← Book details Rumfar Bayi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 6 OF 53

Sashe 6

Rumfar Bayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A tare suka mike bayan an aiko musu da sakon cewa za'a fara liyafar.
Khadija ta banka wa juwairiya harara.
Ke ina zaki?
'A hakan zamu tafi dake  ki sake tsorata ya jalal din?
Zainaba ta daure fuska,kinga khadija bana son shishshigi,abunda ya faru da dadewa shikenan kin din ga maimaita shi..

   Khadija tace haba zainaba,kalli fa shigar ta ki gani ga fuska kuma a kone..

Zainaba tabi juwairiya da kallo,ita bata damu da tabon dake fuskarta ba amma kayan ne ko irin su jakadiya ma da uwar soro da du'bu ai ba saka irin su sukeyi ba..

    Zainaba ta koma daki ta fito da wata jar atamfa...
Ta mikawa juwairiya amsa ki canza zuwa wadan nan..
Juwairiya ta ware ido ni?ta nuna kanta..

Khadija tace,da' wa?
idan ba ke ba uhm?
Juwairiya ta amsa a sanyaye sannan ta shiga ta sanyo kayan..

Tana fitowa sukabi ta da kallo...
Duk da dogowar riga ce a jikinta amma sai da shape dinta ya bayyana..

Ita kanta sai datayi mamakin irin dirin ta tunda dai bata taba saka kaya irin wannan ba...
ko kadan bataso ta saka kayan ba amma babu yarda zatayi tunda baza ta iya musawa hakan ba.

   Khadija ta tabe baki babu laifi... (nan kuwa kishi takeyi.)
Zainaba kanta sai data tsorata da ganin canzawar da juwairiya tayi amma ta da'ke tace muje...

'Wuri yayi wuri mutane kamar ba gobe..
Su khadija suka zauna a inda aka tanadar domin su..
Juwairiya kuwa ta koma layin yan uwanta bayi sai kalle kalle takeyi kada su ummanta su ganta da wannan shigar...

Wattpad @afreey101

[9/18, 3:13 PM] Aysha Galadima: *RUMFAR BAYI*
(A historical fiction )
Na Afrah bhai
Page 7
Wattpad @afreey101

******************************

"Ta'ro yayi taro anci an'sha anyi kuma wasanni sosai..
' sai wuraren karfe goma na dare sannan aka tashi,an kai amarya sashen ta dayaji gyara cikin tsari na gargajiya.

     'Surayya an sha wanka cikin turare ga turaren jiki kuyangin nayi mata kamshi kam ba'a mgn.
    Wata riga ta saka marar nauyi sannan aka daura mata alkyabba mai kyan gaske..
    Tana nan a zaune bayinta na ta kara gyara cikin dakin sai ji sukayi ana sanar da shigowar yarima.
Ta kallesu fuskar nan ba a daure tace,ku fita duka!
Jiki na rawa duk suka fice da saurin su..

  'Da sauri Ta sake gyara fuskarta tana kokarin rufe fuskarta taji shigowar ango..

'Yarima cikin kasaita ya karasa gaban gadon yana bin'ta da kallo...
ya rasa dalilin daya sa mahaifiyar sa ta matsa masa akan ya amince da auren wannan yarinyar..
'shi dai yasan ko'da ya fara ganinta lkcn da mai martaba ya matsa masa akan yaje zance dan su fahimci junansu kwata kwata batayi masa ba..
Tunawa da wannan kyakkyawar fuskar da ya gani dazu yayi,wacece ita?a ina kuma zai sake ganin ta?

'Surayya dake lullube taji wani irin haushi ya turnike ta,
miye haka zai wani shigo ya zauna shiru kamar ya manta da anyi ajiyar ta..mtsw....

    Ni kike wa tsaki...?
Taji an fada da murya me cike da gadara da kasaita..
Ware ido tayi dan kuwa duk a tunaninta a cikin zuciyarta ne tayi tsakin..
   Shiru tayi masa tana runtse idonta..
Yarima ya mike tsaye..yace...
'Naga alamar tun ba'a kai ko ina ba kin fara raina ni ko...

'Surayya tayi shiru tana jin haushin kanta data bari har tsakin ta ya fito fili..
Yarima yaja gundun tsaki,sannan yace bana mgn kana shareni kin gane?..
Surayya tace a sanyeye, kayi hakuri..
Ya sake tabe baki,
bude fuskarki...
Ta saka hannu a nutse ta yaye lullubinta...
   Yarima dake tsaye agabanta ya kura wa fuskarta ido..
Ko kadan baiji kwatankwacin abunda yaji dazu ba..meyasa?

Yadan ja tsaki..
Ya sunanki ma?
Surayya taji wani irin abu ya tukare mata wuya,mai?miye sunanta?dama bai san sunanta ba kenan?amma ai koda sukaje gidansu ta tabbata yaji sunanta..

'Tadan daurefuska, baka san sunana ba ashe..
Yarima ya shafa sa'jen dake kwance a fuskarsa..
  Tambaya kike?ko mamaki kikeyi?
Surayya ta dan murmusa idan nace duka biyun banyi laifi ba..?

  Yarima daya so gundura da mgnr yace..
Bana son ana maida min tamabaya ta da wata tamabayar..

Surayya tadan tabe baki,lallai wannan mutumin akwai son mulki..
Sunana SURAYYA...ta fada tana kafe shi da ido..

Yadan gyada kai,toh surayya dan matsa min na kwanta nima yayi mgnr yana karasawa gefen gadon..
'Surayya haushi ne ya kama ta,wane irin daren farkone haka ta matsa mishi? bashi ma da niyyar yin komai ma kenan?ita dai ba haka taji ana fadin daren farkon ba...
tana kallonshi ya rage kayan dake jikinsa yazo ya tsaya yana mata nuni da ido irin ke nake jira dinnan..

'Surayya taja gefe da sauri yarima ya hau ya kwanta yana runtse idonsa..

Duniyar tunani ya tafi,meyasa yake jin hakane?kodan baya son yarinyar ne?yadan bude idonsa,yasan cewa gobe dole ne gimbiya kilishi ta turo a duba mata ko wani abu ya shiga tsakanin sa da surayya tunda haka al'adar take,ya sake runtse ido,baya jin ze iya kwanciya da yarinyar can a yau, tunani kawai yakeyi har  barci me dadi ya dauke sa cike da mafarkin wannan kyakkyawar  fuskar daya gani..... .

********
'A wajen juwairiya kuwa,bayan taro ya tashi suka taho tare da zainaba,suna tafiya juwairiya taji kamar takon wani a bayansu,ta kalli zainaba a tsorace itama kanta zainaba haka jikinta ya bata,da sauri juwairiya ta jawo zainaba suka boye bayan wata bishiya,zainaba tayi kasa da murya..
  Waye yake bin mu?
Juwairiya ta girgiza kai nima ban sani ba ranki ya dade..

Zainaba ta matse hannun juwairiya cikin nata tace..
Yanzu ya zamuyi ? mun shiga uku...
Juwairiya ta jawo wani itace ta rike tana jira wanda ke bin nasu ya karaso wajen ta buge shi...

       Tafiya yake yi yana waige waige yan matan daya biyo daga wajen taro yake nema ina suka shiga ne?
     Baiyi aune ba sai dai yaji saukar itace a bayansa...

  Matse bakinsa yayi ya juyo yana musu kallon mamaki..
Gaba daya jikinsu rawa yakeyi..
Zainaba ce tayi saurin cewa..
Waye kai?meyasa kake bin mu?
Mustapha ya daga hannunsa irin surrender dinnan yace..
Kuyi hakuri yan mata dama zuciyata ce kuka taho da ita shine nake binku domin an amso ta..

Kallon juna sukayi,juwairiya ta shiga gaban zainaba wai ita nan tana kare tane..
Tace,malam kasan kuwa dawa kake mgn,gimbiya zainaba ce fa DIYAR SARKI kuma uwar dakin juwairiya...
Mustapha yace,madalla yanzu zan dan samu nutsuwa tunda na ji sunan masoyiyar tawa ZAINABA....yaja sunan yana lumshe idonsa..

Da kallo suka bishi..balle zainaba dake ta lekowa tana karewa fuskar shi kallo..
Kyakkyawa ne ,chocolate color kuma yana da tsayi sosai se de siririne..
    Juwairiya zatayi mgn zainaba ta dafa ta..

Mustapha yace,gimbiyata Allah yasa wani bai min shigar sauri ba ko,ya fada hade da karkace kansa..
Zainaba bata san lkcn da murmushi ya subuce mata ba sannan ta girgiza masa kai cike da kunya ta juya da gudu tayi gaba..
Juwairiya cike da mamaki tabi bayanta..

*************
'Da safe juwairiya na gani zaune laure na mata kwan'tar(tsifar)kai..

Laure tace,kedai yarinyar nan anyi kazama wlh kitso se ki barshi har kusan wata daya,gashi Allah ya baki gashi amma kwata kwata bakya kula dashi.. wai ni yaushe rabon ma da ki wanke shi ne?

Laure jin ita kadai keta zancenta yasa tadan kai mata duka..
Bakya jina ko?
Juwairiya ta kai hannu wajen da laure ta duke ta,ta turo baki haba goggo laure ina jinki fa wlh.
Laure tace karya kike,wai tunanin menene kikeyi ne haka?

Juwairiya tace babu komai,sai kuma ta mike da sauri tana kwace kanta daga hannun laure..
Goggo laure ina zuwa,ta shiga daki tayi shirin ta ta fito da gudu tayi hanyar sashen zainaba...

Tana shiga ta tarar da ita a tsaye,da sauri ta karasa wajenta lafiya ranki ya dade?..
  Zainaba ta sauke ajiyar zuciya yauwa dama ke nake ta jira,zauna..kiji....

Juwairiya ta zauna tana saurarenta.
Zainaba tace,dazu wannan saurayin ya turo min da wasika..

Juwairiya ta saki murmushi me yace ranki shi dade nasan dai da gani sonki yakeyi..ko?
Zainaba ta rufe fuska wai haka yace..

Juwairiya tayi dariya kasa'kasa dan ta lura uwar dakin tata ma ta fara zurmawa dayawa..
Zainaba ta gyara zamanta sannan ta buga tagumi,amma kinsan me yace?

Juwairiya ta gyara zaman itama ah ah se ranki ya dade ta fada min.
Zainaba ta turo baki..
Wai idan na amince masa toh naje da Fure (flower) na same sa a zaure na biyu yana jirana kafin su tafi..

   Juwairiya tayi murmushi, kada ki damu ranki ya dade akwai wani fure me kyau dasu yasira ke cirowa zan samo miki shi..
Zainaba tayi murmushi, yauwa juwairiya yi maza kije toh..
Juwairiya na murmushi ta mike ta fita..

"Sashen hamza ta nufa dan anan ne yasira ke aiki,ta jawo ta waje ta tambayeta ina ne take ciro furen?
Yasira tadan waro ido,juwairiya yaushe rabon da ki ganni da wannan furen?yanzu fa kinsan an tare sashen..

Juwairiya tace,wai dama sashen waye?
Yasira tace,sabon sashen matar yarima jalal ne..
Juwairiya hakanan taji gabanta ya fadi,ta juya kawai tayi gaba..

Tsaye tayi a kofar shiga sashen,tunani takeyi ko ta shiga ko kada ta shiga,bata son ko kadan ta hadu da wannan yariman...
   Leke tayi karaf ta hango itaciyar furen kuma akwai dayawa a jiki...
  Taja lumfashi sannan kai tsaye tayi wajen tana waiwayen bayanta..

*************
Yarima jalal ne na gani a tsaye gaban surayya dake ta kwasar baccinta a takure.
Ya kura mata ido ko tunanin me yakeyi oho..
Haske ya gani yana ratsuwa dakin daga window yana taba fuskarta..

  Juyawa yayi yazo gaban window din yana kokarin rufe labulen ya hango ta..

  Dauke kai yayi da sauri dan kuwa konannen sashen fuskarta yaci karo dashi ,zuciyarshi yaji ta baci,ya tsani yarinyar can baya son ganin irritating face dinta ko kadan,duk da ze iya kirga ganin ta da yayi a masarautar..

   Ya juya kawai ya fito a fusace dan bai ga me ya kawo ta sashen ba..
   Yana fitowa bayin dake tsaye bakin kofar suka shiga gaisar dashi..
Bai amsa musu ba kawai yayi waje abunsa..

******
Juwairiya ta ciro furen daya mai kyau sosai..
takai hancinta tana shakar kamshinsa me sanyi..
Ta tabbata dole ne zainaba ta yaba mata idan taga turen..
Har ta juya zata fice taji ance..

    Me ya kawo ki nan!
Chapter 6 · 0% Book details