← Book details Rumfar Bayi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 53

Sashe 3

Rumfar Bayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Laure ta mike da sauri tace toh ranki ya dade..
  Laure na fita ta shiga buga sauri bata zarce ko ina ba se sashen gimbiya kilishi tayi tsaye tana tunanin yarda zata samu mgn da hansai...

  Can ta hango wata baiwa ta fito da tire a hannunta,laure ta tare ta da sauri..
  ke Yimin mgn da hansai kice mata ina mata neman gaggawa..

   Laure na nan jingine da kango sai ga hansai kamar an jeho ta, ta kalli laure ya akayine laure?

   Laure tace ina jakadiya?
Hansai tace tana can fadar mai martaba ,laure taja lumfashi sannan ta sanar ma hansai yarda ake ciki,hansai ta dafe kirji yau mun shiga uku yaushe juwairiya ta fito daga rumfar bayi?

Laure tace ba wannan ba yanzu ya zamuyi?dan fulani ta nemi dana kawo ta..
  Hansai tace a gaskiya bana son juwairiya ko kadan tayi irin rayuwar da muke ciki,bamu san asalinta ba bamu san daga wace duniyar ta fito ba amma laure wlh bana son ganin juwairiya cikin damuwa ko kadan,kuma kinsan halinta kwarai bata ji  kada taje tayi wani laifin...... kuka ne yaci karfin ta..

  Laure ta dafa ta bari na saka wani bafaden yayi mana kiran jakadiya se mu san nayi.

Cikin tashin hankali jakadiya ta karaso wajen su,lafiya naji kira haka,shamaki yake ce sanar min ana nema na bayan kunsan yau ina fa'da ne da kyal na samu waziri yamin alfarmar tahowa..

   Hansai na hawaye ta sanar mata da komai,jakadiya taja lumfashi toh miye a ciki?dole ne kun san watarana hakan zata faru,laure tace bari dai na je na kai ta wajen fulani nasan dole ne a gobe zata fara aikinta na BAUTA...

Laure ce ta shigo rumfar bayi can ta hango juwairiya tana ta tsalle tsalle tana zolayar du'bu dake zaune tana linkin kaya..
   Laure ce ta karasa ta zauna kusa da du'bu tana sanar mata umurnin fulani na son ganin juwairiya..

Du'bu ta gyara zamanta tana murmushin murna dan ita kam ta hannun damar fulani ce sosai sam bata son komai daya danganci gimbiya kilishi..

Tace Allahu akbar ai zainaba ba kadan ta biyo mahaifiyar ta fulani ba,na tabbata juwairiya zataji dadin zama da ita.

  Laure tace uhm,sannan taje ta kamo hannun juwairiya, juwairiya tace,goggo laure ina zamuje?laure tace badai ke yawo ba ai gashi nan jin jawo wa kanki aikin BAUTA..

"A kofar sashen fulani akayi musu iso..
Laure taja hannun juwairiya dake ta kalle kalle suka shiga ciki..

   Baki sosai juwairiya ta bude ganin kyau da tsarin falon ,can ta hango fulani hakimce akan kilisar ta..
  Tayi kasa da kanta,zainaba ce ta mike tana fadin,itace wannan umma kin ga ta nan..

Fulani tayi murmushi tana kallon juwairiya a ranta tace,yarinyar kyakkyawa, ta kalli laure toh kinji laure ita zainaba take so a matsayin kuyangar ta dan haka daga gobe zata fara yiwa zainaba hidima...

    Juwairiya tayi saurin kallo zainaba dake kallonta dauke da murmushi, sannan ta kalli turaki dake zaune shiru yana saurarensu..

Laure tace an gama ran fulani ya dade,zainaba ta kalli juwairiya sai mun hadu gobe ko?juwairiya ta gyada kai sannan suka juya suka fice..

"A daren ranar raba dare su jakadiya,laure da hansai sukayi suna fahimtar da juwairiya yanayin rayuwar da zata shiga..

Suka fara da gaya mata matsayin ta,ke ba kowa bace fa'ce BAIWA,
yanzu gimbiya zainaba itace uwar dakinki wacce zakiyi wa hidima..
komai takeso shi zakiyi mata babu gardama,
ko me tace dole ki amince dashi,
duk abunda take so shi zaki so,
duk abunda bataso kada kiyi,
ki guji bata mata rai,
kome zakiyi se kin nemi  izinin ta,
ki bauta mata dan a halin yanzu rayuwarki kamar tana hannunta ne..

   Juwairiya taji abun banbara kwai,tace amma umma jakadiya rayuwa  tana ga Allah ne ai ko?laure tace hakane amma rayuwarki da zakiyi a wannan masarautar tana hannun gimbiya zainaba ne,dan a kowane lkcn zata iya ba'tar dake...

  Juwairiya ta tsorata sosai,jakadiya ta shiga nuna mata yarda duk zata kula da gimbiya zaOneloveuk wata hidima da akeyiwa ya'yan sarauta an koyar da ita,sai cikin dare sosai suka samu rintsawa sbd tambayoyi da juwairiya ta rufe  su dashi....

" Wannan kenan "

Share pls n pls vote on wattpad @afreey101
#Onelove

[9/18, 3:10 PM] Aysha Galadima: 🏕 *RUMFAR BAYI* 🏕
(A historical fiction)

Na Afrah bhai
Page 4
Wattpad @afreey101

************************

       "Washe gari da sassafe,hansai ce ta shirya juwairiya cikin irin shigar tasu ta bayi, kayane irin na Sa'ki' dinnan riga da zani(blue color kayan fulani dinnan ),laure ta shigo taja hannunta suka fice..

   "Tafiya sukeyi juwairiya na ta kalle kalle tana tsallenta cike da nishadi..
' can ta hango wani yaro dauke da kwando a kansa aciki kuwa su mangoro ne da gwaba gashi tana mugun son mangoro sosai,nan ta kura mai ido tana tafiya tana waiwayen sa,yana dago da kai ya hango ta,ganin yarda take bin kwandon dake kansa da kallone sai ta bashi dariya har sai daya murmusa..

    Laure ce ta hadu da wata baiwa suka tsaya gaisawa,juwairiya ta tsaya tana tunanin irin girman masarautar dan sun sha tafiya sosai ga gine gine masu yawa ga shukoki masu kayatarwa..

  " Amsa.."
Taji ance daga bayanta,tayi saurin juyowa..
Sukayi ido hudu da wannan yaron..yana mika mata mangoro biyu fuskarsa dauke da murmushi..

Ta kalleshi ta saki wani irin murmushin murna,ji tayi laure tace,muje muje juwairiya....

  Da sauri ta amshe mangoron ta furta ngd da sauri tayi gaba...

Suna isa sashen zainaba ayi musu iso ciki..
Zainaba na hakimce a zaune ana ta mata fifita...
Juwairiya ta saki baki ganin kyawun dakin ya burge ta sosai..
Zainaba ta saki fuska sannan tace,wai ya sunan ki ne ma?
Sauke kanta tayi kasa tuna mgnr su  yaha ta jiya da sukace banda  hada ido da uwar daki,a sanyaye tace sunana JUWAIRIYA..

Zainaba tace toh muje makewayi (toilet ) dan ina son nayi wankana yanzu..
Juwairiya tayi saurin kallon laure,laure ta gyada kai sannan taje kusa da ita tace,kada ki manta da maganar mu ta jiya,tana gama fadin haka tayi gaba..

     Juwairiya kanta a kasa tace ina ne ban dakin ranki shi dade?
Zainaba ta dan murmusa sannan ta kalli baiwar dake kusa da ita tana mata fifita tace,kai ta ban dakina sannan ki nuna mata yarda nake son ruwan wanka na..

"toh ranki shi dade ta mike hade da kiran juwairiya suka shiga wata kofa data sada su da wani makeken toilet sai kamshin sabulai yakeyi ga wani bahon wanka na silver a ciki, baiwar ta kalli juwairiya tace,kingani ruwan zafin kadan zaki saka dan zainaba bata son ruwan wankanta yafiya zafi da yayi dumi ya isa'

,ta dauko wasu ganyayya'ki masu fitar da wani sanyin kamshi,tasa hannu ta damka kadan tace kinga haka?juwairiya ta gyada kai,toh haka zaki ringa sakawa duk lkcn da zaki hada mata ruwankan ta,juwairiya duk ta fahimta dan kuwa akwai ta da kaifin basira.

'Se data taimakawa zainaba ta cire kayanta sannan suka shiga ban dakin.

'zainaba ta shige cikin bahon wanka da dan shimin dake jikinta,ta kalli juwairiya,tace..

"cu'da min bayana"
juwairiya ta dauko soso mai taushi tazo ta fara cu'ta mata bayan a hankali sbd dai an sanar mata yarda akeyi.

   Sai da zainaba ta wanko sosai sannan suka dawo daki,ta kalli juwairiya dauko min wancan akushin,ta dauko tazo gabanta ta ajiye,zainaba ta bude kayan kwalliyarta ne a ciki.

  Ta kalli juwairiya......
miko mi'ni jan bakin can,juwairiya tayi sakatoto tana kallonta dan bata ma san minene shi jan bakin ba,zainaba taji shiru tace lah baki san shi ba ne?

"Ta gyada kai tana fadin,Allah ya huci zuciyar  ranki ya dade bani da masaniyar me kike bukata idan har ranki ya dade baza ta damu ba ina so ta ganar dani minene shi,zainaba tayi dariya sannan ta dauko jan bakin da kwalli da hoda duk ta nuna mata su'sannan ta tsara yar kwalliyarta da kanta,juwairiya cike da mamaki take kallonta ta saki baki ganin yarda zainaba tayi kyau abunta.

sai da ta taimaka mata ta saka kaya sannan suka dawo cikin falo...
cikinta ne ya hau rurin yunwa ganin irin delicious din dake jere a gaban zainaba tana ci tana wani yatsina.

Tunawa tayi da mangoron ta na dazu data ajiye akan ta'ga (window)lkcn shigowar su.
Tadan sadda kai kasa,ranki shi dade zan iya fita yanzu yanzun nan na dawo?
Zainaba ta kalleta da mamaki ina zakije?
Juwairiya ta dan dafe cikinta sannan tace wata ajiya nayi  a waje zan dauko.
Zainaba ta gyada kai zaki iya tafiya..
Da gudu ta fito neman mangoron ta,sai ko ta gansu a inda ta ajiye su din.
cikin murna ta dauka ta shiga shansa kamar an aikota duk tayi kaca kaca da bakinta..

    "Ashe ke kazama ce?

Taji an fada daga gefen ta,da sauri ta kallo wajen,turaki ne ta gani da bawan sa a bayansa..
Ta dan sude hannunta sannan tayi kasa da kai,barka da zuwa ranka ya dade..

Cike da mamaki yake binta da kallo wato yanzu ta fara sanin dokokin gidan kenan?
Yauwa kawai ya fada sannan ya shige wajen kanwar sa..

   'Yana shiga zainaba ta mike cike da murna,yaya ashe zaka zo?
Ya dan daure fuska miye na kirana da sassafen nan haka?
Zainaba ta shagwabe fuska,dama fa zan tuna maka ne yau nakeso muje na hau do'ki nima..

  Turaki ya lumfasa wato bazaki bar wannan zancen ba ko?
Daure fuska tayi,amma ai har fulani na fadawa kuma ta amince naje na da'na dokin nima..

  'Turaki ya girgiza kai sanin halin kafiya irin ta zainaba,juwairiya ce ta shigo kamar munafuka se goge bakinta takeyi..
    Zainaba ta kalleta ki shirya zamuje hawan doki,juwairiya tace toh ranki ya dade.

Tsaye suke a cikin wajen ajiyar dawakan sarki.
Zainaba se zumudi takeyi,ta kalli bawan dake tsaye wajen tace,wancan dokin nakeso na hau,ta nuna wani farin doki dayaji kayan ado sosai..

Zubewa kasa bawan yayi yace,kiyi min rai ranki shi dade wannan dokin musamman YARIMA yasa aka shirya masa shi yau din nan..
   Zainaba a take ta daure fuska ta kalli turaki dake gefenta,yaya kaji wai na ya jalal ne ta karashe mgnr kamar zatayi kuka..
Turaki yace,kiyi hkr ki zabi wani mana?

Zainaba ta zunburo baki,zatayi mgn suka hango yarima yana tahowa cikin kasaitar sa bayi na biye dashi a baya.
   Yana karasowa wajen duk suka tsaya kallonsa bayin dake wajen kuwa suka zube suna kwasar gaisuwa..
Chapter 3 · 0% Book details