← Book details Rumfar Bayi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 24 OF 53

Sashe 24

Rumfar Bayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Runtse ido yayi dan sai yanzu ya tuna da cewa ba kayan sa bane a jikinsa..
Juwairiya ta waro ido tana kasa da murya tace..
Badai baka fito da kudin ba?
Jalal ya gyada mata kai yana cije lebensa..
Juwairiya ta dafe goshi tace, yanzu ya zamuyi kenan?

Jalal ya kalli zobunan dake hannunsa a jere ya ciro daya daga ciki ya mika mata..
Ki biya shi da wannan dan na tabbata kudinsa kawai ze iya siyen daya wajen nan sau biyar..

  Juwairiya ta saki baki tana kallonsa..
Jalal Ya juya da kansa ya mikawa mutumin zoben sannan ya karasa wajen wani kututturen itace ya zauna..
Juwairiya ta juya wajen me siyar da kifin tace masa..

Malam Ka ajiye min zoben can gobe zan kawo maka kudinka na amshe shi..
Me kifi ya daure fuska a take.. dan shi kam har ya hau murna yayi kudi a dare daya..
Cikin haushi yace..Toh dai idan baki zo da wuri ba ki sani siyar dashi zanyi..
Juwairiya tace zan ma zo din ka ajiye min...

"Tsayawa tayi tana kallon yarda yarima ke cin kifin...cike da yanga yake tsakurar shi..
Baki ta tabe,ji abunda aka fito siya tunda masarauta amma kalla yarda yake cin sa..

  Jalal ya dago yace,magana kike?
A take ta daburce dan a tunanin ta acikin zuciyarta ne tayi mgnr..ni ni bance komai ba ranka shi dade..

Jalal ya nuna mata kusa dashi yace zauna..
Ta zauna babu gardama..
Takardar kifin ya ajiye a kan cinyar ta yace..
   Ciyar dani...
Ta waro ido..
Shima din yayi yarda tayi..
Wato ya waro idon shima yace..
Na ga ai kin fi ni sanin yarda ake cin sa ko?

Juwairiya tayi wiki wiki da ido..
Baki ya bude yana mata nuni da ido akan ta fara aikinta..
Juwairiya ta sauke lumfashi kafin ta saka hannu ta ciro tsokar kifi ta cire kayoyin sannan ta hada da dankalin ta kai bakinsa ta tura..
Ware ido yayi ganin ta cika masa bakinsa tab..

juwairiya tace,ka cinye ranka shi dade yafi dadi a haka,ta dage masa girar ta daya..
Jalal ya fara ci yana lumshe ido..
A haka tayi ta basa har ya daga hannu yace ya koshi..

Tana shirin cire hannunta daga cikin kifin yace..
Kema kici..
Ta girgirza kai,duk da itama din tana dan jin yunwar..
Jalal ya daure fuska..
Umarni ne..!
Ta gyada kai sannan ta fara ci itama,ya tsare ta da ido..

"Sai cikin dare sosai suka dawo cikin masarautar..
   Juwairiya taga yayi hanyar rumfar bayi..
Da sauri tasha gabansa tace..
Ranka shi dade ai dare yayi sosai kawai ka koma sashen ka..

Jalal ya kura mata ido..kafin yace..
Yaushe kika zama bai bani shawara ?
Juwairiya ta matse bakinta..
Yace wuce muje..
Ta gyada kai suka hau tafiya...

"Suna kawowa kusa da rumfar bayi yaja burki..
Juwairiya ta kallesa..nagode ranka shi dade..
Jalal ya jinjina kai,har ta fara tafiya sai jitai yace..

"Kada kije kina mamakin me yasa sarki guda zai jaki kuje kifi a waje..
  Juwairiya tayi saurin juyowa tana kallonsa...

Ya dauke kai yana ci gaba da cewa..
"Tun ina karami nake kwadayin naci kifin wajen nan watarana,amma ban samu damar hakan ba sai yau..
Juwairiya ta saki murmushi tana shirin mgn ne sukaji muryoyin bayi suna shirin fitowa..

  Ai da sauri juwairiya ta janyo sa suka boye bayan wani kango...

Jalal ya kura mata ido ganin yarda ta matse shi ajikin bango tana lekawa taga ko bayin sun wuce..
   Wani irin shock ne yakeji a gaba daya jikinsa..
Ya kurawa gefen fuskarta ido..

Juwairiya kuwa ganin bayin lekowa sukayi kawai suka koma ciki sai ta sauke ajiyar zuciya me nauyi..

Ina zata iya bari wani ya ganta da sarki jalal!?tab bazata taba bari asirin su ya tonu ba..
Ta dago da kanta..

Sai gani tayi fuskokinsu sunyi dab da juna har tsinin hancinsu na gogar na juna..
   Gabanta ne ya shiga faduwa..
Dama haka ta matse shi?wayyo...
Ai da sauri taja baya tana kasa da kanta..
Jalal ya murmusa kafin yabi ta gefen ta ya fice......

******************
"Surayya ta kalli umaymah tana damke hannayenta cike da tsananin bakin ciki da fusata.
   Na tabbata wani ne ya saka a batamin girkina!kuma wlh wlh bazan yafewa ko wanene wannan ba,ni surayya bana barin bashi!

Umayma ta dafa kafadarta,ranki shi dade kema ai kin san wacece zata iya yi maki irin wannan katobarar.. ina kyautata zaton gimbiya khadija ce....
Surayya ta gyada kai,lallai dole ne na koyawa wannan yarinyar hankali!!dan ta gane ni ba abokiyar yin ta bace!!!

**************
Washe gari...

"Juwairiya gaba daya tunda ta tashi daga barci take cikin farin ciki ..
Hansai ta lura da hakan dan haka tace,lallai diyata wannan murna haka meya farune ?

juwairiya ta murmusa,bata taba yin barcin me dadi irin na jiya ba..
Girgirza kai kawai tayi tace,umma babu komai wlh,kinsan haka Allah ke ikon sa watarana se kawai kaji ka tashi da farin ciki..

Hansai ta rungume ta,Allah ya baki duk farin cikin dake cikin duniyar nan diyata..juwairiya tayi dariya kema haka ummana..

***************
"Tana fitowa daga cikin rumfar bayi tayi hanyar sashen zainaba dan ta gaishe ta kafin tayi reporting wajen aikinta..

Tafiya kawai takeyi cike da murnarta har bata lura da turaki da hamza dake tsaye a gefen hanyar ba..
   Turaki ya kura mata ido tun kafin ta karaso wajen da suke..
Ga mamakin sa ko kallon inda suke batayi ba bare ma ya saka ran ta gaishe su..

      Hamza ya kalla yace,kayi gaba kawai ina zuwa...
Bayan juwairiya yabi yana mamakin me ya dauke mata hankali har haka...
Sai da suka kawo kofar shiga sashen zainaba sannan ya jira sunanta..

"juwairiya. ...
Ta juyo tana kallonsa da mamaki..kafin tace ranka ya dade ina kwana?

Ya murmusa lafiya lau,yau kin kawo wa kawar taki ziyara kenan?
Juwairiya ta gyada kai..
Yace toh yayi kyau,sannan ya juya ya fice yana sakin murmushi..

Juwairiya ta shige ciki da murnar ta..
   Zainaba ta tarar ta tule kaya a gabanta zabba'u na gyara mata linkinsu ..
Tana ganin juwairiya da murna ta tare ta..
Sun gaisa sosai kafin juwairiya tayi mata sallama ta fice...

******************

"Koda ta shiga sashen sarki jakadiya ce ta tsayar da ita akan surayya na nan cikin dakin jalal..
ta jira sai ta fita sai ta shiga ta gyara..
    Wani abune ya tokare mata makoshi,ta fito waje ta zauna a waje gaba daya duk farin cikin data fito dashi ya gushe...

*************
  "Sarkina ba zaka tashi haka nan bane?
Surayya dake zaune akan gadon jalal tana shafa kirjinsa ta fada cike da kissa..

   Yarima ya gyara kwanciyarsa barci ne sosai a idonsa kasancewar  bai kwanta da wuri ba jiya..
Cikin kasalalliyar murya yace..
Surayya ki fita ki bani waje mana,nace miki barci nakeji ko?
  Surayya ta tabe baki...tana tunanin a ina umayma ta tsaya?

**********
"Juwairiya na waje umayma ta shigo sashen dauke da tire ta rufe shi da wani dan kyalle..
   Juwairiya ta kalleta, su umayma manya..
Umayma ta washe baki,lah juwairiya ai ban lura dake bane ma,wai ni jiya ina kika shige ne da daddare ?
ta karashe mgnr cike da son jin gulma,
dan ta nemi juwairiya jiya a Rumfar bayi bata ganta ba..
juwairiya taji gabanta ya fadi..
Ina fa zanje?dare yayi sosai ina dakin du'bu tare dasu goggo laure..
Umayma tayi murmushi a zuciyarta,
lallai wannan yarinyar ita zatayi wa karya?har fa dakin du'bun ta shiga bata ganta ba,amma a fili sai cewa tayi..
  Allah sarki bari na shiga uwar dakina na jira..

***********
Jakadiya ce ta shiga dakin jalal ta sanar ma surayya zuwan umayma..
Murmushi tayi a zuciyarta..
Sannan ta mike ta falon..
Umayma ta cire kyallen data rufe tiren data shigo dashi..
Glass cup ne cike da fresh milk..
Surayya ta amsa tana kallonta..
Kinyi yarda nace..?
Umayma ta gyada kai..
Surayya tayi murmushi sannan ta koma cikin dakin da tiren a hannunta ..

   Ajiye tiren tayi a kan wani dan karamin table sannan ta koma kan gadon jalal ta kai bakinta saitin kunnensa tace..

Sarkina ga madara can na ajiye maka ,idan ka tashi dan Allah kasha kaji?
   Jalal cike da zakuwar tafiyar ta daga dakin yace..
Naji...
Ta murmusa hade da kai masa sumba a goshinsa sannan ta mike ta fita tana addu'ar Allah yasa yasha madarar..
Dan dolene itama ta zama wulakancin da khadija tayi mata..

****************

_"Ni kuwa nace kome surayya ta shirya oho...."_

Muje zuwa 👇
TEAM RUMFAR BAYI
[9/18, 3:22 PM] Aysha Galadima: *RUMFAR BAYI*
(A historical fiction)
Na Afrah bhai
Page 25
Wattpad @afreey101
*Pls do visit n vote Me*

_This page is for you TEAM RUMFAR BAYI groups..😍_

******************

"Surayya na fitowa daga cikin dakin ta jawo umayma gefe tace da ita....
ki samu waje ki tsaya a nan har sai kin tabbatar min da jalal yasha wannan madarar kina ji?...
Umayma ta gyada kai kada ki damu ranki shi dade(ur wish is my commad) ...

Surayya tace yauwa, sannan ta nufi hanyar fita..
A nan ta hango juwairiya a zaune ta takure..
Ta watsa mata harara tayi gaba..
Juwairiya ta girgiza kai kawai tabi bayanta da kallo..
     sai ga Jakadiya tazo tayi kiran ta bayan fitar surayya da minti kusan talatin..

    **************
A hankali ta shiga dakin tana kare masa kallo..
Idonta ne yakar kan gadon..
A can ta hango sa ya takure waje daya yana ta barcinsa..

Me yasa jakadiya tace ta shigo bayan jalal din ma bai tashi ba..
Har ta juya zata fita sai kuma ta dawo da sauri ta je gaban gadon ta tsaya..
    Kirjinta na bugawa ta kurawa fuskarsa ido tana tunanin me yasa zuciyarta take son ta kai ta inda aka fi karfin ta ne...juwairiya jalal yafi karfin baiwa kamar ki...

   Taja lumfashi....zata juya ta fita kenan..
Sai Ganin wani kwaro tayi yana shirin hawa kan jikin jalal..dan har ya haye kan abun rufar sa..

Da sauri ta kai hannunta wajen ta kore masa shi..
Tana shirin gyara tsayuwarta ne kawai taji tayi losing balance dinta ta fado a kansa tim!

"Jalal ya farka a fusace yana fadin..
Surayya wai me nace miki ne huh!
Ga mamakin sa sai ganin juwairiya ce saman jikinsa tana mutsu mutsun tashi..gabanta nata faduwa..
Chapter 24 · 0% Book details