Sashe 36
Rumfar Bayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ammi da kanta ta shiga cirewa juwairiya kayan jikinta..
Juwairiya ta runtse idonta gam tana mamakin abunda ammi ke aikata mata babu ko kunya ta tube ta tas ta barta da yar shimin dake jikinta..
Ban daki suka shiga,ammi ta umurce ta data shiga cikin bahon wankan dake cike da ruwa me dumi sai kamshi yakeyi..
Juwairiya gaba daya girman/kunyar ammi takeji kuma har zuciyarta tana jin kaunar matar..
Batayi mata musu ba ta shige ciki..
Ammi da kanta da shiga wanke juwairiya tana bata labarai da suka danganci masarautar su..
Juwairiya gaba daya ji takeyi kamar mafarki takeyi...
Tasha mamaki sosai ganin Anyi mata wanka yafi kala biyar..
Data fito daga wannan ruwan ammi ta fita ta kirawo su marka su hada wani..
Ta wanko iya wankowa..
A take kuwa fatar jikinta ta canza..
Tayi wani irin fes da ita..
fatar ta tayi wani irin haske,gashin kanta sai baza kamshi yakeyi..
Tana fitowa daga baton ammi ta nade ta cikin bargo mai kauri ta saka marka ta dauke ta cak dama ita ba wani nauyi ba..
A saman gadon ammi marka ta ajiyeta..
Ammi ta kalli marka..
Kije can MA'DINKA(wajen tailors)ki fada musu inaso suyiwa juwairiya kaya yanzun nan ki kawo min,marka tace toh ranki ya dade sannan ta fice..
Ammi ta zauna a gefen juwairiya tana hada mayuka masu shegen kamshi tace..
Ina so ki daina jin kunyata juwairiya,ni kakar kice babu wata kunya a tsakanin mu kinji?..
Juwairiya ta gyada kai tana murmushi..
Sallamar wasu yan mata guda biyu ne ya katse su..
Ammi na jin muryar su tace..
Ku shigo ciki yan matana har an taso daga makarantar ne?
Yan matan suka shigo ciki...Ammi kin san ko...
Mgnr ce ta tsaya musu a makoshi ganin juwairiya da sukayi akan gadon ammin su..
Kallon kallo suka shigayi wa juna..
A tare sukace..
Ammi a ina kika samo me kamar dake haka (her look alike)
Ammi tayi dariya, diyarku ce..
Cikin murna suka haye kan gadon suma suna saka juwairiya a tsakiyar su..
juwairiya dai da kallo kawai take bin su..
farare ne kamar ammi amma da ganin su zaka gane yan biyu ne da suna kama da juna..
Ammi na dariya tace..
Juwairiya wadan nan sune Autaye na,ga hassana ga kuma hussaina..
Juwairiya tabi su da kallo..
Hassana ta shafa fuskar juwairiya, diyar mu na kama da Ammi sosai..
Husssaina tace,sosai ma kuwa..
Ammi ta mike tana fadin,toh ku shirya min Jikata na bar muku wuka da nama a hannunku.
Murna sosai suka shiga yi ....
Ammi ta fice tana sanar musu marka zaka kawo kayan juwairiya..
"Sun gama shirya juwairiya cikin kaya na alfarma ba karamin kyau tayi ba,zan iya ce muku kamar an canzo mana juwairiya ne dan gaba daya (transforming)tayi..kamar ba juwairiya BAIWAR RUMFAR BAYI ba..
"Jama'ar gidan ne suka shiga shigowa ganin ta,ana ta taya ammi da murna..
Ammi kam baki bar kunne..
Hassana da hussaina kuwa suna makale da ita..
Khaleed ma sai da ya shigo,ya wara ido yana kallon juwairiya yace..
Ammi wacece wannan haka?
Ammi tayi dariya,diyarka ce mana..
Hassana tace,ya khaleed kaga yarda juwairiya ke kama da ammin mu ko?
Khaleed yayi dariya na gani sarkin surutu..
Juwairiya ta dago tana kallon khaleed, wai dama wannan mutumin kawun tane?
Khaleed ne ya kashe mata ido..
Yadai kina mamaki ko?
juwairiya tace ni gani nakeyi ma kamar mafarki nakeyi..
Ammi ta kamo hannunta tace..
ba mafarki kikeyi ba juwairiya duk abunda ke faruwa dake a yanzun GASKE NE.....
Juwairiya ta saki murmushi me cike da farin ciki...
Lallai dole ta gode wa Allah daya bayyanar mata da ASALINTA.....
Team RUMFAR BAYI
*RUMFAR BAYI*
(A historical fiction)
Na Afrah bhai
Page 33
Wattpad @afreey101
***************
"Washe gari...
"Mai martaba sarkin zazzau ya dawo daga tafiyar sada zumuncin daya tafi..
Labari ne mai dadi ris'ke sa na bayyanar diyar zarah'u...
Bai ma san wane irin farin ciki zayyi ba, bai bata wani lkc ba ya saka akayi masa Ammi..
Ammi da kanta ta saka su hassana su shirya juwairiya tsab sannan suka nufi bangaren na mai martaba..
Juwairiya har cikin zuciyarta take jin dadi sosai zata ga kakanta kuma mahaifin ummanta ta gaskiya..
"Sun tarar dashi a zaune saman kujerar sa ta karfe a cikin dakinsa..
Tsoho ne da zaikai shekaru kusan tamanin haka,amma ba zaka taba cewa mijin Ammi bane dan kuwa ta fishi jikin yarinta sosai..tunda dai ya girme mata nesa ba kusa ba..
"Tunda suka cikin shigo dakin sarki ya kurawa juwairiya ido yana kallonta cike da al'ajabi...
Tabbas wannan jinin diyar sa ce zarah'u ..
Da hannu yayi mata alama dataje garesa..
Ammi juwairiya ta kalla..
ta gyada mata kai tace kije juwairiya..
Ta taka har zuwa gabansa sannan ta duka kasa ta gaishe sa cike da girmamawa..
Hawaye ne suka cika masa ido..
Sai yanzu yake mugun dana sanin abunda ya aikawa diyar sa..
Ya shiga shafa kanta hannayensa na rawa haka ma lebensa...
Yace...
Asma'u (AMMI)
Ina godewa Allah daya bayyana mana jinin fatima muka ganta tun muna da sauran lumfashi a duniyar nan.
ina farin ciki sosai dana samu ganawa da ke...
ya fadi yana dago dakan juwairiya, hawaye itama takeyi sosai..
Ammi ta zauna tana fadin..
.. (note an sanarma sarki lbrn juwairiya duka)
Ba lkcn zubar da hawaye bane wannan,lkcn farin ciki ne da gode wa Allah...
Sannan kuma lkcne da zamu sanar ma juwairiya labarin mahaifiyar ta..
Mai martaba ya gyada kai,cike takaicin rashin zarah'u da sukayi yace,hakane dole ne mu sanar dake Wacece FATIMA wato ZARAH'U mahaifiyar ki....
*******************
*Masarautar zazzau A shekarun baya da suka gabata*..
"Zarah'u itace diya ta farko da Ammi ta fara haifa tun bayan auren su da mai martaba..
yarinya ce mai saukin kai da tausayin gaske gashi bata da wani hayaniya ko kadan,bazaka tabajin tayi fada ko gardama da wani ba..
Ta taso ne cikin so da kaunar mutanen dake cikin masarautar nan..
Dan Ko ina a cikin masarautar nan shiga takeyi tun tana yar karamar ta dan haka babu wanda bai santa ba..
"Zarah'u na da shekara sha bakwai mane ma aurenta sukayi mana caaaa..
Tunda ga yayan yan uwanmu zuwa masu kudin kasar mu..
"hakan kuwa ba karamin tashin hankali ya saka mu ba dan kuwa munyi wa zarah'u alkawarin zamu bata damar zabar mijin da zata aura..
Kuma a wannan lkcn ma a yarda na lura da ita ba auren bane a gabanta karatun da takeyi shi ta saka a gaba..
Ana cikin haka ne kuma sai muka riski ziyara daga sarkin kanon dabo a lkcn daurin auren garba..
Mai martaba ne yayi kiran dukka iyalensa dan gabatar dasu ga sarki ABU-TURAB...
Duk muka hallara a cikin babban falon mai martaba dan gaisawa da babban bakonsa..
Amma banda zabba'u wacce take can bangaren kakarta suna shan firarsu..
Marka ce na aika dan ta sanar da ita neman gaggawar da mahaifinsu keyi mata...
Zabba'u da gudunta ta shigo falon da sallama..
Kallone ya koma kanta..
A lkc guda kuma ta shiga zuciyar sarki ABU-TURAB farat daya....
Bayan mun gama gaisawa ne da sarki duk muka tashi muka fice dan basu waje..
Sarki ya kalli mai martaba yace..
Takawa Duk wadan nan yan matan yaranka ne?
Mai martaba ya gyada kai yace,duka yarana na ne ni na haife su..
amma zarah'u ce karama ce a cikinsu duk da tafi su jikin girma...
Sarki abu-turab ya jinjinar da kai kafin yayi sallama da mai martaba suka kama hanya..
Sati daya da zuwa ziyarar shi sai ga waziri da wambai sun sake sauka a kasar zazzau...
Munyi mutukar mamakin ganinsu dan basu aiko mana da wasikar zuwan nasu ba..
Mai martaba ya saka akayi musu tarba mai kyau suka ci suka sha kafin aka sake zama dan a gaisa..
Waziri bayyi kasa a gwiwa ba ya sanar da mai martaba sakon sarki abu-turah...
akan sunga IRI a cikin gidan sa kuma suna so..
Murna sosai mai martaba yayi dan kuwa yayi wa AMINA sha'awar abu-turab din..
Yayi murmushin su na manya yace..
Toh madallah ai babu wata matsala tunda akwai dangantaka mai karfi ta zumunci a tsakanin mu..
Waziri da wambai sukayi farin ciki sosai sannan cike da murna suka koma kasar kano...
Bayan sun sanarwa sarki abu-turab amincewar mai martaba ba karamin dadi yaji ba..
A take kuma yaje ya sanar ma mahaifiyar sa HAJJO..
Itama din taji dadi sosai dan kuwa tana mutukar son dan nata ya karo aure sbd irin rikicin da suke samu a wajen matar sa ta faro HINDU...
"Bayan wata daya ta shude sai ga sarki ABU-TURAB ya sake kawo mana wata ziyarar amma a wannan karon Zance ne ya kawo sa na Aure..
Mai martaba ya tare shi cikin murnar sa ya kuma saka YAYA BABBA (kishiyar ammi)ta shirya AMINA dan su dan gana da abu-turab din..
A can falon baki inda ya sauka aka shirya musu wajen da zasu kebe dan fahimtar junan su..
"Lkcn da amina ta shiga falon abu-turab ya kyalla ido ya ganta sai ya mike da sauri yana kiran waziri dake waje...
Ya nuna amina yace,ba wannan bace nake so..
Waziri mamaki ne ya kamasa..
cikin Fa'da suka koma a nan abu-turab yake sanarma mai martaba shi ba amina ce yake nufi ba wata ce daban..
Mai martaba yayi mamaki dan kuwa a lkcn yan matan gidan duka basu fi guda uku ba..
HAJIYA (kishiyar ammi ce itama )ya sake sanar ma wa akan a shirya BILKISU ta zo fada yana nemanta..
Bilkisu na zuwa abu-turab ya sake cewa ba ita bace..
Sai lokacin ne hankalin mai martaba ya tashi,dan kuwa yasan ba kowa bace abu-turab yake mgn face ZARAH'U ...
Jiki a sanyaye ya saka aka zo aka sanar min dana shirya zarah'u taje fada..
Nayi mutukar mamaki sosai sannan kuma hankalina ya tashi..
A haka na matsa mata ta shirya ta tafi..
Tana shiga Abu-turab yace ai itace yake mgn,shi itaa yake so a basa..
Mai martaba ya rasa yarda zayyi gashi kuma yayi musu alkawari tun da farko akan cewa ya basu..
damuwa sosai ne ya shiga dan ba'asan sarki da mgn biyu ba..
Bayan su abu-turab sun koma kasar su akan zasu dawo dan a saka ranar biki..
mai martaba ya same ni dan neman shawarata..
Juwairiya ta runtse idonta gam tana mamakin abunda ammi ke aikata mata babu ko kunya ta tube ta tas ta barta da yar shimin dake jikinta..
Ban daki suka shiga,ammi ta umurce ta data shiga cikin bahon wankan dake cike da ruwa me dumi sai kamshi yakeyi..
Juwairiya gaba daya girman/kunyar ammi takeji kuma har zuciyarta tana jin kaunar matar..
Batayi mata musu ba ta shige ciki..
Ammi da kanta da shiga wanke juwairiya tana bata labarai da suka danganci masarautar su..
Juwairiya gaba daya ji takeyi kamar mafarki takeyi...
Tasha mamaki sosai ganin Anyi mata wanka yafi kala biyar..
Data fito daga wannan ruwan ammi ta fita ta kirawo su marka su hada wani..
Ta wanko iya wankowa..
A take kuwa fatar jikinta ta canza..
Tayi wani irin fes da ita..
fatar ta tayi wani irin haske,gashin kanta sai baza kamshi yakeyi..
Tana fitowa daga baton ammi ta nade ta cikin bargo mai kauri ta saka marka ta dauke ta cak dama ita ba wani nauyi ba..
A saman gadon ammi marka ta ajiyeta..
Ammi ta kalli marka..
Kije can MA'DINKA(wajen tailors)ki fada musu inaso suyiwa juwairiya kaya yanzun nan ki kawo min,marka tace toh ranki ya dade sannan ta fice..
Ammi ta zauna a gefen juwairiya tana hada mayuka masu shegen kamshi tace..
Ina so ki daina jin kunyata juwairiya,ni kakar kice babu wata kunya a tsakanin mu kinji?..
Juwairiya ta gyada kai tana murmushi..
Sallamar wasu yan mata guda biyu ne ya katse su..
Ammi na jin muryar su tace..
Ku shigo ciki yan matana har an taso daga makarantar ne?
Yan matan suka shigo ciki...Ammi kin san ko...
Mgnr ce ta tsaya musu a makoshi ganin juwairiya da sukayi akan gadon ammin su..
Kallon kallo suka shigayi wa juna..
A tare sukace..
Ammi a ina kika samo me kamar dake haka (her look alike)
Ammi tayi dariya, diyarku ce..
Cikin murna suka haye kan gadon suma suna saka juwairiya a tsakiyar su..
juwairiya dai da kallo kawai take bin su..
farare ne kamar ammi amma da ganin su zaka gane yan biyu ne da suna kama da juna..
Ammi na dariya tace..
Juwairiya wadan nan sune Autaye na,ga hassana ga kuma hussaina..
Juwairiya tabi su da kallo..
Hassana ta shafa fuskar juwairiya, diyar mu na kama da Ammi sosai..
Husssaina tace,sosai ma kuwa..
Ammi ta mike tana fadin,toh ku shirya min Jikata na bar muku wuka da nama a hannunku.
Murna sosai suka shiga yi ....
Ammi ta fice tana sanar musu marka zaka kawo kayan juwairiya..
"Sun gama shirya juwairiya cikin kaya na alfarma ba karamin kyau tayi ba,zan iya ce muku kamar an canzo mana juwairiya ne dan gaba daya (transforming)tayi..kamar ba juwairiya BAIWAR RUMFAR BAYI ba..
"Jama'ar gidan ne suka shiga shigowa ganin ta,ana ta taya ammi da murna..
Ammi kam baki bar kunne..
Hassana da hussaina kuwa suna makale da ita..
Khaleed ma sai da ya shigo,ya wara ido yana kallon juwairiya yace..
Ammi wacece wannan haka?
Ammi tayi dariya,diyarka ce mana..
Hassana tace,ya khaleed kaga yarda juwairiya ke kama da ammin mu ko?
Khaleed yayi dariya na gani sarkin surutu..
Juwairiya ta dago tana kallon khaleed, wai dama wannan mutumin kawun tane?
Khaleed ne ya kashe mata ido..
Yadai kina mamaki ko?
juwairiya tace ni gani nakeyi ma kamar mafarki nakeyi..
Ammi ta kamo hannunta tace..
ba mafarki kikeyi ba juwairiya duk abunda ke faruwa dake a yanzun GASKE NE.....
Juwairiya ta saki murmushi me cike da farin ciki...
Lallai dole ta gode wa Allah daya bayyanar mata da ASALINTA.....
Team RUMFAR BAYI
*RUMFAR BAYI*
(A historical fiction)
Na Afrah bhai
Page 33
Wattpad @afreey101
***************
"Washe gari...
"Mai martaba sarkin zazzau ya dawo daga tafiyar sada zumuncin daya tafi..
Labari ne mai dadi ris'ke sa na bayyanar diyar zarah'u...
Bai ma san wane irin farin ciki zayyi ba, bai bata wani lkc ba ya saka akayi masa Ammi..
Ammi da kanta ta saka su hassana su shirya juwairiya tsab sannan suka nufi bangaren na mai martaba..
Juwairiya har cikin zuciyarta take jin dadi sosai zata ga kakanta kuma mahaifin ummanta ta gaskiya..
"Sun tarar dashi a zaune saman kujerar sa ta karfe a cikin dakinsa..
Tsoho ne da zaikai shekaru kusan tamanin haka,amma ba zaka taba cewa mijin Ammi bane dan kuwa ta fishi jikin yarinta sosai..tunda dai ya girme mata nesa ba kusa ba..
"Tunda suka cikin shigo dakin sarki ya kurawa juwairiya ido yana kallonta cike da al'ajabi...
Tabbas wannan jinin diyar sa ce zarah'u ..
Da hannu yayi mata alama dataje garesa..
Ammi juwairiya ta kalla..
ta gyada mata kai tace kije juwairiya..
Ta taka har zuwa gabansa sannan ta duka kasa ta gaishe sa cike da girmamawa..
Hawaye ne suka cika masa ido..
Sai yanzu yake mugun dana sanin abunda ya aikawa diyar sa..
Ya shiga shafa kanta hannayensa na rawa haka ma lebensa...
Yace...
Asma'u (AMMI)
Ina godewa Allah daya bayyana mana jinin fatima muka ganta tun muna da sauran lumfashi a duniyar nan.
ina farin ciki sosai dana samu ganawa da ke...
ya fadi yana dago dakan juwairiya, hawaye itama takeyi sosai..
Ammi ta zauna tana fadin..
.. (note an sanarma sarki lbrn juwairiya duka)
Ba lkcn zubar da hawaye bane wannan,lkcn farin ciki ne da gode wa Allah...
Sannan kuma lkcne da zamu sanar ma juwairiya labarin mahaifiyar ta..
Mai martaba ya gyada kai,cike takaicin rashin zarah'u da sukayi yace,hakane dole ne mu sanar dake Wacece FATIMA wato ZARAH'U mahaifiyar ki....
*******************
*Masarautar zazzau A shekarun baya da suka gabata*..
"Zarah'u itace diya ta farko da Ammi ta fara haifa tun bayan auren su da mai martaba..
yarinya ce mai saukin kai da tausayin gaske gashi bata da wani hayaniya ko kadan,bazaka tabajin tayi fada ko gardama da wani ba..
Ta taso ne cikin so da kaunar mutanen dake cikin masarautar nan..
Dan Ko ina a cikin masarautar nan shiga takeyi tun tana yar karamar ta dan haka babu wanda bai santa ba..
"Zarah'u na da shekara sha bakwai mane ma aurenta sukayi mana caaaa..
Tunda ga yayan yan uwanmu zuwa masu kudin kasar mu..
"hakan kuwa ba karamin tashin hankali ya saka mu ba dan kuwa munyi wa zarah'u alkawarin zamu bata damar zabar mijin da zata aura..
Kuma a wannan lkcn ma a yarda na lura da ita ba auren bane a gabanta karatun da takeyi shi ta saka a gaba..
Ana cikin haka ne kuma sai muka riski ziyara daga sarkin kanon dabo a lkcn daurin auren garba..
Mai martaba ne yayi kiran dukka iyalensa dan gabatar dasu ga sarki ABU-TURAB...
Duk muka hallara a cikin babban falon mai martaba dan gaisawa da babban bakonsa..
Amma banda zabba'u wacce take can bangaren kakarta suna shan firarsu..
Marka ce na aika dan ta sanar da ita neman gaggawar da mahaifinsu keyi mata...
Zabba'u da gudunta ta shigo falon da sallama..
Kallone ya koma kanta..
A lkc guda kuma ta shiga zuciyar sarki ABU-TURAB farat daya....
Bayan mun gama gaisawa ne da sarki duk muka tashi muka fice dan basu waje..
Sarki ya kalli mai martaba yace..
Takawa Duk wadan nan yan matan yaranka ne?
Mai martaba ya gyada kai yace,duka yarana na ne ni na haife su..
amma zarah'u ce karama ce a cikinsu duk da tafi su jikin girma...
Sarki abu-turab ya jinjinar da kai kafin yayi sallama da mai martaba suka kama hanya..
Sati daya da zuwa ziyarar shi sai ga waziri da wambai sun sake sauka a kasar zazzau...
Munyi mutukar mamakin ganinsu dan basu aiko mana da wasikar zuwan nasu ba..
Mai martaba ya saka akayi musu tarba mai kyau suka ci suka sha kafin aka sake zama dan a gaisa..
Waziri bayyi kasa a gwiwa ba ya sanar da mai martaba sakon sarki abu-turah...
akan sunga IRI a cikin gidan sa kuma suna so..
Murna sosai mai martaba yayi dan kuwa yayi wa AMINA sha'awar abu-turab din..
Yayi murmushin su na manya yace..
Toh madallah ai babu wata matsala tunda akwai dangantaka mai karfi ta zumunci a tsakanin mu..
Waziri da wambai sukayi farin ciki sosai sannan cike da murna suka koma kasar kano...
Bayan sun sanarwa sarki abu-turab amincewar mai martaba ba karamin dadi yaji ba..
A take kuma yaje ya sanar ma mahaifiyar sa HAJJO..
Itama din taji dadi sosai dan kuwa tana mutukar son dan nata ya karo aure sbd irin rikicin da suke samu a wajen matar sa ta faro HINDU...
"Bayan wata daya ta shude sai ga sarki ABU-TURAB ya sake kawo mana wata ziyarar amma a wannan karon Zance ne ya kawo sa na Aure..
Mai martaba ya tare shi cikin murnar sa ya kuma saka YAYA BABBA (kishiyar ammi)ta shirya AMINA dan su dan gana da abu-turab din..
A can falon baki inda ya sauka aka shirya musu wajen da zasu kebe dan fahimtar junan su..
"Lkcn da amina ta shiga falon abu-turab ya kyalla ido ya ganta sai ya mike da sauri yana kiran waziri dake waje...
Ya nuna amina yace,ba wannan bace nake so..
Waziri mamaki ne ya kamasa..
cikin Fa'da suka koma a nan abu-turab yake sanarma mai martaba shi ba amina ce yake nufi ba wata ce daban..
Mai martaba yayi mamaki dan kuwa a lkcn yan matan gidan duka basu fi guda uku ba..
HAJIYA (kishiyar ammi ce itama )ya sake sanar ma wa akan a shirya BILKISU ta zo fada yana nemanta..
Bilkisu na zuwa abu-turab ya sake cewa ba ita bace..
Sai lokacin ne hankalin mai martaba ya tashi,dan kuwa yasan ba kowa bace abu-turab yake mgn face ZARAH'U ...
Jiki a sanyaye ya saka aka zo aka sanar min dana shirya zarah'u taje fada..
Nayi mutukar mamaki sosai sannan kuma hankalina ya tashi..
A haka na matsa mata ta shirya ta tafi..
Tana shiga Abu-turab yace ai itace yake mgn,shi itaa yake so a basa..
Mai martaba ya rasa yarda zayyi gashi kuma yayi musu alkawari tun da farko akan cewa ya basu..
damuwa sosai ne ya shiga dan ba'asan sarki da mgn biyu ba..
Bayan su abu-turab sun koma kasar su akan zasu dawo dan a saka ranar biki..
mai martaba ya same ni dan neman shawarata..