Sashe 20
Rumfar Bayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
**********
"Sarki jalal ne ya fito daga fada tare da magaji da turaki a gefensa..
Kallon su yayi a gajiyensa yace,ku karasa da sauran cases din kaina ke ciwo zan dan shiga na huta..
Shamaki da sallama ne suka rufa masa baya suna masa kirari hade da gyara masa babbar rigar jikinsa..
"Rabi ba karamin nema tasha a dakin ba,a can karkashin gado ta hango layar da saurinta ta dauketa ta tura a cikin zani sannan ta fito..
Ganin babu juwairiya a falon sai tayi tunanin ko har ta tafi ne..
_"'Kuyi hakuri da wannan zuwa anjima inshaAllah_
_RUMFAR BAYI give away,thanks for all d readers that participate in my next post i will ANNOUNCE the 2 winners"_
TEAM RUMFAR BAYI
[9/18, 3:22 PM] Aysha Galadima: *RUMFAR BAYI*
(A historical fiction)
Na Afrah bhai
Page 21
Wattpad @afreey101
_juma'at mubarak all may Allah forgive us our sins amin_
****************
"Washe gari"
"Juwairiya na gani a zaune ta buga uban tagumi,yanzu menene mafita a gareta?
Ta shiga kallon yarda bayi ke ta wani rawar jiki suna gyara jikinsu dan kawai su samu yarima ya zabe su a cikin sababbin masu mishi hidima asashen sa..
Ita kuwa ya zatayi yanzu?tasan da cewa indai har tana ganin shi a kullum toh zuciyarta bazata taba samun sukuni ba,gashi kuma abun haushin ma yasan konewar fuskarta duk karya ce..
Laure ce ta dafa kafadarta,a sanyaye ta dago ta kalleta,laure tace taso muje,juwairiya ta mike suka shige cikin dakin jakadiya..
Hansai ta kalle ta tace, haba yar umma wannan hade rai har haka?
Juwairiya ta turo baki..
Jakadiya tace,ki kwantar da hankalinki juwairiya,na tabbata mai martaba bazai dauke ki ba ma,hansai tace,ni fa mamakin ma wadancan yaran nake da suke ta rawar jiki..
Laure tace ki kyele su duk so suke me martaba ya dauke su ko sunje su samu waje a can kinsan wasu da shegen kwadayin abun duniya suke...
Jakadiya ta girgiza kai,matsalar dai itace,duk lkcn da sarki ya ga wata baiwa daga cikin su kuma ya kyasa ta har ya kuma kwana da ita toh daga ranar zata zama SA'DAKARSA,wasu ma a haka suke karatar rayuwar su bai sake waiwayen su ba,masu rabon haihuwa kawai ne ba'a mantawa dasu a tarihi,toh wannan rayuwar har wani abun kwadayi ce?
Juwairiya dake sauraren jakadiya taji jikinta duk yayi sanyi ,wato dai ita baiwa ba zata taba samun damar zama mata kamar kowacce mace ba?sai dai amatsayin kwakwara?
Hayaniyar da sukaji ne daga waje yasa su duk mike duka,laure ta kalli juwairiya,
ki kwantar da hankalinki diyata,wannan tabon na fuskar ki kawai ya isa me martaba yaki zabar ki..
Juwairiya ta jinjina kai tana tausayin iyayen nata,
Wato su a nasu tunanin wannan tabon ne ze taimake ta?lallai da sun san da cewa jalal yasan komai da basu saka rai a kan shi ba..
"Suna fitowa suka tarar da bayi duk an ja layi,
kowaccen su na ta addu'ar samun nasara dan aiki a sashen sarki kamar wani garin girma ne suka samu..
Du'bu ce tazo taja hannun juwairiya ta kai ta cikin layin itama..
****************
"A waje kuwa...
Sarki jalal ne tare dasu shamaki dakuma wasu fadawan ana ta kwararo masa kirari..
"Zaune yake a wata kujerar alfarma ga kuma lema (umbrella) an rike masa yana shan iskan inuwa abunsa..
Fuskarshi a daure tamau sai shan kamshi yakeyi abu ga jinin sarakai...
A haka bayin suka ringa fitowa set by set.
duk wacce tayi masa kalar tsabta sai yayi wa shamaki kwatancen ta a kunne shi kuma shamakin yaje ya sanar wa uwar soro itake zuwa ta dauko su ta kai gefe...
Set dinsu juwairiya ne zasu fita yanzu,gabanta nata faduwa,zuciyarta ta kasu kashi biyu.
Kallo daya zakayi mata ka fahimci a tsorace take sosai ..
Fitowar ta yayi daidai da saukar da idanuwanta akan fuskar yarima..
Ji tayi duk karfin ta yana so ya kare..
Ta dauke kai da sauri taja kafarta taje ta tsaya akan layin.
Shamaki ne ya dan duka wajen kunnen yarima yace..
Allah ya kara maka yawan rai ga wasu nan sun sake fitowa suma..
Jalal kamar bayaso ya dago da kansa..
Caraf ya kyallo ta a cikin su..
Ya lumshe ido ya bude su ahankali,se yanzu ne yake jin dadin wannan selection din.
bai wani bata lkc ba ya sanar ma shamaki wacce yake so acikinsu..
Shamaki ba karamin mamaki yayi ba dan kuwa sai yarima ya dauki kusan minti sha biyar bai zaba ko daya ba, amma ji yanzu ko minti daya bai dauka ba ya zabo wancan..
Shamaki ya fadawa uwar soro..
Juwairiya kuwa kanta na kasa ta damke hannayenta..
Ji tayi kawai an dafa ta..
Ta dago a tsorace tana kallon uwar soro..
Uwar soron ta gyada mata kai,kware kuwa yarinya mai martaba ke ya zaba a duk cikin wannan layin!
Dum dum dum kake ji kirjin juwairiya nata bugawa..
Tadan kallo sa kasa'kasa...
taga yarda ya wani hade rai,tadan ja tsaki a cikin zuciyarta toh me yasa zai zabe ta?
ji yarda ya wani dauke fuskarsa...wata zuciyar kuma dadi takeji dan zata ringa samun ganin sa a kullum..
Cikin rumfar bayi ta koma,ta tarar da lbr har yaje kunnensu hansai,rungume ta kawai sukayi suka fada cikin daki..
****************
"Umayma ce na gani a zaune tana lillasafo wa surayya bayin da yarima duk ya zaba jiyan..
Tana kaiwa kan juwairiya surayya tayi saurin mikewa daga kwancen da take..
"Kina nufin harda wannan yarinyar me konannar fuskar?
Umayma tace kin san tane ranki ya dade?
Surayya taja tsaki,dole ne kuwa mu saka ido a cikin sashen sarki..
umayma kin gane,inaso ki samo min baiwa da zamu aminta da ita kina jina?
Umayma tace an gama ranki shi dade..
******************
"Da safe jakadiya da kanta ta kawo wa juwairiya kayan da ringa kasawa (kamar matsayin uniform kenan)
Sai da ta gama shiryawa sannan suka fito dan tafiya..
Juwairiya ta kalli jakadiya,kiyi gaba inna bari na dan shiga wajen zainaba ,jakadiya tace,toh amma kiyi sauri dai,juwairiya tayi murmushi sannan da gudu tayi gaba..
"Tun kafin ta idasa shiga sashen take jin ihun zainaba, hankalinta a tashe ta shige da saurinta...
"Laure ta iske a tsaye tare da zabba'u a gefenta ,zainaba sai zazzaga masifa takeyi..
Ni wlh babu wata baiwa da za'a canza min,ni juwairiya nake so!
Laure kamar ta fashe da kuka tace,Allah ya huci zuciyar ki,jiya fa mai martaba da kansa ya zabe ta a matsayin sabowar baiwarsa,dole ne kiyi hakuri a canza miki da wata..
Zainaba zatayi mgn juwairiya tayi saurin karasa wajenta..
Dan Allah ranki shi dade kiyi hakuri..
Zainaba ta damko hannunta muje wajen fulani dolene ya jalal ya barmin ke...
"Haka zainaba tayi ta jan juwairiya har sashen fulani diyya..
Turaki da fulani na zaune suna gaisawa sai ganin su kawai sukeyi kamar daga sama.
Zainaba ta fashe da kuka tana fadin..
Ni dai wlh fulani kije ki fadawa abba ya jalal ya barmin baiwa ta bazan bawa kowa ita ba!
Fulani ta mike tana fadin,haba zainaba kinsan fa a yanzu jalal shine mai wuka da nama acikin masarautar nan..
Zainaba ta kalli turaki dake ta kallonsu yana jin abun wani banbara kwai,me yasa ya jalal zai dauke juwairiya? Haka nan yaji wani irin abu a cikin zuciyarsa...
Ya turaki dan Allah muje ka tayani rokonsa?
Turaki ya mike a sanyaye,ki yi hakuri zainaba kinji?
Zainaba ta kalli juwairiya dake gefenta tana yan hawayen rabuwa da uwar dakin tata.
Allah ya gani ba karamin shakuwa tayi da ita ba..
Naji zan bar masa ita...amma da sharadi idan har ita ce ta amince zata zauna acan din..
Juwairiya taji gabanta ya fadi..
Fulani tace wane irin sakarci ne haka?
Zainaba bata tanka ta ba ta sake jan juwairiya suka fice turaki na bayansu yana faman kwalawa zainaba kira..
"A sashen sarki jalal taja burki,jakadiya ta fito da sauri ta tare su,zainaba tace,jakadiya ina ya jalal?inason ganinsa dan Allah..
Jakadiya zatayi mgn sai ga yarima ya fito cikin shigar alfarma se baza kamshi yakeyi..khadija ce a gefensa tana wani yanga sai faman gyara masa alkyabbar jikinsa takeyi..
Zainaba ce ta karasa gabansa tana kuka..
Jalal ya tsaya yana kallonta da mamaki..
Cikin muryar tausayi tace,dan Allah ya jalal kabar min baiwata ta nuna gefen da juwairiya take..
Sai a lkcn ya lura da juwairiya dake gefen zainaba tana goge hawayen ta..
Ji yayi zuciyarsa ta buga,ya sake kallon zainaba yace cike da kasaita,sarki baya mgn biyu kanwata..
Zainaba tace,nidai yaya bazan iya bar maka ita ba sai dai idan itace tace min zata iya zama a nan din..
Khadija dake faman hararar juwairiya tace,ya jalal kawai ka bar mata ita mana me zakayi da wannan me konannar fuskar..
Har cikin ransa yaji kalamanta..
Zainaba ta kalli juwairiya, ki fada min gsky na barki a nan kinaso?zaki iya rayuwa a inda ake kyamatarki?
Juwairiya gabanta ya hau faduwa zuciyarta ta kasu kashi biyu...
ga Idanu duk a kanta...
bakinta ne ya soma rawa tana shirin mgn ne.. sai ganin turaki sukayi ya karaso wajen..
Bai tsaya wata'wata ba ya fisgo hannun zainaba sannan ya kalli jalal yace..kayi hakuri yaya......ya shiga jan zainaba sukayi waje...
Khadija taja dogon tsaki itama kafin tabi bayansa tana wurgawa juwairiya harara...
Yarima dake tsaye ya maida kallonsa kan juwairiya dake ta sharar kwalla..
Karasawa yayi gabanta yana rungume hannayensa a kirjinsa kafin nan taji yace a takaice..
"Ki saka a zuciyarki bazan taba bari ki subuce min ba......"
Yana gama fadar haka yayi tafiyarsa...
"Juwairiya tabi bayansa da kallon mamaki..
Bazai bari ta subuce masa ba?
Me hakan yake nufi?
Ta dafe kanta, lallai idan batayi a hankali ba yarima yana gab da rikita mata lissafinta...
*************
"Jakadiya ce da kanta ta shiga da juwairiya wajen shakatawar yarima,tace nan ne wajen aikin ki juwairiya,nan ne kawai nake ganin zai nisantaki daga duk wani rikicin gidan sarauta..
Juwairiya ta murmusa tace,nagode da kulawarki inna jakadiya..
"Da daddare duk sun gama aikinsu suna tsaye suna jiran jakadiya ta fito ta sallame su,sai ga surayya ta shigo tare da umayma a bayanta..
Taci gayu kamar zata kasar sarauniyar kyau (yau ne kwananta)
Ko kallon inda su juwairiya suke batayi ba..
Umayma kam harda zuwa ta gaisa dasu tana karewa juwairiya kallo..
************
"A daki surayya ta iske shi ya kwanta ya lumshe idanuwansa..
"Sarki jalal ne ya fito daga fada tare da magaji da turaki a gefensa..
Kallon su yayi a gajiyensa yace,ku karasa da sauran cases din kaina ke ciwo zan dan shiga na huta..
Shamaki da sallama ne suka rufa masa baya suna masa kirari hade da gyara masa babbar rigar jikinsa..
"Rabi ba karamin nema tasha a dakin ba,a can karkashin gado ta hango layar da saurinta ta dauketa ta tura a cikin zani sannan ta fito..
Ganin babu juwairiya a falon sai tayi tunanin ko har ta tafi ne..
_"'Kuyi hakuri da wannan zuwa anjima inshaAllah_
_RUMFAR BAYI give away,thanks for all d readers that participate in my next post i will ANNOUNCE the 2 winners"_
TEAM RUMFAR BAYI
[9/18, 3:22 PM] Aysha Galadima: *RUMFAR BAYI*
(A historical fiction)
Na Afrah bhai
Page 21
Wattpad @afreey101
_juma'at mubarak all may Allah forgive us our sins amin_
****************
"Washe gari"
"Juwairiya na gani a zaune ta buga uban tagumi,yanzu menene mafita a gareta?
Ta shiga kallon yarda bayi ke ta wani rawar jiki suna gyara jikinsu dan kawai su samu yarima ya zabe su a cikin sababbin masu mishi hidima asashen sa..
Ita kuwa ya zatayi yanzu?tasan da cewa indai har tana ganin shi a kullum toh zuciyarta bazata taba samun sukuni ba,gashi kuma abun haushin ma yasan konewar fuskarta duk karya ce..
Laure ce ta dafa kafadarta,a sanyaye ta dago ta kalleta,laure tace taso muje,juwairiya ta mike suka shige cikin dakin jakadiya..
Hansai ta kalle ta tace, haba yar umma wannan hade rai har haka?
Juwairiya ta turo baki..
Jakadiya tace,ki kwantar da hankalinki juwairiya,na tabbata mai martaba bazai dauke ki ba ma,hansai tace,ni fa mamakin ma wadancan yaran nake da suke ta rawar jiki..
Laure tace ki kyele su duk so suke me martaba ya dauke su ko sunje su samu waje a can kinsan wasu da shegen kwadayin abun duniya suke...
Jakadiya ta girgiza kai,matsalar dai itace,duk lkcn da sarki ya ga wata baiwa daga cikin su kuma ya kyasa ta har ya kuma kwana da ita toh daga ranar zata zama SA'DAKARSA,wasu ma a haka suke karatar rayuwar su bai sake waiwayen su ba,masu rabon haihuwa kawai ne ba'a mantawa dasu a tarihi,toh wannan rayuwar har wani abun kwadayi ce?
Juwairiya dake sauraren jakadiya taji jikinta duk yayi sanyi ,wato dai ita baiwa ba zata taba samun damar zama mata kamar kowacce mace ba?sai dai amatsayin kwakwara?
Hayaniyar da sukaji ne daga waje yasa su duk mike duka,laure ta kalli juwairiya,
ki kwantar da hankalinki diyata,wannan tabon na fuskar ki kawai ya isa me martaba yaki zabar ki..
Juwairiya ta jinjina kai tana tausayin iyayen nata,
Wato su a nasu tunanin wannan tabon ne ze taimake ta?lallai da sun san da cewa jalal yasan komai da basu saka rai a kan shi ba..
"Suna fitowa suka tarar da bayi duk an ja layi,
kowaccen su na ta addu'ar samun nasara dan aiki a sashen sarki kamar wani garin girma ne suka samu..
Du'bu ce tazo taja hannun juwairiya ta kai ta cikin layin itama..
****************
"A waje kuwa...
Sarki jalal ne tare dasu shamaki dakuma wasu fadawan ana ta kwararo masa kirari..
"Zaune yake a wata kujerar alfarma ga kuma lema (umbrella) an rike masa yana shan iskan inuwa abunsa..
Fuskarshi a daure tamau sai shan kamshi yakeyi abu ga jinin sarakai...
A haka bayin suka ringa fitowa set by set.
duk wacce tayi masa kalar tsabta sai yayi wa shamaki kwatancen ta a kunne shi kuma shamakin yaje ya sanar wa uwar soro itake zuwa ta dauko su ta kai gefe...
Set dinsu juwairiya ne zasu fita yanzu,gabanta nata faduwa,zuciyarta ta kasu kashi biyu.
Kallo daya zakayi mata ka fahimci a tsorace take sosai ..
Fitowar ta yayi daidai da saukar da idanuwanta akan fuskar yarima..
Ji tayi duk karfin ta yana so ya kare..
Ta dauke kai da sauri taja kafarta taje ta tsaya akan layin.
Shamaki ne ya dan duka wajen kunnen yarima yace..
Allah ya kara maka yawan rai ga wasu nan sun sake fitowa suma..
Jalal kamar bayaso ya dago da kansa..
Caraf ya kyallo ta a cikin su..
Ya lumshe ido ya bude su ahankali,se yanzu ne yake jin dadin wannan selection din.
bai wani bata lkc ba ya sanar ma shamaki wacce yake so acikinsu..
Shamaki ba karamin mamaki yayi ba dan kuwa sai yarima ya dauki kusan minti sha biyar bai zaba ko daya ba, amma ji yanzu ko minti daya bai dauka ba ya zabo wancan..
Shamaki ya fadawa uwar soro..
Juwairiya kuwa kanta na kasa ta damke hannayenta..
Ji tayi kawai an dafa ta..
Ta dago a tsorace tana kallon uwar soro..
Uwar soron ta gyada mata kai,kware kuwa yarinya mai martaba ke ya zaba a duk cikin wannan layin!
Dum dum dum kake ji kirjin juwairiya nata bugawa..
Tadan kallo sa kasa'kasa...
taga yarda ya wani hade rai,tadan ja tsaki a cikin zuciyarta toh me yasa zai zabe ta?
ji yarda ya wani dauke fuskarsa...wata zuciyar kuma dadi takeji dan zata ringa samun ganin sa a kullum..
Cikin rumfar bayi ta koma,ta tarar da lbr har yaje kunnensu hansai,rungume ta kawai sukayi suka fada cikin daki..
****************
"Umayma ce na gani a zaune tana lillasafo wa surayya bayin da yarima duk ya zaba jiyan..
Tana kaiwa kan juwairiya surayya tayi saurin mikewa daga kwancen da take..
"Kina nufin harda wannan yarinyar me konannar fuskar?
Umayma tace kin san tane ranki ya dade?
Surayya taja tsaki,dole ne kuwa mu saka ido a cikin sashen sarki..
umayma kin gane,inaso ki samo min baiwa da zamu aminta da ita kina jina?
Umayma tace an gama ranki shi dade..
******************
"Da safe jakadiya da kanta ta kawo wa juwairiya kayan da ringa kasawa (kamar matsayin uniform kenan)
Sai da ta gama shiryawa sannan suka fito dan tafiya..
Juwairiya ta kalli jakadiya,kiyi gaba inna bari na dan shiga wajen zainaba ,jakadiya tace,toh amma kiyi sauri dai,juwairiya tayi murmushi sannan da gudu tayi gaba..
"Tun kafin ta idasa shiga sashen take jin ihun zainaba, hankalinta a tashe ta shige da saurinta...
"Laure ta iske a tsaye tare da zabba'u a gefenta ,zainaba sai zazzaga masifa takeyi..
Ni wlh babu wata baiwa da za'a canza min,ni juwairiya nake so!
Laure kamar ta fashe da kuka tace,Allah ya huci zuciyar ki,jiya fa mai martaba da kansa ya zabe ta a matsayin sabowar baiwarsa,dole ne kiyi hakuri a canza miki da wata..
Zainaba zatayi mgn juwairiya tayi saurin karasa wajenta..
Dan Allah ranki shi dade kiyi hakuri..
Zainaba ta damko hannunta muje wajen fulani dolene ya jalal ya barmin ke...
"Haka zainaba tayi ta jan juwairiya har sashen fulani diyya..
Turaki da fulani na zaune suna gaisawa sai ganin su kawai sukeyi kamar daga sama.
Zainaba ta fashe da kuka tana fadin..
Ni dai wlh fulani kije ki fadawa abba ya jalal ya barmin baiwa ta bazan bawa kowa ita ba!
Fulani ta mike tana fadin,haba zainaba kinsan fa a yanzu jalal shine mai wuka da nama acikin masarautar nan..
Zainaba ta kalli turaki dake ta kallonsu yana jin abun wani banbara kwai,me yasa ya jalal zai dauke juwairiya? Haka nan yaji wani irin abu a cikin zuciyarsa...
Ya turaki dan Allah muje ka tayani rokonsa?
Turaki ya mike a sanyaye,ki yi hakuri zainaba kinji?
Zainaba ta kalli juwairiya dake gefenta tana yan hawayen rabuwa da uwar dakin tata.
Allah ya gani ba karamin shakuwa tayi da ita ba..
Naji zan bar masa ita...amma da sharadi idan har ita ce ta amince zata zauna acan din..
Juwairiya taji gabanta ya fadi..
Fulani tace wane irin sakarci ne haka?
Zainaba bata tanka ta ba ta sake jan juwairiya suka fice turaki na bayansu yana faman kwalawa zainaba kira..
"A sashen sarki jalal taja burki,jakadiya ta fito da sauri ta tare su,zainaba tace,jakadiya ina ya jalal?inason ganinsa dan Allah..
Jakadiya zatayi mgn sai ga yarima ya fito cikin shigar alfarma se baza kamshi yakeyi..khadija ce a gefensa tana wani yanga sai faman gyara masa alkyabbar jikinsa takeyi..
Zainaba ce ta karasa gabansa tana kuka..
Jalal ya tsaya yana kallonta da mamaki..
Cikin muryar tausayi tace,dan Allah ya jalal kabar min baiwata ta nuna gefen da juwairiya take..
Sai a lkcn ya lura da juwairiya dake gefen zainaba tana goge hawayen ta..
Ji yayi zuciyarsa ta buga,ya sake kallon zainaba yace cike da kasaita,sarki baya mgn biyu kanwata..
Zainaba tace,nidai yaya bazan iya bar maka ita ba sai dai idan itace tace min zata iya zama a nan din..
Khadija dake faman hararar juwairiya tace,ya jalal kawai ka bar mata ita mana me zakayi da wannan me konannar fuskar..
Har cikin ransa yaji kalamanta..
Zainaba ta kalli juwairiya, ki fada min gsky na barki a nan kinaso?zaki iya rayuwa a inda ake kyamatarki?
Juwairiya gabanta ya hau faduwa zuciyarta ta kasu kashi biyu...
ga Idanu duk a kanta...
bakinta ne ya soma rawa tana shirin mgn ne.. sai ganin turaki sukayi ya karaso wajen..
Bai tsaya wata'wata ba ya fisgo hannun zainaba sannan ya kalli jalal yace..kayi hakuri yaya......ya shiga jan zainaba sukayi waje...
Khadija taja dogon tsaki itama kafin tabi bayansa tana wurgawa juwairiya harara...
Yarima dake tsaye ya maida kallonsa kan juwairiya dake ta sharar kwalla..
Karasawa yayi gabanta yana rungume hannayensa a kirjinsa kafin nan taji yace a takaice..
"Ki saka a zuciyarki bazan taba bari ki subuce min ba......"
Yana gama fadar haka yayi tafiyarsa...
"Juwairiya tabi bayansa da kallon mamaki..
Bazai bari ta subuce masa ba?
Me hakan yake nufi?
Ta dafe kanta, lallai idan batayi a hankali ba yarima yana gab da rikita mata lissafinta...
*************
"Jakadiya ce da kanta ta shiga da juwairiya wajen shakatawar yarima,tace nan ne wajen aikin ki juwairiya,nan ne kawai nake ganin zai nisantaki daga duk wani rikicin gidan sarauta..
Juwairiya ta murmusa tace,nagode da kulawarki inna jakadiya..
"Da daddare duk sun gama aikinsu suna tsaye suna jiran jakadiya ta fito ta sallame su,sai ga surayya ta shigo tare da umayma a bayanta..
Taci gayu kamar zata kasar sarauniyar kyau (yau ne kwananta)
Ko kallon inda su juwairiya suke batayi ba..
Umayma kam harda zuwa ta gaisa dasu tana karewa juwairiya kallo..
************
"A daki surayya ta iske shi ya kwanta ya lumshe idanuwansa..