← Book details Rumfar Bayi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 52 OF 53

Sashe 52

Rumfar Bayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Juwairiya taja lumfashi tace hakan ma yayi..
Jalal ya rungume ta yana fadin..
Na kagara naga dan'mu/yarmu ni dake Giwata..
Yadan rike habar sa🤔Ko dawa zayyi kama a cikin mu?
juwairiya tayi dariya..
Da ni mana tunda a cikina yake..
Jalal ya dago fuskarta yace..
Ke yarinya SARAKI da babansa zayyi kamanni..
Juwairiya tace amma ai a cikin mamansa yake ko?😛

Jalal yadan turo baki...
Wato ma zolaya ta kike ko?
juwairiya ta make kafada ni na isa nayi wa baban SARAKI zolaya?
Jalal ya mike yana fadin..
Toh bari naje wajen khadija tunda ita har addu'a takeyi danta/yarta yayi kama da ni..

Juwairiya tayi saurin mikewa tana fadin..
Nima ai na yarda..
Jalal ya kwashe da dariya yana sake rungume ta ciki da tsantsar farin ciki da nishadi...

Team RUMFAR BAYI
             *RUMFAR BAYI*
          (A historical fiction)
Na Afrah bhai
Page 43

*KARSHE.........*

ONELOVE😘

********************

      "Washe gari...
Sai ga mai magani ta dira a cikin sashen sarki jalal..
Jalal ya saka jakadiya taje tayi masa kiran surayya da kuma juwairiya..

   Ai kuwa sai gasu sun shigo..
Surayya gaba daya jikinta babu wani karfi duk tayi laushi..
Jalal ya kalleta yace,surayya tunda kin ki sanar dani meke damunki yanzu dole ne ki tsaya me magani ta duba mana ke dan mu san halin da kike ciki..bakya ganin duk yarda kika koma ne?

Surayya ta shiga girgirza masa kai tana zubar da hawaye...tace
Sarkina nasha fada maka babu abunda ya ke damuna kada ka damu dani duk laifin da nayi muku....am...kuka yaci karfin ta..
Juwairiya ta dafa ta..a sanyaye tace..
Ah ah surayya ki bari kawai a duba ki dan hankalin mu bazai taba kwanciya ba idan har bamu san meke damun ki ba...

  Da kyal su juwairiya suka samu surayya ta yarda me magani ta duba ta..
   A firgice me magani ta kalli jalal tana fadin..
Mai martaba ai guba ce a jinin ta....

GU'BA!!!!!!
Jalal da juwairiya suka hada baki wajen fada cike da tsananin fargaba..
Ita kanta surayya sai da lumfashin ta ya dauke na wasu yan dakikai..

    Mai magani ta saka surayya ta kwanta flat a kasa,sannan ta saka wasu allulori ta tsaka su a saman ciki ta  sake fitowa dasu..
Sai ga wani bakin jini ya fito bakikkirin dashi..
Ta sake kallon jalal tace, Guba ce me tattare da bakin asiri,kuma tabbas da baku kawo ni nan yau din nan ba ina tabbatar muku da cewa a cikin watan nan zata iya rasa rayuwar dan bakin asirin dake jikinta ya gama gurbata jinin dake jikinta..

Jalal tashin hankali sosai ya shiga..
Juwairiya ma duk ta rude ta kama hannun surayya dake kuka sosai tace..
Dan Allah surayya ki sanar damu meya same ki?waye yake son kashe ki?
A ina kika ci wannan bakar Gubar?

Surayya duk a rikice take jin abunda me maganin nan ta fada..
Ta rirrike  juwairiya tana wani irin matsanan cin kuka...
Sannan ta sanar dasu duk abunda ya faru..
maganin neman haihuwa  ne da sukaje amsa a wajen wani malam can Sandamu,tunda tasha maganin ta rasa sukuni...

  Jalal  kam takaici duk ya ishe shi..
sbd neman haihuwa gashi nan  taje zata kashe kanta a banza..
Mai maganin tace..
Ni abunda ban gane ba a nan shine..
Shi me yasa malamin zai nemi ya kashe ki da bakar guda?
Bacin da kudin ki kika je wajen sa neman taimako..
Juwairiya tace nima shine na gani ai..
Ta kalli jalal tace..
Amale dan Allah ka saka aje a dauko mana wannan malamin ya fadi dalilinsa na son kashe surayya da bakar guba..
Jalal ya kalli jakadiya yace..
Kije ki sanar dasu shamaki aje can sandamun a dauko min wannan bokan malamin!!!..

"Malam sandamu a gaban sarki Jalal da sauran(royal family)...

Jalal ya kalli sarkin dorina dake tsaye yana ta bude hanci..
Yace..
idan har bai fada mana gsky ba akan dalilinsa na son kashe gimbiyar daura surayya.. toh na baka izinin lugwigwita shi a nan wajen..
   Malam na Sandamu ya hau wiki wiki da ido tsoro ya shige sa sosai..
Hamza yace..
Kayi mgn malam!!!!ko kaga tsararrakin ka a nan ne?

Malam ya zube kasa yana neman gafara yace..
Wlh tallahi babu ruwana a ciki..
Sarkin dorina ya kai masa duka mai shiga jiki..
Malam ya hau ihun azaba sannan yace..
Wallahi BAIWARTA ce,baiwarta ce wlh babu ruwana a ciki !!!!..

Jalal yace baiwarta ce?
Gaba daya wajen suka cika da al'ajabi da kuma tsananin mamaki!..

Surayya da kyal take iya bude ido ta kalleshi..
UMAYMA ta gama cutar  da ita..
har abada ba zata taba yafe mata ba..
Yanzu dama kashe ta dake da niyyar yi?
Lallai mutum abun yarda bane..

    Turaki yace,me baiwar tayi?
Malam yace,watarana ne tazo har wajena da makodan kudi sosai..
tace min..
zasu zo tare da uwar dakin ta akan tana neman haihuwa...
Shine ta biyani akan tana so na taimaka mata mu cuce ta mu bata wannan Gubar a matsayin maganin daukar cikin..
   Shine na ni kuma na hada ta da wanj bakin aljani shiyasa take ta fama da wannan ciwon ciki duk dare,aljanin ne yake zuwa yana lalata jinin ta da wannan gubar..

      Gaba daya wajen aka hau sallalami...
Nan suka tsare shi sai ya karya wannan asirin da yayi mata..
  Malam yasha bugu kamar ba gobe sannan ya karya asirin dake jikin surayya..duk ya gama tsorata..
  A Take surayya ta sume a wajen kilishi ta saka bayi suka dauke ta zuwa sashen ta..

""""""A cikin kankanin lkc labarin duk bazu a cikin masarautar...
juwairiya kam ta tausayawa surayya sosai...
Mutum ba abun yarda bane ashe dai cutar ta kawai umayma takeyi..
oh rayuwa kenan se ka rantse da Allah umayma tafi kowa san surayya...
ALLAH dai ya tsare gaba..
Amin

****************
""""A haka rayuwa taci gaba da tafiya a cikin masarautar ta daure...

Dan A yanzu kam surayya ta murmure sosai jikinta ya dawo..
dan kuwa tana samun kulawa sosai daga wajen yan gidan..
Duk da dai da farko sun ji haushin ta sosai na bin malamai da takeyi..
Sai kuma daga baya suka gane dai cewa abunda ta shuka ne ta garbe yanzu duniya tayi mata hankali..

"Wasa wasa cikin juwairiya ya fara girma gashi yanzu har yayi wata shidda...
Jalal kam na mugun son cikin nan dan kullum sai shiga sashen ta ya duba ta..
Duk kuma abunda da take so sai ya saka ayi mata shi..
khadija kam a watan nan ake saka ran haihuwar ta..

"Yau dai shirye shirye kawai akeyi a cikin masarautar dan yau ne daurin auren MAGAJI DA ZAINABA..

    Juwairiya ce uwar biki dan kuwa duk ita aka bar wa duk wani shirye shirye na bikin..
hakan kuwa ba karamin bata wa jalal rai yayi ba dan shi kam yafi so a bar masa giwar sa ta huta...

"An daura auren ne da karfe biyu na ranar asabar..

Dun'bim jama'ar kasar daura suka halarci daurin auren MAGAJI dan gidan WAZIRI da kuma gimbiya ZAINABA diyar mai martaba tsohon sarki Abdul-Jabbar..

"Amarya zainaba ba karamin  gyara tasha ba..
Dan tun sati daya kafin bikin me gyaran jiki tazo daga kasar borno ta shiga gyara ta a can sashen juwairiya.. dan nan ta dawo da zama ko su samira sai dai su leko su..

"Yau kuwa fulani ce ta aiko mata da kaya na alfarma data  saka ayi mata na musamman..
Gimbiya kilishi ma dai ba'a bar ta a baya ba dan kuwa sai data aikowa zainaba zinari me kyan gaske..

  Samira itama da tsohon cikin ta,nafisa kuwa cikin ta karamine shiyasa duk  tafi su karfi a wajen hidimar da akeyi da ita da surayya..

Dan itama Surayya dai har a wannan lkcn shiru bata samu cikin ba,sai dai a yanzu ta bar wa Allah komai ta rungumi kaddarar ta..

  Magaji ango ansha babbar riga sai washe baki akeyi...
jalal ne babban abokinsa kuma babban yayar amarya,hidima kam a ranar ba a magana..

"Karfe shidda na yamma aka fara shirin kai amarya..
Khadija dama ita tana can gidansu tunda sune dangin ango da katoton cikin ta haihuwa yau ko gobe..

An kai amarya dakin ta lafiya a can kusa da gidan Waziri magaji yayi ginin gidansa babban gaske..
taro ya watse lafiya aka bar amarya da halinta..

  Magaji kam yayi farin ciki sosai da kasancewa da zainabar sa dan kuwa a daren farkon su ba karamin faranta masa tayi ba..

Kwana biyu da auren su da zainaba..
Khadija ta sullubo yarta mai kama da ita sosai..
Jalal yayi murna sosai hakama sauran yan uwa..
Yarinya taci sunan kakar su jalal wato SHAFA'ATU

******************
Bayan wata uku..

"A yau juwairiya ta tashi da nakuda sosai..
Hansai da laure sukayi kiran jakadiya aka sanarwa sarki da kuma su gimbiya kilishi..

    Addu'a sosai aka shiga yi mata dan ta haihu lafiya dan ba karamar wahala take sha ba.

Surayya kam na gefen ta tana rike da hannunta tana tayi mata sannu..
Jalal kam ya kasa zaune ya kasa tsaye..
Turaki da hamza ne ke ta basa baki dan ya kwantar da hankalin sa..

Bayan wucewar awanni uku sai ga kukan jarirai ya cika sashen..
Nan aka hau murna bayi nata wakokinsu na nuna murna da farin ciki..
  Hansai ta kalli laure duk sunyi zufa tace..
Allahu akbar....
Yan biyu ne kuma duka maza.....!!!!!!!
Gu'da du'bu ta hau yi jakadiya kuwa tayi waje da gudun ta...

Sai sashen Sarki jalal..
Yana ganinta ya mike tsaye da saurinsa... ya taro ta hankalinsa a tashe..
Ta shiga rangwada guda tana rangwado wa jalal kirari cike da tsantsar farin cikin ta..
"Ga toya matsafa,babban Bajimi Babban Bako,Ga magajin Rumfa!
Ga........
Jalal yayi sauri tsayar da ita cike da kagara yaji da mai ta zo....dan kuwa hankalinsa ya kasa kwanciya ko kadan.....bai san halin da juwairiyar sa take ciki ba...
Jakadiya taja lumfashi kafin tace
Allah ya sauki GIWAR AMALE lafiya sumul..
ta haifa mana samari har biyu kyakkyawa kamar ka Sarkin mu..,Allah ya kawo mana TAGWAYEN SARAKAI..jinin JALALLUDEEN sarkin da ba kamar sa...!

Murna sosai Jalal yayi...
Ya rasa me zai ce sai godiya da yake ta zuba wa Allah...
turaki da hamza ne suka zo suka rungume sa suna taya sa murna sosai suma..
Chapter 52 · 0% Book details