Sashe 24
Tambarin Talaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Tunda A Majeed ya shiga bedroom dinshi bai fito ba domin yanda yake jin jikinshi wani iri ga kamshin turaren indo daya dameshi yasa shi cikin wani yanayi dakyar ya tashi ya fada toilet yayi wanka amma still kamshin na nan sai juyi yakeyi tare da kallon inda ta cijeshi yana dan shafawa a hankali, yanda yake ji a zuciyanshi yafi zafin cizon sau dubu, domin babu komai sai son indo dake addabanshi, zazzabi ne ya rufeshi wanda yasa ya kasa fitowa waje koh sallah a daki yake yi dan bazai iya zuwa masallaci ba, haka ya kwana baiko leko ba, yana ciki yana fama da zazzabi sosai,
Indo da mum suna zaune a falon kasa, abdul ya shigo da sallama, duka Suka amsa da Fara'a, abdul ya gaida Mum cikin kulawa ta amsa da abdul har yanzu dai kana ta fama, dan murmushi yayi tare da zama, Mum taci gaba da fadin ni inaga daka hakura da yarinyar wlh ka auri wata nan gaba in Allah yasa matarka ce sai ayi, indo ce tace Mum niko nafi son ya auri yarinyar wlh saboda irin halin da take ciki, Mum tace hakane aysha taimako ne amma Abu yau wajan shekara biyar ana fama, indo ta danyi shuru can ta nisa tace niko Mum dan Allah inaso inje inga yarinyar, Mum kallonta tayi tare da fadin babu damuwa zan fadama Dad sai kusa rana, Abdul yaji dadin hakan sosai, masu aikin gidan ne suka Kawo ma Abdul Abun taba baki, ya kalli indo yace ya Office din? Indo tace Alhmdlh, wayan Mum ne yayi kara dauka tayi ban san mai ake fada mata ba naji tace gani nan zuwa, kallon abdul tayi tace wai A Majeed ne tun jiya daya shiga Gida bai fito ba, gashi matarshi bata nan shine driver dinshi ya kira, abdul yace bari inje in gani, mum tace muje tare, Bin abdul tayi akabar indo a gida wacce tunda taji hakan jikinta ya mata wani iri, daki ta koma ta kwanta tana jin wani iri.
Koda su Mum sukaje gidan a dakinshi suka sameshi ya lullube duk da AC din dakin a kashe yake amma yana ta rawan sanyi cikin tashin hankali Mum ta kira No Dr dinsu wanda yace mata gashi nan amma baya kusa zai dan kai nan da 30mnt,kwatancen gidan A majeed tamai sannan ta kashe, abdul fita yayi yabar Mum ita daya cikin tashin hankali tama rasa abunyi jin muryanshi tayi yana fadin aysha I love You come back to me I will treat you like a queen, shuru tayi tana mamaki, daukan wayanta tayi ta kara kiran Dr din yace yana hanya karta damu, Mum tace koh su Kawo shi hspt ne, yace ta bari ya kusa zuwa ba'a dade ba sai ga Dr din da abdul nan aka fara dubashi inda Dr ya mishi allura tare da bashi Magani, yace ma Mum a bashi abinci yaci, amma mai ruwa, mum da sauri ta hado mishi Tea cikin kitchen din da yayi kura dan Zainab ta Kori masu mata aiki sai dai wani lokacin ta kira azo a Mata shara duk saboda gudun kar a kara nanata abunda akayi da indo, mum rikoshi tayi tana bashi tea din jikinshi yadan fara rage zafi dan alluran da aka mai,mum ta bashi Magani yasha nan dr yama Mum sallama tace ya tsaya su tayata kama A Majeed din a sashi mota domin gidanta za'a kaishi hakan koh akayi aka kamashi suka nufi gidan mum din, sama akayi Dashi kusa da dakinta inda aka kwantar Dashi akan gadon dakin, idonshi a lumshe daka gani yana fama da ciwan sosai, Mum ruwa ta dibo tasa towel a ciki tana matsewa tana dan shafamai a jiki, lokaci daya zafin jikin ya sauka bacci ya daukeshi, Mum wani irin tausayin dan nata take ji, amma idan ta tuna abunda yayi sai taji ranta na baci, domin ya nuna mata baya son gatan da tamai, kun san d'a da uwa😢, dakin indo ta nufa wacce take zaune amma hannunta biyu akan fuskanta daka gani tunani takeyi domin har Mum ta shigo bata ji motsinta ba har saida ta kira sunanta, tayi firgit tare da tashi tana kakaro murmushi tana fadin sannu da dawowa Mum, mum amsawa tayi tare da zama akan gadon dakin ganin haka yasa indo ta zauna a kusa da ita, Mum tace aysha lafiya kuwa? Dam taji kirjinta ya buga kodai A Majeed ya fadama Mum ta cije shine, jin Mum tayi tana fadin aysha wannan irin tunani haka har in shigo baki san na shigo ba, dan Allah ki fadamin abunda ke damunki, ajiyan zuciya tayi tare da fadin babu komai Mum kawai dai ina tuna halin rayuwa ne, da yanda abubuwa sukan canza, Mum tayi dan murmushi tare da fadin hakane Allah babu yanda baya lamarin sa, sai yasa akeso bawa ya kasance mai godiya a duk halin daya sami kanshi, Allah yakan jaraba bawa ta hanyoyi da dama idan yayi hakuri ya dangana sai kiga Allah ya Kawo mai sauyi cikin sauki, indo wacce hawaye ya zubo mata a fuska tace hakane Mum sai yasa a kullum nake kara godema Allah daya hadani daku a rayuwa na, Mum janyota tayi jikinta tana fadin ki daina hawaye Allah ya fimu sanin dalilin haduwan mu duk da abunda ya hadamu ya raba mu amma Allah bai sa mun rabu ba har yau muna tare wanda zan so mu..... Dan shuru Mum tayi ba tare data karasa abunda take son fadi ba, indo jin tayi shuru ta dago ta Kalli Mum wacce idonta yake hawaye cikin tashin hankali indo take tambayan Mum lafiya kuwa? Mum rike ma indo hannu tayi tana dan murmushi ga hawaye kuma na zuba, tace aysha Allah yasa min sonki tun kafin in ganki tun lokacin dana ji labarin ki nake burin in taimaka miki, naso ace in kasance dake har abada domin nasan in A Majeed yana tare dake har abada muna tare sai mutuwa,dan shuru Mum tayi Kafin tace nasan nan bada dadewa za kiyi aure ki tafi gidan wani May be ma ya hanaki zumunci Dani, wani hawaye ya zubo ma indo mai zafi tare da fadin Mum har abada ke mahaifiya tace duk Mai sona dole ya soki,mum rungume indo tayi tare da fadin Allah ya miki albarka ya baki yara masu miki biyayya inga jikoki na, indo rufe fuska tayi ba tare data amsa ba, amma a zuciyarta ta amsa, mum tayi murmushi tare da fadin bari inje in duba A Majeed inga ko ya tashi, indo da mamaki take kallonta, Mum kaman tasan abunda take tunani tace nasa an kawo shi nan dan in kula Dashi, Indo cikin murya wacce ya dashe tace ya jikin nashi Mum tace da sauki, bayan fitan Mum ne indo tayi ta tunani akan maganganun Mum, tabbas abunda ta fahimta Mum har gobe tana sonta da dan nata, kai indo ta girgiza tare da fadin ba haka Mum ke nufi ba kawai tana son in yafe mai abunda yayi min ne da wannan tunanin indo tafi yarda dan haka ta tashi itama ta fita, motsi taji a kusa da dakin Mum din dan haka ta shiga Mum ce a ciki tare da A Majeed wanda yake kwance idonshi a lumshe kaman mai bacci amma idonshi biyu, kanshi ke mishi ciwo sosai ga zazzabin yaki sauka, Mum tace aysha inaga asibiti zamu gskya, jin an kira sunan wacce yake burin gani yasa ya bude ido a hankali, dai2 lokacin ta matso kusa da gadon idanshi a kanta yana mata murmushi, dakewa tayi domin irin kallon da yake mata yasa take jin wani iri, murya na rawa tace mai ya jiki?amsawa yayi da fadin kaina kaman zai fashe tanan gefen tare da nuna mata yana maganan ne dakyar, tashi tayi ta fita tare da cema Mum bari in duba shi, jim kadan sai gata da abun gwada VP, wayan mum ne yayi kara ta dauka tare da barin dakin, a hankali ta zauna gefen gadon tare da fadin Kawo hannunka,wannan ne karo na farko data mishi magana tunda ta dawo kasar, kaman dama jira yake ya mika mata jallabiya ne a jikinshi mai gajeran hannu ta daura abun a hannun lumshe ido yayi ga kamshin turarenta na dukan shi, idanta ya sauka a inda ta cijeshi domin taga shaidan hakori wani iri taji a ranta, jin muryanshi tayi yana fadin haka kike ma mutane a hspt kina taba su.......
Taku maryam obam😘
*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*
*NA*
*MARYAM ALHASSAN DAN'IYA*
*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*
*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*
*WWW.maryamobamnovels.com*
https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/
135to140
*DEDICATED TO....*
*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*
Indo da mum suna zaune a falon kasa, abdul ya shigo da sallama, duka Suka amsa da Fara'a, abdul ya gaida Mum cikin kulawa ta amsa da abdul har yanzu dai kana ta fama, dan murmushi yayi tare da zama, Mum taci gaba da fadin ni inaga daka hakura da yarinyar wlh ka auri wata nan gaba in Allah yasa matarka ce sai ayi, indo ce tace Mum niko nafi son ya auri yarinyar wlh saboda irin halin da take ciki, Mum tace hakane aysha taimako ne amma Abu yau wajan shekara biyar ana fama, indo ta danyi shuru can ta nisa tace niko Mum dan Allah inaso inje inga yarinyar, Mum kallonta tayi tare da fadin babu damuwa zan fadama Dad sai kusa rana, Abdul yaji dadin hakan sosai, masu aikin gidan ne suka Kawo ma Abdul Abun taba baki, ya kalli indo yace ya Office din? Indo tace Alhmdlh, wayan Mum ne yayi kara dauka tayi ban san mai ake fada mata ba naji tace gani nan zuwa, kallon abdul tayi tace wai A Majeed ne tun jiya daya shiga Gida bai fito ba, gashi matarshi bata nan shine driver dinshi ya kira, abdul yace bari inje in gani, mum tace muje tare, Bin abdul tayi akabar indo a gida wacce tunda taji hakan jikinta ya mata wani iri, daki ta koma ta kwanta tana jin wani iri.
Koda su Mum sukaje gidan a dakinshi suka sameshi ya lullube duk da AC din dakin a kashe yake amma yana ta rawan sanyi cikin tashin hankali Mum ta kira No Dr dinsu wanda yace mata gashi nan amma baya kusa zai dan kai nan da 30mnt,kwatancen gidan A majeed tamai sannan ta kashe, abdul fita yayi yabar Mum ita daya cikin tashin hankali tama rasa abunyi jin muryanshi tayi yana fadin aysha I love You come back to me I will treat you like a queen, shuru tayi tana mamaki, daukan wayanta tayi ta kara kiran Dr din yace yana hanya karta damu, Mum tace koh su Kawo shi hspt ne, yace ta bari ya kusa zuwa ba'a dade ba sai ga Dr din da abdul nan aka fara dubashi inda Dr ya mishi allura tare da bashi Magani, yace ma Mum a bashi abinci yaci, amma mai ruwa, mum da sauri ta hado mishi Tea cikin kitchen din da yayi kura dan Zainab ta Kori masu mata aiki sai dai wani lokacin ta kira azo a Mata shara duk saboda gudun kar a kara nanata abunda akayi da indo, mum rikoshi tayi tana bashi tea din jikinshi yadan fara rage zafi dan alluran da aka mai,mum ta bashi Magani yasha nan dr yama Mum sallama tace ya tsaya su tayata kama A Majeed din a sashi mota domin gidanta za'a kaishi hakan koh akayi aka kamashi suka nufi gidan mum din, sama akayi Dashi kusa da dakinta inda aka kwantar Dashi akan gadon dakin, idonshi a lumshe daka gani yana fama da ciwan sosai, Mum ruwa ta dibo tasa towel a ciki tana matsewa tana dan shafamai a jiki, lokaci daya zafin jikin ya sauka bacci ya daukeshi, Mum wani irin tausayin dan nata take ji, amma idan ta tuna abunda yayi sai taji ranta na baci, domin ya nuna mata baya son gatan da tamai, kun san d'a da uwa😢, dakin indo ta nufa wacce take zaune amma hannunta biyu akan fuskanta daka gani tunani takeyi domin har Mum ta shigo bata ji motsinta ba har saida ta kira sunanta, tayi firgit tare da tashi tana kakaro murmushi tana fadin sannu da dawowa Mum, mum amsawa tayi tare da zama akan gadon dakin ganin haka yasa indo ta zauna a kusa da ita, Mum tace aysha lafiya kuwa? Dam taji kirjinta ya buga kodai A Majeed ya fadama Mum ta cije shine, jin Mum tayi tana fadin aysha wannan irin tunani haka har in shigo baki san na shigo ba, dan Allah ki fadamin abunda ke damunki, ajiyan zuciya tayi tare da fadin babu komai Mum kawai dai ina tuna halin rayuwa ne, da yanda abubuwa sukan canza, Mum tayi dan murmushi tare da fadin hakane Allah babu yanda baya lamarin sa, sai yasa akeso bawa ya kasance mai godiya a duk halin daya sami kanshi, Allah yakan jaraba bawa ta hanyoyi da dama idan yayi hakuri ya dangana sai kiga Allah ya Kawo mai sauyi cikin sauki, indo wacce hawaye ya zubo mata a fuska tace hakane Mum sai yasa a kullum nake kara godema Allah daya hadani daku a rayuwa na, Mum janyota tayi jikinta tana fadin ki daina hawaye Allah ya fimu sanin dalilin haduwan mu duk da abunda ya hadamu ya raba mu amma Allah bai sa mun rabu ba har yau muna tare wanda zan so mu..... Dan shuru Mum tayi ba tare data karasa abunda take son fadi ba, indo jin tayi shuru ta dago ta Kalli Mum wacce idonta yake hawaye cikin tashin hankali indo take tambayan Mum lafiya kuwa? Mum rike ma indo hannu tayi tana dan murmushi ga hawaye kuma na zuba, tace aysha Allah yasa min sonki tun kafin in ganki tun lokacin dana ji labarin ki nake burin in taimaka miki, naso ace in kasance dake har abada domin nasan in A Majeed yana tare dake har abada muna tare sai mutuwa,dan shuru Mum tayi Kafin tace nasan nan bada dadewa za kiyi aure ki tafi gidan wani May be ma ya hanaki zumunci Dani, wani hawaye ya zubo ma indo mai zafi tare da fadin Mum har abada ke mahaifiya tace duk Mai sona dole ya soki,mum rungume indo tayi tare da fadin Allah ya miki albarka ya baki yara masu miki biyayya inga jikoki na, indo rufe fuska tayi ba tare data amsa ba, amma a zuciyarta ta amsa, mum tayi murmushi tare da fadin bari inje in duba A Majeed inga ko ya tashi, indo da mamaki take kallonta, Mum kaman tasan abunda take tunani tace nasa an kawo shi nan dan in kula Dashi, Indo cikin murya wacce ya dashe tace ya jikin nashi Mum tace da sauki, bayan fitan Mum ne indo tayi ta tunani akan maganganun Mum, tabbas abunda ta fahimta Mum har gobe tana sonta da dan nata, kai indo ta girgiza tare da fadin ba haka Mum ke nufi ba kawai tana son in yafe mai abunda yayi min ne da wannan tunanin indo tafi yarda dan haka ta tashi itama ta fita, motsi taji a kusa da dakin Mum din dan haka ta shiga Mum ce a ciki tare da A Majeed wanda yake kwance idonshi a lumshe kaman mai bacci amma idonshi biyu, kanshi ke mishi ciwo sosai ga zazzabin yaki sauka, Mum tace aysha inaga asibiti zamu gskya, jin an kira sunan wacce yake burin gani yasa ya bude ido a hankali, dai2 lokacin ta matso kusa da gadon idanshi a kanta yana mata murmushi, dakewa tayi domin irin kallon da yake mata yasa take jin wani iri, murya na rawa tace mai ya jiki?amsawa yayi da fadin kaina kaman zai fashe tanan gefen tare da nuna mata yana maganan ne dakyar, tashi tayi ta fita tare da cema Mum bari in duba shi, jim kadan sai gata da abun gwada VP, wayan mum ne yayi kara ta dauka tare da barin dakin, a hankali ta zauna gefen gadon tare da fadin Kawo hannunka,wannan ne karo na farko data mishi magana tunda ta dawo kasar, kaman dama jira yake ya mika mata jallabiya ne a jikinshi mai gajeran hannu ta daura abun a hannun lumshe ido yayi ga kamshin turarenta na dukan shi, idanta ya sauka a inda ta cijeshi domin taga shaidan hakori wani iri taji a ranta, jin muryanshi tayi yana fadin haka kike ma mutane a hspt kina taba su.......
Taku maryam obam😘
*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*
*NA*
*MARYAM ALHASSAN DAN'IYA*
*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*
*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*
*WWW.maryamobamnovels.com*
https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/
135to140
*DEDICATED TO....*
*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*