Sashe 60
Alkibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haka kawai ta samu kanta da zurfafa tunaninta kadan ta maidashi can baya,tana tuna kalolin abincin da yafi muradin ci,wanda a wancan lokacin matuqar su sukayi ya dinga gwalewa da kushesa kenan,wataran ma yaqi ci,har sai mama tayi masa fada sannan,ta saki murmushi tana tsaka da aikin,sanda ta tuna wani lokaci da hajja tasa ta diba masa abincin data yiwa abdulyasar,ranar kamar zaiyi me saboda tsabar hade gira,hatta hajjan tasha muzurai,akaci sa'a tayi magana,dama neman mai tankashi yake,yahau fada sosai,har sai dasu hafsat suka dinga kwasarsa suna gulmarsa a boye
"Hmmm...hala yau allurar sojoji ce ta motsa?"
"Allah sarki....duniya labari" ta fada a sarari ita kadai.
Bata dauki wani lokaci mai tsaho ba,kasancewar abincin dai dai cikin daya zuwa mutum biyu tayishi,ta shirya komai bisa wani tsari me birgewa,tana gyara kitchen din hajja ta shigo,ta kalli yadda ta tsara komai saita kyabe baki
"Ashe dai ashe dai,yanzu dukka zakin aka yiwa wannan?" Waiwayowa zahran tayi tana duban kwanukan data shirya da hannunta,sam batasan ma tayi abunda hajjan ta gani din ba sai data magantu,komai a tsare,duk wanda ya kalla saiya burgeshi bare ya bude ciki,flask din hajja ne sababbi,wanda jikoki da 'ya'yanta ke siyo mata da wanda ake bata kyautarsu dake ajiyewa bata amfani dasu suta dauko ta bare ta zuba masa abincin a ciki
"Ya gama ci kuyi lissafin kudin kwanukana,saikun bayani,ko naje har gida na fanshe a kitchen dinki" kunya taji ta kamata sosai,don bata kawo komai a kanta ba sai yanzu,sai ta yiwa hajjan tabarmar kunya,tahau zumbura baki tana cewa
"Wai komai mutum yayi shi bai iya ba,inafa zaman zamana kika ce sai na masa abinci....inda naqi tashi kuma nan ma qilu ta jawo bau,nayin kuma nan ma ban miki gwaninta ba....to inaga kawai a fasa kai abincin"
"Iyeee.....to uwata,ni meye nawa a ciki idan baicin bama,asarata ko taku keda shi?,ki tambaya kiji,mijina bai taba neman abinci ya rasa ba wajena har ya mutu,girki ma daya amsa sunansa ba irin nakun nan ba taba ka lashe....wanda kula da mijinma kamar an muku gori sai ance kuyi,yo ni meye nawa afasa kai masa.....kai....mustapha" tahau qwala kiran gangan da ganganci,don tasan mustapha baya falon,baya ma gidan gaba daya,tun safe abba yusuf ya aikeshi gyaran motarshi,ai kam a sukwane ta saki kwanon hannunta cikin sink ta isa gaban kwanukan
"Saiki bari na bayar da kaina nida nasha aiki,amma kya kira ya musty mai shegen ci da saiya kusa hadawa da flask din duka ya cinye ma?" Dariya sosai ta qwacewa hajja ba tare data shirya ba,sai kuma tadan maze bayan ta gama dariyarta
"Ya suke da mijinki wajen shegen ci,kijimin yarinya" itadai sai raba ido take,kada hajja tayi mata aika aika,bata sake tanka mata ba har ta gama abinda ya kawota kitchen din ta fice abinta ko a jikinta.
Gangar jikinsa ce kawai zaune waje daya da sunan hutu,amma gaba daya zuciyarsa da qwaqwalwarsa sun gaza samun hutun da yake buqata din,ga yunwa da yakeji amma ya kasa katabus,minti daya biyu saiya dubi qofar shigowa sashen nasa,haka kawai jikinsa ke bashi tana nan zuwa gareshi kowanne lokaci,saiya yunqura zai tashi ya aiwatar da abinda zuciyarsa ke gaya masa,sai kuma miskilanci ya maidashinya zaunar,yana sonne ya tabbatarwa kansa cewa aikinsa yayi kyau?,duk da ya fara ganin alamomi da suka sanya ya baiwa kansa mark,tare da shanshano qamshin nasara,mutum ne shi daya tashi kaf rayuwarsa cikin cimma nasara kan abunda yasa gaba,matuqar nasararsa ta kasance......to wannan shine mataki na qarshe da zai kawo qarshen komai.
Miqewa yayi a karo na qarshe,yana jin juriyarsa da haqurinsa sunkai qarshe,bazai iya ci gaba da zaman jira ba,saidai yana isa bakin qofa yaji an murda handle din an turo qofar,dai dai sanda wayarsa ta dauki ringing,saiya dakata daga bayan qofar,ya ciro wayar yana dubawa.
Daya daga cikin jami'ansu ne me suna Deborah,tana qarqashin jagorancinsa,saidai ita din likita ce,wadda sanda suka dawo yabar kulawar sojojin da suka dawo dasu marasa lafiya da masu rauni ana kula dasu a asibitinsu,itace kuma shugabar likitocin ya buqaci zamun duk wani bayani bayan ya tafi kan ci gaban da aka samu kan marasa lafiyan,babbar macace sosai,don tayi shekara a qalla arba'in da takwas,kaf cikin ma'aikatan mata ita kadai yakewa dariya,saboda yana ganin girmanta kamar yadda take ganin nashi.
Mummunar faduwar gaba hadi da bacin raine suka bijiro mata sanda taji ya ambaci sunan mace cikin wayarsa,hakanan yana wayar cikin sakin fuska,abinda ba zata iya tune yaushe ne lokaci na qarshe data jishi yana waya da wani koda namiji bane cikin walwala haka,wani abu ya taso ya tokare mata maqogaro,har yasa kunnuwanta suka toshe,ta daina ji ko gane maganar da yake,maganganun da hasashen da zuciyarta keta kawo mata su take fahimta,don haka tana dire kwandunan hannunta tayi hanyar fita ba tare data ko kalleshi ba.
Duk takunta daya idanunsa na biye da ita,sai hankalinsa ya rabu biyu,rabi naga wayar da yakeyi,rabi kuma na akanta,karon farko daya taba qarewa tafiyarta kallo,kamar wadda ke rangaji haka takunta suke a tsare,saidai yanayin halittarta ne hakan,batasan ma hakan na faruwa ba.
Ganin ta nufo qofar gadan gadan saiya taka a hankali ya qarasa rufe qofar,ya murza muqulli ya rufeta gaba daya,sannan ya jingina jikinsa da qofar,sai ya zaman shida ita suna fuskantar juna.
Zata iya cewa bataji ya yiwa wadda suke wayar sallama ba,yadai zame wayar daga kunnensa ya jefata gefanshi,tsintar kanta kawai tayi cikin jikinsa,ya mata wata kyakkyawar runguma da taso zabge duk wani baci da ranta yayi kan wayar da yayi yanzun.
Tuni jikinta ya soma mutuwa saboda qamshij da jikinsa ke fitarwa,da wani irin dumi dake fita daga jikinsa zuwa nata,amma duk da haka ta aje wannan gefe,ta soma turashi da yunqurin barin jikinsa,da sauri ya sake yi mata qawanya da hannayensa yana sake yi mata kyakkyawan mazauni cikin qirjinsa yana fadin
"Ke......relax mana,kada kiyi kishi....abokiyar aikina ce fa,nothing else" mamaki ne ya kamata sosai,ya akayi ya karanci haka daga idanuwanta kawai?,kamar me aiki da sihiri,ko kuma wanda ya karanci ilimin sanin halayyar dan adam.
Mintuna a qalla kusan biyar suna tsaye a haka,shuru ba tare da ya sake cewa komai ba,ita dinma haka,kowa na sauraren bugun zuciya da fitar numfashin dan uwansa,ita kanta batasan ke ya debeta taci gaba da zama cikin jikinsa ba,sai taga ya kamata tayi koda pretendin ne,kada ta zubda kanta
"Ka sakeni" ta fada tana tura hannayensa,da sauri ya hannunsa ya birkitota ta dawo tana fuskantarsa,a maimakon dazu data bashi baya,hannayensa duka biyun ya sanya ya kama qugunta ya ruqe yana qarewa fuskarta kallo,cikin wata murya mai laushi da sanyi,can qasan maqoshi wanda koda kana kusa dasu sai ka kasa kunnenka sannan zaka iya jin abinda suke fada yace
"Zahra...." Mamaki ya kusan kasheta a tsaye a wajen,dama yasan sunanta ne?,eh dole tace haka,saboda tsahon rayuwarsu cikin gidan bata taba jin ya ambaci sunanta ba ko a wasa,ji tayi duk duniya kamar yafi kowa iya ambaton sunanta,kamar ya fadi sunan nata ne da wani yaren daban ba hausa ba
"Ke kadai ce rayuwata bata da amfani cikin taki rayuwar ko?" Ji tayi tambayar ta mata nauyi sosai,bata kuma gama fahimtar abinda ya fada din
"Yes....kowa yayi kewata amma banda ke....kowa yana nemana amma banda ke,kyautawa kenan?" Lallai yau mamakin da haidar din yake bata ya wuce tunaninta,da zata iya zata so ta daga kanta ta kalli idanunshi da fuskarshi,don ta samu tabbacin daga bakinsa kalaman ke fita
"Kin kyauta....matsamin daga jiki" kamar me jira kuwa ta janye jikinta,haushi ya cikata taf,ita din ya nemeta?,sau nawa yana kiransu hajja tana wajen ba wanda ya taba bi ta kanta,kwanciyarta a asibiti saboda waye tayi?,ko don ba zata iya gaya masa bane.
Caraf aka riqe hannuta,ta waiwayo da sauri don har ta soma yin gaba,fuskarshi a hade kamar bashi ne yayi maganar da yayin dazun ba,saiya sakar mata hannun sanda take zamewa itama daga hannunsa,ta juya zuwa inda ta ajjiye abincin ya bita a baya,ya samu waje ya zauna.
Duk wani motsi da zatayi sai ta tsinci idanunshi a kanta,wanda hakan ke sake narkar da ita,kamar zata saki kuka haka takejin zuciyarta na rauni,wani abu mai qarfi yana ratsata loko da saqo,daidai sanda ta kammala zuba mishi abincin wayarsa ta dauki tsuwwa,hajja ce saiya daga kanshi tsaye,ya kuma sanya handsfree
"Zaki.....maza ka turomin innawuro....hadari garin" shuru yayi yama kasa amsawa hajjan,shi abun nata ma mamaki yake bashi,haushi ya kuma cikashi sosai,da gaske wannan karon yaji haushi har ransa,don haka yace
"Gata nan,daga yau a dinga turo min mustapha shamsu ko ibrahim su dinga kawomin abincina" saiya katse wayar,tana jinsa bata waiwayo ba,saita qara wuta,dama neman hanyar tafiyarta cikin sauqi take,don ita kadai tasan yadda yake qara wa zuciyarta pressure,tana jin kamar ba zata iya dogon xama dashi ba.
Tana fita ruwa ya tsinke,saita tsaya cak tana kallon yadda ruwan ke sauka daga sama da gudunsa,shahada tayi ta saka qafarta ta fara takawa cikin ruwan,wata walqiya me azabar haske aka saki,take ta haska ko ina kai kace tsakiyar rana ce,cikin sakanni ta dauke,kafin ta gama mutstsika idanunta da walqiyar ta kashe tsawa mai qarfi ta biyo baya,ai batasan sanda ta juya da mugun gudu ba ta koma ciki.
"Subhanallazi yusabbihur ra'adu bi hamdihi,wal mala'ikatu min khifatihi" ya furta addu'ar tsawa sanda yaji tsawar,yana gama rufe bakinsa tana shigowa a rude,ta jiqe sosai sai diga takeyi,sunayin arba kuma saita daburce,ta karanci abinda ya tsoratatan,amma sai yayi kaman bai gane ba.
Qin zama tayi tana ta leqen ruwan,saidai ba alamar zai dauke,ga sanyin ac ya hadu da jiqewar da tayi yana kadata har cikin jikinta,shima ya lura da hakan,amma yana mamakin dakiya da taurin kai irin nata,ya gama karantar komai daga gareta ta cikin qwayar idanunta,amma taba qaryata kanta da kanta da ayyukanta.
A hankali taji sanyin yana raguwa,data lura ashe kashe acn yayi,ya maye gurbinta da room heater,saita dan samu nutsuwa kadan,ta sake saka kanta tana leqen ruwan.
Ta saman kanta taji an yafa mata wani abu me qamshi,ta daga kanta da sauri sai taga ya bude mata lema
"Muje" kawai ya fada,ta tsaya sosai ta fara takawa yana biye da ita riqe da lemar,hannunta riqe da abinda ya yafa matan,wanda ya kasance qaramin bargo ne mai laushi sosai,kuma yana da nauyin da zai kare maka sanyi.
"Hmmm...hala yau allurar sojoji ce ta motsa?"
"Allah sarki....duniya labari" ta fada a sarari ita kadai.
Bata dauki wani lokaci mai tsaho ba,kasancewar abincin dai dai cikin daya zuwa mutum biyu tayishi,ta shirya komai bisa wani tsari me birgewa,tana gyara kitchen din hajja ta shigo,ta kalli yadda ta tsara komai saita kyabe baki
"Ashe dai ashe dai,yanzu dukka zakin aka yiwa wannan?" Waiwayowa zahran tayi tana duban kwanukan data shirya da hannunta,sam batasan ma tayi abunda hajjan ta gani din ba sai data magantu,komai a tsare,duk wanda ya kalla saiya burgeshi bare ya bude ciki,flask din hajja ne sababbi,wanda jikoki da 'ya'yanta ke siyo mata da wanda ake bata kyautarsu dake ajiyewa bata amfani dasu suta dauko ta bare ta zuba masa abincin a ciki
"Ya gama ci kuyi lissafin kudin kwanukana,saikun bayani,ko naje har gida na fanshe a kitchen dinki" kunya taji ta kamata sosai,don bata kawo komai a kanta ba sai yanzu,sai ta yiwa hajjan tabarmar kunya,tahau zumbura baki tana cewa
"Wai komai mutum yayi shi bai iya ba,inafa zaman zamana kika ce sai na masa abinci....inda naqi tashi kuma nan ma qilu ta jawo bau,nayin kuma nan ma ban miki gwaninta ba....to inaga kawai a fasa kai abincin"
"Iyeee.....to uwata,ni meye nawa a ciki idan baicin bama,asarata ko taku keda shi?,ki tambaya kiji,mijina bai taba neman abinci ya rasa ba wajena har ya mutu,girki ma daya amsa sunansa ba irin nakun nan ba taba ka lashe....wanda kula da mijinma kamar an muku gori sai ance kuyi,yo ni meye nawa afasa kai masa.....kai....mustapha" tahau qwala kiran gangan da ganganci,don tasan mustapha baya falon,baya ma gidan gaba daya,tun safe abba yusuf ya aikeshi gyaran motarshi,ai kam a sukwane ta saki kwanon hannunta cikin sink ta isa gaban kwanukan
"Saiki bari na bayar da kaina nida nasha aiki,amma kya kira ya musty mai shegen ci da saiya kusa hadawa da flask din duka ya cinye ma?" Dariya sosai ta qwacewa hajja ba tare data shirya ba,sai kuma tadan maze bayan ta gama dariyarta
"Ya suke da mijinki wajen shegen ci,kijimin yarinya" itadai sai raba ido take,kada hajja tayi mata aika aika,bata sake tanka mata ba har ta gama abinda ya kawota kitchen din ta fice abinta ko a jikinta.
Gangar jikinsa ce kawai zaune waje daya da sunan hutu,amma gaba daya zuciyarsa da qwaqwalwarsa sun gaza samun hutun da yake buqata din,ga yunwa da yakeji amma ya kasa katabus,minti daya biyu saiya dubi qofar shigowa sashen nasa,haka kawai jikinsa ke bashi tana nan zuwa gareshi kowanne lokaci,saiya yunqura zai tashi ya aiwatar da abinda zuciyarsa ke gaya masa,sai kuma miskilanci ya maidashinya zaunar,yana sonne ya tabbatarwa kansa cewa aikinsa yayi kyau?,duk da ya fara ganin alamomi da suka sanya ya baiwa kansa mark,tare da shanshano qamshin nasara,mutum ne shi daya tashi kaf rayuwarsa cikin cimma nasara kan abunda yasa gaba,matuqar nasararsa ta kasance......to wannan shine mataki na qarshe da zai kawo qarshen komai.
Miqewa yayi a karo na qarshe,yana jin juriyarsa da haqurinsa sunkai qarshe,bazai iya ci gaba da zaman jira ba,saidai yana isa bakin qofa yaji an murda handle din an turo qofar,dai dai sanda wayarsa ta dauki ringing,saiya dakata daga bayan qofar,ya ciro wayar yana dubawa.
Daya daga cikin jami'ansu ne me suna Deborah,tana qarqashin jagorancinsa,saidai ita din likita ce,wadda sanda suka dawo yabar kulawar sojojin da suka dawo dasu marasa lafiya da masu rauni ana kula dasu a asibitinsu,itace kuma shugabar likitocin ya buqaci zamun duk wani bayani bayan ya tafi kan ci gaban da aka samu kan marasa lafiyan,babbar macace sosai,don tayi shekara a qalla arba'in da takwas,kaf cikin ma'aikatan mata ita kadai yakewa dariya,saboda yana ganin girmanta kamar yadda take ganin nashi.
Mummunar faduwar gaba hadi da bacin raine suka bijiro mata sanda taji ya ambaci sunan mace cikin wayarsa,hakanan yana wayar cikin sakin fuska,abinda ba zata iya tune yaushe ne lokaci na qarshe data jishi yana waya da wani koda namiji bane cikin walwala haka,wani abu ya taso ya tokare mata maqogaro,har yasa kunnuwanta suka toshe,ta daina ji ko gane maganar da yake,maganganun da hasashen da zuciyarta keta kawo mata su take fahimta,don haka tana dire kwandunan hannunta tayi hanyar fita ba tare data ko kalleshi ba.
Duk takunta daya idanunsa na biye da ita,sai hankalinsa ya rabu biyu,rabi naga wayar da yakeyi,rabi kuma na akanta,karon farko daya taba qarewa tafiyarta kallo,kamar wadda ke rangaji haka takunta suke a tsare,saidai yanayin halittarta ne hakan,batasan ma hakan na faruwa ba.
Ganin ta nufo qofar gadan gadan saiya taka a hankali ya qarasa rufe qofar,ya murza muqulli ya rufeta gaba daya,sannan ya jingina jikinsa da qofar,sai ya zaman shida ita suna fuskantar juna.
Zata iya cewa bataji ya yiwa wadda suke wayar sallama ba,yadai zame wayar daga kunnensa ya jefata gefanshi,tsintar kanta kawai tayi cikin jikinsa,ya mata wata kyakkyawar runguma da taso zabge duk wani baci da ranta yayi kan wayar da yayi yanzun.
Tuni jikinta ya soma mutuwa saboda qamshij da jikinsa ke fitarwa,da wani irin dumi dake fita daga jikinsa zuwa nata,amma duk da haka ta aje wannan gefe,ta soma turashi da yunqurin barin jikinsa,da sauri ya sake yi mata qawanya da hannayensa yana sake yi mata kyakkyawan mazauni cikin qirjinsa yana fadin
"Ke......relax mana,kada kiyi kishi....abokiyar aikina ce fa,nothing else" mamaki ne ya kamata sosai,ya akayi ya karanci haka daga idanuwanta kawai?,kamar me aiki da sihiri,ko kuma wanda ya karanci ilimin sanin halayyar dan adam.
Mintuna a qalla kusan biyar suna tsaye a haka,shuru ba tare da ya sake cewa komai ba,ita dinma haka,kowa na sauraren bugun zuciya da fitar numfashin dan uwansa,ita kanta batasan ke ya debeta taci gaba da zama cikin jikinsa ba,sai taga ya kamata tayi koda pretendin ne,kada ta zubda kanta
"Ka sakeni" ta fada tana tura hannayensa,da sauri ya hannunsa ya birkitota ta dawo tana fuskantarsa,a maimakon dazu data bashi baya,hannayensa duka biyun ya sanya ya kama qugunta ya ruqe yana qarewa fuskarta kallo,cikin wata murya mai laushi da sanyi,can qasan maqoshi wanda koda kana kusa dasu sai ka kasa kunnenka sannan zaka iya jin abinda suke fada yace
"Zahra...." Mamaki ya kusan kasheta a tsaye a wajen,dama yasan sunanta ne?,eh dole tace haka,saboda tsahon rayuwarsu cikin gidan bata taba jin ya ambaci sunanta ba ko a wasa,ji tayi duk duniya kamar yafi kowa iya ambaton sunanta,kamar ya fadi sunan nata ne da wani yaren daban ba hausa ba
"Ke kadai ce rayuwata bata da amfani cikin taki rayuwar ko?" Ji tayi tambayar ta mata nauyi sosai,bata kuma gama fahimtar abinda ya fada din
"Yes....kowa yayi kewata amma banda ke....kowa yana nemana amma banda ke,kyautawa kenan?" Lallai yau mamakin da haidar din yake bata ya wuce tunaninta,da zata iya zata so ta daga kanta ta kalli idanunshi da fuskarshi,don ta samu tabbacin daga bakinsa kalaman ke fita
"Kin kyauta....matsamin daga jiki" kamar me jira kuwa ta janye jikinta,haushi ya cikata taf,ita din ya nemeta?,sau nawa yana kiransu hajja tana wajen ba wanda ya taba bi ta kanta,kwanciyarta a asibiti saboda waye tayi?,ko don ba zata iya gaya masa bane.
Caraf aka riqe hannuta,ta waiwayo da sauri don har ta soma yin gaba,fuskarshi a hade kamar bashi ne yayi maganar da yayin dazun ba,saiya sakar mata hannun sanda take zamewa itama daga hannunsa,ta juya zuwa inda ta ajjiye abincin ya bita a baya,ya samu waje ya zauna.
Duk wani motsi da zatayi sai ta tsinci idanunshi a kanta,wanda hakan ke sake narkar da ita,kamar zata saki kuka haka takejin zuciyarta na rauni,wani abu mai qarfi yana ratsata loko da saqo,daidai sanda ta kammala zuba mishi abincin wayarsa ta dauki tsuwwa,hajja ce saiya daga kanshi tsaye,ya kuma sanya handsfree
"Zaki.....maza ka turomin innawuro....hadari garin" shuru yayi yama kasa amsawa hajjan,shi abun nata ma mamaki yake bashi,haushi ya kuma cikashi sosai,da gaske wannan karon yaji haushi har ransa,don haka yace
"Gata nan,daga yau a dinga turo min mustapha shamsu ko ibrahim su dinga kawomin abincina" saiya katse wayar,tana jinsa bata waiwayo ba,saita qara wuta,dama neman hanyar tafiyarta cikin sauqi take,don ita kadai tasan yadda yake qara wa zuciyarta pressure,tana jin kamar ba zata iya dogon xama dashi ba.
Tana fita ruwa ya tsinke,saita tsaya cak tana kallon yadda ruwan ke sauka daga sama da gudunsa,shahada tayi ta saka qafarta ta fara takawa cikin ruwan,wata walqiya me azabar haske aka saki,take ta haska ko ina kai kace tsakiyar rana ce,cikin sakanni ta dauke,kafin ta gama mutstsika idanunta da walqiyar ta kashe tsawa mai qarfi ta biyo baya,ai batasan sanda ta juya da mugun gudu ba ta koma ciki.
"Subhanallazi yusabbihur ra'adu bi hamdihi,wal mala'ikatu min khifatihi" ya furta addu'ar tsawa sanda yaji tsawar,yana gama rufe bakinsa tana shigowa a rude,ta jiqe sosai sai diga takeyi,sunayin arba kuma saita daburce,ta karanci abinda ya tsoratatan,amma sai yayi kaman bai gane ba.
Qin zama tayi tana ta leqen ruwan,saidai ba alamar zai dauke,ga sanyin ac ya hadu da jiqewar da tayi yana kadata har cikin jikinta,shima ya lura da hakan,amma yana mamakin dakiya da taurin kai irin nata,ya gama karantar komai daga gareta ta cikin qwayar idanunta,amma taba qaryata kanta da kanta da ayyukanta.
A hankali taji sanyin yana raguwa,data lura ashe kashe acn yayi,ya maye gurbinta da room heater,saita dan samu nutsuwa kadan,ta sake saka kanta tana leqen ruwan.
Ta saman kanta taji an yafa mata wani abu me qamshi,ta daga kanta da sauri sai taga ya bude mata lema
"Muje" kawai ya fada,ta tsaya sosai ta fara takawa yana biye da ita riqe da lemar,hannunta riqe da abinda ya yafa matan,wanda ya kasance qaramin bargo ne mai laushi sosai,kuma yana da nauyin da zai kare maka sanyi.