Sashe 4
Rumfar Bayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bai ko kallon inda su turaki ke tsaye bayyi ba..
idanunsa ne suka sauka akan juwairiya dake tsaye a bayan zainaba bata da ko niyyar dukawa ta gaishe shi..
Ke!
Ya fada yana yastine fuska..
Juwairiya ta dago suka hada ido,dauke kansa yayi..
"Na lura har yanzu baki san matsayin ki ba ko?
Sake dukar da kanta tayi tace'barka da fitowa ranka shi dade..
Yarima ya tabe baki sannan ya maida kallonsa kansu turaki..
Zainaba ta daure fuska Allah ya gani bata son girman kai da isa da ikon da ya jalal yake ji dashi..
Lafiya?...yarima ya fada yana musu kallon me kuke a nan?..
Turaki ya murmusa babu komai dama wucewa muka zo yi..
Yarima ya tabe baki ya karasa wajen do'kin sa wani bawa ya taimaka masa ya haye sama abunsa....
Zainaba kuwa ta banka wa turaki harara sannan ta juya a fusace tayi gaba,juwairiya tayi saurin bin bayanta ..
"Fulani ce a zaune saman kilisar ta laure na mata tausar kafa suka shigo bayan anyi musu iso..
Zainaba ta fada jikin fulani tana kukan shagwaba,fulani wai me yasa a gidan nan ne akafi girmama su UMMA babba (gimbiya kilishi kenan) da su yaya YARIMA?akan mu?
Naga ai mu ma baban mu daya dasu ko?tunda duk mai martaba ne ya haife mu..
Fulani ta sa hannu ta dago fuskarta'da ta fara ji'kewa da ruwan hawaye..
girgiza mata kai tayi,zainaba nasha fada miki ke jinin sarauta ce ba'a san'mu da zubar da hawaye haka ba kaskancine a garemu....
Zainaba ta goge fuskarta..
Toh umma na daina..
Juwairiya dake tsaye fulani ta kalla,sannan ta maida kallonta ga zainaba..
Ya baiwar taki?
Zainaba tayi murmushi,tana kula dani sosai umma sannan ta iya aikinta tana da kokari ..
Laure dake zaune ta saki lumfashi..
*********
'Sai da daddare bayan uwar dakin tata ta samu barci sannan a gajiye ta fito daga sashen tana hamma..cike da gajiya dan zainaba akwai shegen son yawo..
Tafiya takeyi cikin duhu sai dan hasken farin wata dake haska mata hanyar kadan..
Maganganu ta fara jiyowa a tsorace ta shiga kalle kalle..
Can ta hango inuwar mutane biyu dake can wani lungu..
Da sauri ta karawa tafiyar tata sauri amma me sai taji kamar muryar TALATU wata sabowar baiwa da'a kawo shekaran jiya..
A hankali ta shiga labewa tana karasawa wajen duk da zuciyarta cike take da tsoro..
Ware ido tayi ta dafe kirjinta ganin wani katon gardi yana neman ya'ge rigar dake jikin talatu dai fisgiwa takeyi amma ina.... yafi karfinta..
Juwairiya ta rasa yadda zatayi gashi mutunen ya juya baya sai dai tufafin dake jikinsa ya nuna mata dan gidan masu dashi ne..
Har ta juya zata wuce sai kuma ta tuna mgnr mahaifiyarta inda take ce mata idan har taga mutum cikin bukatar taimako toh lallai ta taimaka masa ..
Sauke ajiyar zuciyar tayi kafin tayi saurin karasawa wajen wasu fadawa dake tsaron kofar babban zaure..
Dan Allah ku taimaka min wata baiwa na cikin neman taimakon ku, da sauri suka bi bayanta,sai dai suna kawowa wajen suka ja suka tsaya,juwairiya ta kalle su,daya daga cikinsu yace yarinya kiyi hakuri amma nan ba hurumin mu bane ba kema idan har kina son rayuwarki tayi tsawo acikin masarautar nan toh ki kama hanyar gaban ki..
Juwairiya na kallonsu suka fice,ta dafe kanta yau ta shiga uku yanzu ya zatayi kenan?
Dubara ce tazo mata,se data je saitin inda suke har mutumen yayi nasarar kwantar da talatu a kasa ta daga murya sosai tana fadin..
Talatu ! Talatu wai ina kika shigane haka!
Jin an ambaci sunan talatu kuma tabbas wajen da suke ne aka nufo,sai ya mike da saurin sa yabar wajen..
Da sauri juwairiya ta karasa wajen tana kallon talatu dake kuka kamar ranta zai fita..
Tasa hannu ta dago ta tana rarrashin ta..
Suna shiga rumfar bayi hansai da du'bu dake zaune gaban wuta sukayi kansu..
Lafiya juwairiya ina kika tsaya haka?juwairiya ta kalli talatu dake bayanta tana goge kwallar bakin ciki..
Umma dama...
Ta sanar musu komai,nan matan bayi sukayi kan talatu cike da tausayawa suka shiga tambayar ta ko yayi sa'ar yi mata fyaden?ta girgiza musu kai nan aka shiga hamdala dan kuwa a wajen su bayi sun dade suna fuskantar irin wannan kalubalen sosai,ayi musu fyade a banzatar dasu kamar kayan wanki..
Lamarin nan ba karamin tashin hankalin hansai yayi ba,ta jawo juwairiya har daki ta tsaya tana kare wa jikinta kallo daga sama har kasa.. yarinya yar shekara goma amma duk halittun girma sun fara bayyanar mata,bata so kadan a ba'ta rayuwar diyarta dan kuwa a yanzu ji takeyi juwairiya kyauta ce daga Allah a garesu..
Ki zauna ki jirani ga abincin ki can a cikin dan chinan can..
Hansai na fita juwairiya ta jawo dan chinan tana kare ma tuwon dawar dake gabanta kallo,ta tuna da irin abincin da zainaba ta gama ci dazun,dafaffiyar kaza ce,miyar naman shanu ne,dambu dayaji zogaye da kayan lambu,ga juice din inibi ne da aka matse shi aka saka mazarkwaila aciki..
Ta girgiza kanta da sauri dan ganin ta fara hadiyar yawu,oh haka rayuwa take"ta saka hannu ta fara kai wa towun ta loma..
Hansai dakin jakadiya ta shiga suna zaune da laure suna yar firar su..
Hansai ta zauna tana saka tagumi.
Jakadiya tace lafiya hansa'u?
Hansai ta kallesu,ni fa hankalina a tashe yake wlh,kunfi kowa sanin irin rayuwar da BAYI mata suke fuskanta a wannan masarautar, ina tsoron wani abu ya faru da juwairiya ganin yarda yanzu ko wane dare ake samun matsalar fyaden nan..
Laure tace toh yanzu ya zamuyi?dan wannan yarinyar juwairiya da gani ba karamar mace za'ayi ba..
Jakadiya tace nima wlh ina cikin wannan tunanin amma miye abunyi?
Hansai tace,ga shawara duk suka kalleta..
TABO (scar )
Tabo kuma?duk suka tambayeta cike da rashin fahimtar abunda take nufi..
Hansai ta murmusa TABO zamuyiwa fuskarta dan babu abinda maza suka fi kyamata kamar TABO ajikin mace..duk wani basarake ko mai mulki da dukiya babu abunda ke saka shi kyamatar mace kamar TABO ...
Laure ta kwashe da dariya kuma fa hakane,dan ko kadan idan bayin dake kula dasu ko SA'DAKA ce suka samu wani dan Tabo ko Konewa a jikinsu toh fa a ranar ake canza musu su..
Jakadiya tace wannan hakane,hansai ta mike tace kuzo muje..
Juwairiya na faman sude kwano suka shigo,ta gaida su tana fadin,goggo laure ina alkawarina yake?
Laure tace ke fa yar nan baki mantuwa..
Hansai ce ta zauna a kusa da ita tace,juwairiya kina jina.....
Wattpad @afreey101
[9/18, 3:10 PM] Aysha Galadima: 🏕 *RUMFAR BAYI* 🏕
(A historical fiction)
Na Afrah bhai
Page 5
Wattpad @afreey101
************************
"Bayani sosai sukayi mata,a tsorace tace, ummana kada ki damu zanyi kokarin rike mutumcina insha Allahu..
'Jakadiya ta fita ta dawo da wani tire ta ajiye a gaban juwairiya, laure ta taso dan ita kam gwana ce sosai wajen harkar kwalliya nan duk masarautar ita tayi fice wajen yiwa matan sarki kwalliya ta fitar kunya..
Wasu abubuwa naga ta hada sannan ta riko kyakkyawar fuskar juwairiya ..
Cikin minti goma ta kammala sannan ta kalli hansai tace,ya kuka gani?
Bude baki sukayi duka dan kuwa duk wanda zai kalli fuskar juwairiya sai yayi tunanin konewa ba'rin fuskarta tayi..
Murmushi sukayi cike da farin ciki,jakadiya ta miko mata wasu kaya ta amsa tana kallonsu,kayane manya manya dan se a saka irin ta biyu a ciki,yanzu wannan sune suturunki kinaji?,juwairiya ta gyada kai.
**************
'Da asuba kuwa sai ga fadawa uku sun shigo Rumfar bayi,du'bu ce tayi saurin tare su..
Lafiya?
Fadane daya ne yace,daga gidan GALADIMA muke,yaronsa GARBATI yaga wata baiwa acikin rumfar nan jiya shine ya turo mu mu tafi da ita..
Gaba daya hankalinsu du'bu ya tashi dan sun fahimci garbati ya siya talatune a matsayin SA'DAKAr sa (concubine)..
Dakin da talatu ke ciki du'bu ta shiga ta fito da ita tana kuka sosai,fadawa suka fosgota suka gaba da ita..
'Juwairiya dake rakube duk tana kula da abunda yake faruwa,
'hansai ce ta kamota ta maida ita cikin daki,
'sannan ta sake yi mata nasiha akan kada ta sake a san tabon fuskarta na karyane inba haka ba itama haka za'a zo a tafi da ita kamar yarda aka dauke talatu..
gari na yin haske haka laure ta shigo ta sake yi mata makeup din tabon ta.
Tana shiga sashen zainaba ta tarar da ita tana ta sharar baccinta.
Ruwan wankanta ta shiga ta hado mata sannan ta zauna a gefe ta tsunduma a cikin tunani..
Zainaba ce ta mike taci karo da fuskar juwairiya, da sauri ta dauke kanta tace,ke meya samu fuskarki haka?konewa kikayi?
Juwairiya ta mike da sauri tace Allah ya huci zuciyar ki ranki shi dade jiya ne ruwan zafi ya kifar min a fuskata.
Zainaba tayi fuskar tausayi Allahu akbar yanzu haka fuskar ki zata zauna kenan?ta yamutsa fuska
Juwairiya tayi murmushi kawai sannan ta sanar mata data hada mata ruwan wankanta..
'Da rana zainaba tace da ita suje gidan waziri..
Fafade daya suka dauka dan yayi musu rakiya..
Duk inda suka bi sai mutane su shiga nuna juwairiya dake bayan zainaba'
A haka har suka shiga gidan waziri..
Hajara matarsa ce a zaune tsakar gidan sai diyarta KHADIJA dake gefe tana wasan diyar ka'ra..
'Zainaba na shigowa khadija ta mike da sauri tazo ta rungume ta..
Idonta ne yakai juwairiya dake can baya..
Taja baya kadan tana yastine fuska..
Wannan fa?ta nuna juwairiya..
Zainaba tayi murmushi sabowar baiwata ce..
Khadija tace,au ni tsoro ma ta bani wlh..
Zainaba tace konewa tayi fa,sannan ta karasa wajen hajara ta gaishe ta.
Suna zaune suna wasan su juwairiya na rakube a gefe tayi shiru abunta.
Khadija tayi fari da ido tace,wai ina ya jalal ne?kinsan tun ranar dana zo wajen ki rannan ban sake ganinsa ba..
Zainaba ta tabe baki ai ke ya da'ma ni muna gida daya ma se mufi sati bamu hadu dashi ba..
Sunyi fira sai da yamma sannan khadija ta shirya suka taho tare wai ita a dole sai taga yarima yau..
"Suna shiga cikin masarautar can a filin wasa doki ta kyallo shi a tsaye tare da wasu samari sa'annin shi..
idanunsa ne suka sauka akan juwairiya dake tsaye a bayan zainaba bata da ko niyyar dukawa ta gaishe shi..
Ke!
Ya fada yana yastine fuska..
Juwairiya ta dago suka hada ido,dauke kansa yayi..
"Na lura har yanzu baki san matsayin ki ba ko?
Sake dukar da kanta tayi tace'barka da fitowa ranka shi dade..
Yarima ya tabe baki sannan ya maida kallonsa kansu turaki..
Zainaba ta daure fuska Allah ya gani bata son girman kai da isa da ikon da ya jalal yake ji dashi..
Lafiya?...yarima ya fada yana musu kallon me kuke a nan?..
Turaki ya murmusa babu komai dama wucewa muka zo yi..
Yarima ya tabe baki ya karasa wajen do'kin sa wani bawa ya taimaka masa ya haye sama abunsa....
Zainaba kuwa ta banka wa turaki harara sannan ta juya a fusace tayi gaba,juwairiya tayi saurin bin bayanta ..
"Fulani ce a zaune saman kilisar ta laure na mata tausar kafa suka shigo bayan anyi musu iso..
Zainaba ta fada jikin fulani tana kukan shagwaba,fulani wai me yasa a gidan nan ne akafi girmama su UMMA babba (gimbiya kilishi kenan) da su yaya YARIMA?akan mu?
Naga ai mu ma baban mu daya dasu ko?tunda duk mai martaba ne ya haife mu..
Fulani ta sa hannu ta dago fuskarta'da ta fara ji'kewa da ruwan hawaye..
girgiza mata kai tayi,zainaba nasha fada miki ke jinin sarauta ce ba'a san'mu da zubar da hawaye haka ba kaskancine a garemu....
Zainaba ta goge fuskarta..
Toh umma na daina..
Juwairiya dake tsaye fulani ta kalla,sannan ta maida kallonta ga zainaba..
Ya baiwar taki?
Zainaba tayi murmushi,tana kula dani sosai umma sannan ta iya aikinta tana da kokari ..
Laure dake zaune ta saki lumfashi..
*********
'Sai da daddare bayan uwar dakin tata ta samu barci sannan a gajiye ta fito daga sashen tana hamma..cike da gajiya dan zainaba akwai shegen son yawo..
Tafiya takeyi cikin duhu sai dan hasken farin wata dake haska mata hanyar kadan..
Maganganu ta fara jiyowa a tsorace ta shiga kalle kalle..
Can ta hango inuwar mutane biyu dake can wani lungu..
Da sauri ta karawa tafiyar tata sauri amma me sai taji kamar muryar TALATU wata sabowar baiwa da'a kawo shekaran jiya..
A hankali ta shiga labewa tana karasawa wajen duk da zuciyarta cike take da tsoro..
Ware ido tayi ta dafe kirjinta ganin wani katon gardi yana neman ya'ge rigar dake jikin talatu dai fisgiwa takeyi amma ina.... yafi karfinta..
Juwairiya ta rasa yadda zatayi gashi mutunen ya juya baya sai dai tufafin dake jikinsa ya nuna mata dan gidan masu dashi ne..
Har ta juya zata wuce sai kuma ta tuna mgnr mahaifiyarta inda take ce mata idan har taga mutum cikin bukatar taimako toh lallai ta taimaka masa ..
Sauke ajiyar zuciyar tayi kafin tayi saurin karasawa wajen wasu fadawa dake tsaron kofar babban zaure..
Dan Allah ku taimaka min wata baiwa na cikin neman taimakon ku, da sauri suka bi bayanta,sai dai suna kawowa wajen suka ja suka tsaya,juwairiya ta kalle su,daya daga cikinsu yace yarinya kiyi hakuri amma nan ba hurumin mu bane ba kema idan har kina son rayuwarki tayi tsawo acikin masarautar nan toh ki kama hanyar gaban ki..
Juwairiya na kallonsu suka fice,ta dafe kanta yau ta shiga uku yanzu ya zatayi kenan?
Dubara ce tazo mata,se data je saitin inda suke har mutumen yayi nasarar kwantar da talatu a kasa ta daga murya sosai tana fadin..
Talatu ! Talatu wai ina kika shigane haka!
Jin an ambaci sunan talatu kuma tabbas wajen da suke ne aka nufo,sai ya mike da saurin sa yabar wajen..
Da sauri juwairiya ta karasa wajen tana kallon talatu dake kuka kamar ranta zai fita..
Tasa hannu ta dago ta tana rarrashin ta..
Suna shiga rumfar bayi hansai da du'bu dake zaune gaban wuta sukayi kansu..
Lafiya juwairiya ina kika tsaya haka?juwairiya ta kalli talatu dake bayanta tana goge kwallar bakin ciki..
Umma dama...
Ta sanar musu komai,nan matan bayi sukayi kan talatu cike da tausayawa suka shiga tambayar ta ko yayi sa'ar yi mata fyaden?ta girgiza musu kai nan aka shiga hamdala dan kuwa a wajen su bayi sun dade suna fuskantar irin wannan kalubalen sosai,ayi musu fyade a banzatar dasu kamar kayan wanki..
Lamarin nan ba karamin tashin hankalin hansai yayi ba,ta jawo juwairiya har daki ta tsaya tana kare wa jikinta kallo daga sama har kasa.. yarinya yar shekara goma amma duk halittun girma sun fara bayyanar mata,bata so kadan a ba'ta rayuwar diyarta dan kuwa a yanzu ji takeyi juwairiya kyauta ce daga Allah a garesu..
Ki zauna ki jirani ga abincin ki can a cikin dan chinan can..
Hansai na fita juwairiya ta jawo dan chinan tana kare ma tuwon dawar dake gabanta kallo,ta tuna da irin abincin da zainaba ta gama ci dazun,dafaffiyar kaza ce,miyar naman shanu ne,dambu dayaji zogaye da kayan lambu,ga juice din inibi ne da aka matse shi aka saka mazarkwaila aciki..
Ta girgiza kanta da sauri dan ganin ta fara hadiyar yawu,oh haka rayuwa take"ta saka hannu ta fara kai wa towun ta loma..
Hansai dakin jakadiya ta shiga suna zaune da laure suna yar firar su..
Hansai ta zauna tana saka tagumi.
Jakadiya tace lafiya hansa'u?
Hansai ta kallesu,ni fa hankalina a tashe yake wlh,kunfi kowa sanin irin rayuwar da BAYI mata suke fuskanta a wannan masarautar, ina tsoron wani abu ya faru da juwairiya ganin yarda yanzu ko wane dare ake samun matsalar fyaden nan..
Laure tace toh yanzu ya zamuyi?dan wannan yarinyar juwairiya da gani ba karamar mace za'ayi ba..
Jakadiya tace nima wlh ina cikin wannan tunanin amma miye abunyi?
Hansai tace,ga shawara duk suka kalleta..
TABO (scar )
Tabo kuma?duk suka tambayeta cike da rashin fahimtar abunda take nufi..
Hansai ta murmusa TABO zamuyiwa fuskarta dan babu abinda maza suka fi kyamata kamar TABO ajikin mace..duk wani basarake ko mai mulki da dukiya babu abunda ke saka shi kyamatar mace kamar TABO ...
Laure ta kwashe da dariya kuma fa hakane,dan ko kadan idan bayin dake kula dasu ko SA'DAKA ce suka samu wani dan Tabo ko Konewa a jikinsu toh fa a ranar ake canza musu su..
Jakadiya tace wannan hakane,hansai ta mike tace kuzo muje..
Juwairiya na faman sude kwano suka shigo,ta gaida su tana fadin,goggo laure ina alkawarina yake?
Laure tace ke fa yar nan baki mantuwa..
Hansai ce ta zauna a kusa da ita tace,juwairiya kina jina.....
Wattpad @afreey101
[9/18, 3:10 PM] Aysha Galadima: 🏕 *RUMFAR BAYI* 🏕
(A historical fiction)
Na Afrah bhai
Page 5
Wattpad @afreey101
************************
"Bayani sosai sukayi mata,a tsorace tace, ummana kada ki damu zanyi kokarin rike mutumcina insha Allahu..
'Jakadiya ta fita ta dawo da wani tire ta ajiye a gaban juwairiya, laure ta taso dan ita kam gwana ce sosai wajen harkar kwalliya nan duk masarautar ita tayi fice wajen yiwa matan sarki kwalliya ta fitar kunya..
Wasu abubuwa naga ta hada sannan ta riko kyakkyawar fuskar juwairiya ..
Cikin minti goma ta kammala sannan ta kalli hansai tace,ya kuka gani?
Bude baki sukayi duka dan kuwa duk wanda zai kalli fuskar juwairiya sai yayi tunanin konewa ba'rin fuskarta tayi..
Murmushi sukayi cike da farin ciki,jakadiya ta miko mata wasu kaya ta amsa tana kallonsu,kayane manya manya dan se a saka irin ta biyu a ciki,yanzu wannan sune suturunki kinaji?,juwairiya ta gyada kai.
**************
'Da asuba kuwa sai ga fadawa uku sun shigo Rumfar bayi,du'bu ce tayi saurin tare su..
Lafiya?
Fadane daya ne yace,daga gidan GALADIMA muke,yaronsa GARBATI yaga wata baiwa acikin rumfar nan jiya shine ya turo mu mu tafi da ita..
Gaba daya hankalinsu du'bu ya tashi dan sun fahimci garbati ya siya talatune a matsayin SA'DAKAr sa (concubine)..
Dakin da talatu ke ciki du'bu ta shiga ta fito da ita tana kuka sosai,fadawa suka fosgota suka gaba da ita..
'Juwairiya dake rakube duk tana kula da abunda yake faruwa,
'hansai ce ta kamota ta maida ita cikin daki,
'sannan ta sake yi mata nasiha akan kada ta sake a san tabon fuskarta na karyane inba haka ba itama haka za'a zo a tafi da ita kamar yarda aka dauke talatu..
gari na yin haske haka laure ta shigo ta sake yi mata makeup din tabon ta.
Tana shiga sashen zainaba ta tarar da ita tana ta sharar baccinta.
Ruwan wankanta ta shiga ta hado mata sannan ta zauna a gefe ta tsunduma a cikin tunani..
Zainaba ce ta mike taci karo da fuskar juwairiya, da sauri ta dauke kanta tace,ke meya samu fuskarki haka?konewa kikayi?
Juwairiya ta mike da sauri tace Allah ya huci zuciyar ki ranki shi dade jiya ne ruwan zafi ya kifar min a fuskata.
Zainaba tayi fuskar tausayi Allahu akbar yanzu haka fuskar ki zata zauna kenan?ta yamutsa fuska
Juwairiya tayi murmushi kawai sannan ta sanar mata data hada mata ruwan wankanta..
'Da rana zainaba tace da ita suje gidan waziri..
Fafade daya suka dauka dan yayi musu rakiya..
Duk inda suka bi sai mutane su shiga nuna juwairiya dake bayan zainaba'
A haka har suka shiga gidan waziri..
Hajara matarsa ce a zaune tsakar gidan sai diyarta KHADIJA dake gefe tana wasan diyar ka'ra..
'Zainaba na shigowa khadija ta mike da sauri tazo ta rungume ta..
Idonta ne yakai juwairiya dake can baya..
Taja baya kadan tana yastine fuska..
Wannan fa?ta nuna juwairiya..
Zainaba tayi murmushi sabowar baiwata ce..
Khadija tace,au ni tsoro ma ta bani wlh..
Zainaba tace konewa tayi fa,sannan ta karasa wajen hajara ta gaishe ta.
Suna zaune suna wasan su juwairiya na rakube a gefe tayi shiru abunta.
Khadija tayi fari da ido tace,wai ina ya jalal ne?kinsan tun ranar dana zo wajen ki rannan ban sake ganinsa ba..
Zainaba ta tabe baki ai ke ya da'ma ni muna gida daya ma se mufi sati bamu hadu dashi ba..
Sunyi fira sai da yamma sannan khadija ta shirya suka taho tare wai ita a dole sai taga yarima yau..
"Suna shiga cikin masarautar can a filin wasa doki ta kyallo shi a tsaye tare da wasu samari sa'annin shi..