa
"La haula wala quwwata illa billah" sannan ya bude idanun nasa ya tada motar suka fice daga wajen cikin tuqi a hankali saboda yadda ruwan saman yake qara qarfi.
Sannu a hankali suke tafiya bisa titin,haka kawai ya samu kansa da waiwayawa ya dubeta lokaci zuwa lokaci,time by time takan motsa ta kuma cije labbanta saboda ciwon da take jinsa har gadon bayanta.
A qalla sun shafe kusan minti talatin sannan suka qarasa unguwar tasu,yayi horn aka bude musu ya sanya motar tishi ciki ya ajeta a wajen adana motoci na gidan,saiya kashe motar,ya zubawa waje idanu ta cikin glass din motar yana kallon yadda ruwa ke gudu yana sauka da qarfinsa,a irin wannan yanayin da lokacin zuciyarsa na masa wani irin fes,tamkar ruwan na sauka ne saman zuciyarsa,saiya sanya hannunsa ya bude murfin motar ya fita,ya ware lemar hannunsa.
A kasalance itama ta bude murfin motar ta zura qafafunta tana rufe ido saboda yadda ruwan ya soma feso mata,duk da haka bata fasa fitowar ba,don babu abinda take buqata a yanzu irin ta samu waje ta kwanta sosai ko zata rage azabar da takeji.
Qanqame jikinta tayi waje daya ta soma nufar cikin gidan,saidai batayi taku biyar cikakke ba taji an lulluba mata abu saman kafadunta.
Kanta ta dago sanda yake dora mata lemar hannunsa tsakanin hannayenta,kafin takai ga kallon qwayar idanunsa tuni yayi gaba,cikin kuma ruwan saman dake saukowa yana dukan suit din jikinsa daya cire 'yar saman ya rufa mata,mamaki ya tsaidata,sai kuma tasoma takawa itama zuwa cikin.
Kamar wanda ya tuna wani abun saiya kuma ya tsaya,sannu a hankali ta iskeshi harma ta wuceshi sannan ya rufe mata baya,tana gaba yana bayanta har suka isa qofar falon.
Zagayeta yayi ya matsa bakin qofar ya sanya key din ya bude,sai yaja baya ya tsaya,taja qafafunta ta shige,da qyar ta qarasa dakinta ta zube saman katifa tana juyi.
A qalla ta kusa minti talatin babu wani sauqi,kadaici da zama ita kadai ta qara ta'azzara mata ciwon,sai qwalla ta cika mata idanu,nan da nan suka fara gangarowa,tana rayawa a ranta inda yanzu ace tana gida babu shakka da tuni an sama mata magani,koda babu magani akwai kai kawon jama'a da zai dauke mata wani abu daga ciwon komai qanqantarsa.
A nutse yake takowa cikin falon bayan yayi wanka da ruwa me dumi sosai ya sanya kaya masu dan kauri saboda ruwan daya dakeshi daga gun ajiye mota zuwa cikin gidan,har yanzu ruwan ake tafkawa bai tsaya ba bai kuma sassauta ba,garin gaba daya ya fara daukar sanyi,saman dining ya qarasa ya samu abinci yaci,ya gama yana sauko ya nufi daki don sanyin daya soma busawar ya fara sashi jin takura,bargo kawai yake da buqatar shiga.
Har zai shige dakin nasa kuma saiya dakata
"Amanar Allah ce a hannunka" ya tuna zancan mamanshi,saiya sauya akalarshi zuwa dakin nata.
Yana shiga ya sanya hannu da sauri yana kashe fankar dake faman wulwulawa kamar babu sanyin ruwan sama,sannan ya dauki remote yayi controlling sanyin da acn ke bayarwa sa'annan ya waiwaya saman katifar dakin.
Can ya hangota cikin bargon tana mutsu mutsu,duk da baka iya ganin koda kanta
"Wayyo Allah na" daya kasa kunne yaji tana fada qasa qasa,saiya qarasa da sauri ya haura zuwa saman katifar ya tankwashe qafafunsa,sannan ya saka hannu yana yaye abun rufar dai dai sanda ta qaraso dab da ita yake zaune garin mirgin mirgin din da takeyi
"Ya Allah" ya fada a hankali yana duban yadda take riqe da qirjinta,tun asali shi mutum me mai tausayin mara lafiya,abu na farko dake daga masa hankali,lalura da kuma raunin 'ya'ya mata.
Miqewa yayi tsaye da sauri yana ciro wayarsa daga aljihunsa,idan bai manta ba ya taba zuwa hutu gida lokacin bata da lafiya irin haka,yaji hajja tana cewa ulcer ce,da alama yanzun ma itace.
Kai tsaye number jafar ya kira,bugu uku ya daga
"How far oga?" Ya fada a sake
"Nasreen tana kusa?"
"Eh....Allah yasa lafiya"
"Lafiya.....amm...." Saiya rasa sunan da xai kira zahran dashi,daga qarshe yace
"Madam ce ba lafiya,ulcer dinta ta tashi....ko zata turamin medication da zata iya sha da zasu bata relief koda zuwa safiya ne?"
"Ok hold the phone" ya fada,sai yajishi yana magana duk da baijin me yake cewa,da alama tana kusa dashi ne,tsahon second talatin sannan yaji muryar jafar din,ya gaya masa magungunan da zata sha din,ya masa godiya sannan ya kashe kiran,ya sake kiran wata number sukayi magana,ya tura sunan magugunan sannan ya katse kiran nan ma yana maida dubanda dai a kanta,har yanzu babu wani canji da sanda ya shigo,yana tuna yadda ummi ke damuwa isan bashi da lafiya,ta miqa dukkan kulawarta akanshi,ya kamata shima ko yaya a yanzu ya kamanta akan jininta,saiya koma bakin katifar yadan tsugunna,yasan cewa bataci komai ba,yakan ji wani lokacin yadda suke daga da hajja idan bata da lafiya kan cin abinci,don haka yace, mata
"Tashi ki samu wani abun kici kafin a kawo magani" kaita girgiza masa alamun ba zataci ba,saiya dan xuba mata idanu na wasu sakanni,ba tare da yace da ita komai ba ya tashi ya fice.
Kusan minti talatin ya sake dawowa dakin,hannunsa dauke da wani irin mazubin abinci mai kyau,mai dauke da tambarin wani waje,ya qarasa ya janyo table din dake dakin ya dora akai,yana shirin miqewa wayarsa ta dauki ruri,ya daga yana amsa sallamar,wanda ya aika siyo magani ne ke shaida masa dukka pharmacies din a rufe suke
"Ok....thanks" ya fada a gajarce yana katse kiran
"Tashi kici abinci" ya kuma fada yana juyawa ya fice a dakin.
Bai wuce minti biyar ba ya dawo dauke da wata butar shayi me qananun kofuna,ya ajeta inda ya aje wancar ledar a hankali yana furxar da iska daga bakinsa,saiya dubeta still dai tana kwancen bata tashi ba,sake maimaita mata yayi ta tashin,saita girgiza masa kai alamun a'a
"Ki tashi nace....ina wasa dake ne!" Ya fada a dan tsawace,wanda hakan ya tilastata yaye bargon da take ciki,hawaye ne jage jage a idanunta,da gumi daya jiqe mata fuska,da alama zazzabin daya soma rufeta ne yake sauka,saita zauna sosai ba tare data miqe din ba.