Sashe 31
Rumfar Bayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Surayya taja tsaki tana tuna lkcn da yarima ya fadawa zainaba ta basa ita(lkcn a cikin lambu).
tabbas ko ba shi bane dole ne ta koyawa wannan yarinyar hankali!!!harma ta isa ta hada miji da ita?ai ko a matsayin SA'DAKA baza ta taba bari yarinyar ta shigo rayuwar jalal dinta ba..dole ne tasan abunyi,
dan zuciyarta ta dade da zargin yarima da wannan yarinyar,
abu dayane kawai zai iya raba su idan ita yarinyar ce ta tona masa asiri a cikin al'ummar sa ta fadi meke tsakaninsu...
ta tabbata jalal bazai taba yafe mata ba, ace kamar shi sarki yana kebewa da baiwarsa a lungu cikin dare,ai girma sa ya gama zubewa a ikon mutane..
Umayma ta kalla tace, kije ki kiramin da ita..
Umayma tace,kin samu wani mafita ne?
Surayya tayi murmushin mugunta,dole ne itama ta dan rama dizgata da jalal yakeyi...
****************
"Juwairiya kam ta gama shirin ta tsab ta dauko sarkar da yarima ya bata jiya data cire ta boyeta..
Murmushi ta sakar kamin ta mike ta fito..
Karo sukaci da umaymah..
Umayma ta kalleta fuska a daure..
Kije uwar dakina na kiran ki..
Juwairiya taji gabanta ya fadi..
Tana kirana?
Umayma tace,kwarai sannan tayi gaba..
"Lkcn da juwairiya ta isa sashen surayya a waje ta tarar da ita zaune akan kujera tana shan kamshi tana ka'da kafarta.
Juwairiya na shirin gaishe da ita taga wasu bayi su biyu sun finciko ta ta fadi a gaban surayya..
Surayya ta banka mata harara kafin tace..
'Na lura baki gama sanin matsayin ki a wannan masarautar ba ko?
Juwairiya ta duka da kai..
Surayya tace,dake nake mgn !
Juwairiya tace na sani ranki ya dade.
Surayya a fusace ta damko gashin kan juwairiya dake lullube cikin mayafi,tana kallon fuskarta tace, da wa aka kama ki jiya daddare?waye shi!!!!!!
Juwairiya gabanta nata faduwa,ta rasa wace amsa zata bata dan kuwa ko kashe ta zatayi zataba taba fadin sunan jalal ba..
Surayya ta kara kolewa..
tasa kafa ta hankade ta gefe..
Tunda bazaki fada min a lallama ba ina tunanin zaki fi son fadawa SARKIN DORINA !ko!!!!
Da sauri juwairiya ta dago ta kalleta idanuwanta kamar zasu zazzago sbd tsabagen tsoron daya shige ta.
Jiki na rawa ta rarrafo gaban surayya ta shiga bata hkr tana zubar da hawaye masu ciwo.
Surayya tayi murmushin takaici kafin ta kalli baiwar dake bayanta tace,ku dauke min ita daga gabana sannan ku Kaita can RUMFAR HUKUNTA BAYI inaso sarkin dorina ya tabbatar da ta fadi sunan wannan mutumin kafin yamma...
Bayin sukazo suka dauke juwairiya sai kuka take gwanin tausayi..
Umayma tabi bayan surayya da sauri tana fadin..
Lallai ranki shi dade na yaba da hankalinki..
Kinga yanzu koma waye juwairiya take boyewa dolen ta ta fada mana,sannan idan tayi kuskuren furta sunan sarki jalal ko gimbiya kilishi kadai ta isa ta hallakar mana da ita..
Surayya tayi murmushin mugunta tabbas hakane umayma...
**************
"Tunda aka taho da juwairiya daga sashen surayya bayin dake kan layin suka hau rike baki suna tauyawa kaddararta...
An shiga da ita RUMFAR HUKUNTA BAYI sarkin dorina ya saka aka kwantar masa da ita flat..
Ya dawo wajen da kanta yake..
jikinta sai rawa yakeyi sbd tsoro..ta dago ta kalli jajayen idanunsa..
Cikin kakkausar murya yace..
Ki fada min sunan wanda aka kama ki dashi jiya daddare!!!!!
Juwairiya ta cije harshe ga mugun tsoron da takeji amma bazata iya taba fadin sunan shi ba..
Sarkin dorina yace,toh shikenan tunda girman kai ne dake ina tunanin wannan itace maganin ki...ya nuna katuwar dorinar dake hannunsa..
Ya dawo daidai saitin tafin kafarta ya shauda mata ita cikin kwarewarsa..
*****************
A hankali ahankali dai lbr ya fara yawo acikin masarautar..
Wannan bawan ya fadawa wancan baiwar gulma ta ko ina....
"Rabi Ce ta fito daga sashen khadija dan zuwa aiken ta..
Gani tayi bayi sai jinjina kai suke suna kusun'kusun..
Ta karasa wajen su ta shiga tambayar su dan tasan akwai lbr da dumin dumin sa..
Ware ido tayi ta dafe kirjinta...
Juwairiya aka kai RUMFAR HUKUNTA BAYI?
Ai da saurinta ta koma sashen khadija ta zube a kasa tana maida lumfashi..
Khadija ta kalleta da mamaki..
Ke kuma ya haka?
Ina aiken da nayi miki yake?
Rabi ta kalle ta..
Ranki shi dade lbr ne naji yanzun nan..
Wai gimbiya surayya ta saka akai juwairiya can RUMFAR HUKUNTA BAYI wajen sarkin dorina..
Khadija ta ware ido..
Wajen sarkin dorina fa kika ce?bama wajen du'bu a cikin RUMFAR BAYI ba?
Rabi tace wlh haka akace..
Khadija tace,lallai surayya bata da imani ko kadan..
Toh me tayi mata ne haka?
Koma zainaba taji lbrn abunda ke faruwa?
Rabi ta kwantar da murya tace,dan Allah ranki ya dade ki taimakawa juwairiya..
Khadija ta tabe baki,lallai wato so kike naje na zubda girmana a wajen surayya sbd wata baiwa can ko!lallai kuwa kinyi kadan!!!
Rabi tabi ta da kallon takaici,su dai mutanen nan basu da ko digin taisayi a cikin zuciyarsu,wato dan kawai kaga ta zubda girma da ajinta a gaban kishiyarta shine bazata iya taimakawa baiwar Allah ba..mtsww wata sa'in mulkin ma jaraba ne..
"Lbr ya gama circulating acikin masarautar daura har ya kai ga kunnen gimbiya kilishi...(wai surayya ta saka akai wata baiwa can RUMFAR HUKUNTA BAYI)
Kilishi ta kalli hansai dake mata fifita..
Lallai ya kamata na san irin takun da zanyi da wannan yarinyar surayya,
dan a yarda nake gani tazo ne da shirin shafe tarihina a cikin wannan masarautar..
Hansai(da bata da masaniyar diyarta ce wannan baiwar) ta jinjina kai tace..
ai Allah ya kara miki yawan rai,lbr ma har ya fara yawo akan,gimbiya surayya na kokari wajen siye zuciyar sarki jalal..dan ta samu dukkan (authority)a cikin masarautar nan..
Gimbiya kilishi cike da bakin ciki tace aikuwa tayi kadan ... (dan kuwa a duk fadin masarautar daura gimbiya kilishi ce kadai mace da ake tsoro kuma ake jin maganarta fiye data sarki...
amma a yarda take ganin taken taken surayya yanzu tana dab ne da dauke mata wannan matsayin da ta dade tana gina shi..)
********
Turaki na hango yana kokarin karasawa gaban fa'da dan amsa kiran sarki jalal..
Caraf kunnensa ya jiyo masa firar da wasu bayi sukeyi..
"Eh wlh wannan yarinyar me konannar fuskar nan ce,ai na tausaya mata wlh"
Ribas yayi ya dawo wajensu..yace..
Me naji kuna fada yanzu?
A tsorace duk suka zube kasa..
Allah ya kara maka yawan rai ayi mana afuwa..
Turaki yace,mgnr da kuke fada yanzu ita nake so naji...dan haka kuyi gaggawar sanar dani..
Daya daga cikinsu yace..
Dama ranka shi dade gimbiya surayya ce ta saka aka kai wata baiwa can RUMFAR HUKUNTA BAYI...
Gaban turaki ya fadi..a zuciyarsa yace..
Juwairiya ce...
Ai da sauri ya juya ya fice ko shiga cikin fa'dar ma fasawa yayi...
"Zabba'u ta shigo falon zainaba a rikicenta..
Uwar dakina kinji lbrn da naji yanzu..
Zainaba dake hakimce akan kilisar ta tace..
Wane lbr ne haka daya rikita ki..
Zabba'u ta zube akasa..
Juwairiya ce juwairiya ce ranki ya dade gimbiya surayya ta saka aka kai can RUMFAR HUKUNTA BAYI...
Mai!!!!!
Zainaba ta mike da sauri,surayya!! Me juwairiya tayi mata haka?
Jiki na rawa ta mike tace wa zabba'u muje...
Can sashen surayya ta shiga kai tsaye,ta tarar da ita hakimce tana cin kayan marmari ga bayi nan nata mata hidima..
Zainaba rai a bace tace..
Matar yaya,inaso kije ki saka a saki juwairiya yanzu..
Surayya tayi murmushi,tace..
Zainaba ina tunanin kin manta da wacce kike mgn ko?
Ta nuna kanta,gimbiya surayya ce fa uwar gidan sarki jalal..
Kuma akan mgnr wannan yarinyar bazan taba bari ta tafi ba tare da an hukunta min ita ba,dan haka zaki iya tafiya..
Zainaba a fusace ta fita..
Ta koma sashen fulani,nan ma babu sa'a,
'samira kawai ce tabi bayanta tana dan bata baki akan tayi hakuri sannan tayi tunani idan akwai wanda take ganin ze iya taimaka mata taje wajensa..
Zainaba ta jinjina kai kafin ta mike da gudu ta fice...
*******
Jalal kuwa baya da masaniya a kan komai ke faruwa.
Dan tunda ya shigo fada bai samu fita ba..
Ga zuciyarsa dake ta azazzalar sa da son ganin juwairiya, kome ya hanata zuwa yau da safe oho?ko rashin lafiyar ne ya dawo?
Magaji ne ya dafa sa..
AMELE ina ganin ya kamata kaje ka huta hakanan..
Jalal yayi mika cike da gajiya yace..
Yanzun nan kuwa dan ba karamin aiki nasha yau din nan ba..
Magaji yayi dariya ai na lura hanklinka ma ya fara barin wajen nan..
Jalal ya mike fadawa suka zo suka zagaye shi suna masa kirari..
Har ya fito daga fa'da sai ga zainaba ta karaso wajen hankalinta a tashe...
Jalal ya kalleta yace,lafiya zainaba?
Zainaba ta karasa kusa dashi tace ya jalal ina son mgn dakai a sirri..
Jalal cike da mamaki ya sallami fadawan wajen sannan ya maida hankalinsa wajenta..
Zainaba ta fashe da kuka...
Ya jalal bani da wanda zai taimake ni sai kai..
Jalal yace taimakon me kike so kanwata?
Zainaba tace,dan Allah ya jalal kaje ka umarci surayya da ta dauke hukuncin da ta saka ayi wa Juwairiya a RUMFAR HUKUNTA BAYI...
Dum dum dum kakaji zuciyar jalal na bugawa..
Mai!!!!!kike nufi da surayya na hukunta juwairiya? ????
ya fada cikin mugun tashin hankali...!!!!
Zainaba tace,nima ban san dalili ba amma wlh yaya juwairiya na cikin halin taimakon mu..
A rikice sosai jalal yace muje...
Zainaba ta sauke ajiyar zuciya dama ta sani ya jalal ne kawai zai iya ceton juwairiya daga wajen surayya tunda taje har wajen fulani amma tace bazata saka baki a cikin harkar surukan kilishi ba dan bata son wani tashin hankali ya shiga tsakani....
(Haka gidan sarauta yake,kowa na kokarin minding business dinsa)
********
"Juwairiya ba karamin jigata tayi ba dan har tafin kafarta sai da duk ya fashe jini nata fita..
Surayya ce ta shigo wajen tare da umayma a bayanta..
Sarkin dorina ta kalla..
Ina fata ka samo min amsar tambayata..waye wannan mutumin da aka kama ta da shi jiya!!!!
"NI NE NAN"
taji an fada daga bayansu...
Gaba dayansu suka juya cikin tsantsar mamaki suke kallonsa....
surayya da umayma idanuwansu kamar zasu fado kasa...
Bakinta na rawa tace....
Dama kaine...?
Ya karaso har gabanta yace..
NI NE na kirata jiya daddare..
Surayya ta kura masa ido..
tabbas ko ba shi bane dole ne ta koyawa wannan yarinyar hankali!!!harma ta isa ta hada miji da ita?ai ko a matsayin SA'DAKA baza ta taba bari yarinyar ta shigo rayuwar jalal dinta ba..dole ne tasan abunyi,
dan zuciyarta ta dade da zargin yarima da wannan yarinyar,
abu dayane kawai zai iya raba su idan ita yarinyar ce ta tona masa asiri a cikin al'ummar sa ta fadi meke tsakaninsu...
ta tabbata jalal bazai taba yafe mata ba, ace kamar shi sarki yana kebewa da baiwarsa a lungu cikin dare,ai girma sa ya gama zubewa a ikon mutane..
Umayma ta kalla tace, kije ki kiramin da ita..
Umayma tace,kin samu wani mafita ne?
Surayya tayi murmushin mugunta,dole ne itama ta dan rama dizgata da jalal yakeyi...
****************
"Juwairiya kam ta gama shirin ta tsab ta dauko sarkar da yarima ya bata jiya data cire ta boyeta..
Murmushi ta sakar kamin ta mike ta fito..
Karo sukaci da umaymah..
Umayma ta kalleta fuska a daure..
Kije uwar dakina na kiran ki..
Juwairiya taji gabanta ya fadi..
Tana kirana?
Umayma tace,kwarai sannan tayi gaba..
"Lkcn da juwairiya ta isa sashen surayya a waje ta tarar da ita zaune akan kujera tana shan kamshi tana ka'da kafarta.
Juwairiya na shirin gaishe da ita taga wasu bayi su biyu sun finciko ta ta fadi a gaban surayya..
Surayya ta banka mata harara kafin tace..
'Na lura baki gama sanin matsayin ki a wannan masarautar ba ko?
Juwairiya ta duka da kai..
Surayya tace,dake nake mgn !
Juwairiya tace na sani ranki ya dade.
Surayya a fusace ta damko gashin kan juwairiya dake lullube cikin mayafi,tana kallon fuskarta tace, da wa aka kama ki jiya daddare?waye shi!!!!!!
Juwairiya gabanta nata faduwa,ta rasa wace amsa zata bata dan kuwa ko kashe ta zatayi zataba taba fadin sunan jalal ba..
Surayya ta kara kolewa..
tasa kafa ta hankade ta gefe..
Tunda bazaki fada min a lallama ba ina tunanin zaki fi son fadawa SARKIN DORINA !ko!!!!
Da sauri juwairiya ta dago ta kalleta idanuwanta kamar zasu zazzago sbd tsabagen tsoron daya shige ta.
Jiki na rawa ta rarrafo gaban surayya ta shiga bata hkr tana zubar da hawaye masu ciwo.
Surayya tayi murmushin takaici kafin ta kalli baiwar dake bayanta tace,ku dauke min ita daga gabana sannan ku Kaita can RUMFAR HUKUNTA BAYI inaso sarkin dorina ya tabbatar da ta fadi sunan wannan mutumin kafin yamma...
Bayin sukazo suka dauke juwairiya sai kuka take gwanin tausayi..
Umayma tabi bayan surayya da sauri tana fadin..
Lallai ranki shi dade na yaba da hankalinki..
Kinga yanzu koma waye juwairiya take boyewa dolen ta ta fada mana,sannan idan tayi kuskuren furta sunan sarki jalal ko gimbiya kilishi kadai ta isa ta hallakar mana da ita..
Surayya tayi murmushin mugunta tabbas hakane umayma...
**************
"Tunda aka taho da juwairiya daga sashen surayya bayin dake kan layin suka hau rike baki suna tauyawa kaddararta...
An shiga da ita RUMFAR HUKUNTA BAYI sarkin dorina ya saka aka kwantar masa da ita flat..
Ya dawo wajen da kanta yake..
jikinta sai rawa yakeyi sbd tsoro..ta dago ta kalli jajayen idanunsa..
Cikin kakkausar murya yace..
Ki fada min sunan wanda aka kama ki dashi jiya daddare!!!!!
Juwairiya ta cije harshe ga mugun tsoron da takeji amma bazata iya taba fadin sunan shi ba..
Sarkin dorina yace,toh shikenan tunda girman kai ne dake ina tunanin wannan itace maganin ki...ya nuna katuwar dorinar dake hannunsa..
Ya dawo daidai saitin tafin kafarta ya shauda mata ita cikin kwarewarsa..
*****************
A hankali ahankali dai lbr ya fara yawo acikin masarautar..
Wannan bawan ya fadawa wancan baiwar gulma ta ko ina....
"Rabi Ce ta fito daga sashen khadija dan zuwa aiken ta..
Gani tayi bayi sai jinjina kai suke suna kusun'kusun..
Ta karasa wajen su ta shiga tambayar su dan tasan akwai lbr da dumin dumin sa..
Ware ido tayi ta dafe kirjinta...
Juwairiya aka kai RUMFAR HUKUNTA BAYI?
Ai da saurinta ta koma sashen khadija ta zube a kasa tana maida lumfashi..
Khadija ta kalleta da mamaki..
Ke kuma ya haka?
Ina aiken da nayi miki yake?
Rabi ta kalle ta..
Ranki shi dade lbr ne naji yanzun nan..
Wai gimbiya surayya ta saka akai juwairiya can RUMFAR HUKUNTA BAYI wajen sarkin dorina..
Khadija ta ware ido..
Wajen sarkin dorina fa kika ce?bama wajen du'bu a cikin RUMFAR BAYI ba?
Rabi tace wlh haka akace..
Khadija tace,lallai surayya bata da imani ko kadan..
Toh me tayi mata ne haka?
Koma zainaba taji lbrn abunda ke faruwa?
Rabi ta kwantar da murya tace,dan Allah ranki ya dade ki taimakawa juwairiya..
Khadija ta tabe baki,lallai wato so kike naje na zubda girmana a wajen surayya sbd wata baiwa can ko!lallai kuwa kinyi kadan!!!
Rabi tabi ta da kallon takaici,su dai mutanen nan basu da ko digin taisayi a cikin zuciyarsu,wato dan kawai kaga ta zubda girma da ajinta a gaban kishiyarta shine bazata iya taimakawa baiwar Allah ba..mtsww wata sa'in mulkin ma jaraba ne..
"Lbr ya gama circulating acikin masarautar daura har ya kai ga kunnen gimbiya kilishi...(wai surayya ta saka akai wata baiwa can RUMFAR HUKUNTA BAYI)
Kilishi ta kalli hansai dake mata fifita..
Lallai ya kamata na san irin takun da zanyi da wannan yarinyar surayya,
dan a yarda nake gani tazo ne da shirin shafe tarihina a cikin wannan masarautar..
Hansai(da bata da masaniyar diyarta ce wannan baiwar) ta jinjina kai tace..
ai Allah ya kara miki yawan rai,lbr ma har ya fara yawo akan,gimbiya surayya na kokari wajen siye zuciyar sarki jalal..dan ta samu dukkan (authority)a cikin masarautar nan..
Gimbiya kilishi cike da bakin ciki tace aikuwa tayi kadan ... (dan kuwa a duk fadin masarautar daura gimbiya kilishi ce kadai mace da ake tsoro kuma ake jin maganarta fiye data sarki...
amma a yarda take ganin taken taken surayya yanzu tana dab ne da dauke mata wannan matsayin da ta dade tana gina shi..)
********
Turaki na hango yana kokarin karasawa gaban fa'da dan amsa kiran sarki jalal..
Caraf kunnensa ya jiyo masa firar da wasu bayi sukeyi..
"Eh wlh wannan yarinyar me konannar fuskar nan ce,ai na tausaya mata wlh"
Ribas yayi ya dawo wajensu..yace..
Me naji kuna fada yanzu?
A tsorace duk suka zube kasa..
Allah ya kara maka yawan rai ayi mana afuwa..
Turaki yace,mgnr da kuke fada yanzu ita nake so naji...dan haka kuyi gaggawar sanar dani..
Daya daga cikinsu yace..
Dama ranka shi dade gimbiya surayya ce ta saka aka kai wata baiwa can RUMFAR HUKUNTA BAYI...
Gaban turaki ya fadi..a zuciyarsa yace..
Juwairiya ce...
Ai da sauri ya juya ya fice ko shiga cikin fa'dar ma fasawa yayi...
"Zabba'u ta shigo falon zainaba a rikicenta..
Uwar dakina kinji lbrn da naji yanzu..
Zainaba dake hakimce akan kilisar ta tace..
Wane lbr ne haka daya rikita ki..
Zabba'u ta zube akasa..
Juwairiya ce juwairiya ce ranki ya dade gimbiya surayya ta saka aka kai can RUMFAR HUKUNTA BAYI...
Mai!!!!!
Zainaba ta mike da sauri,surayya!! Me juwairiya tayi mata haka?
Jiki na rawa ta mike tace wa zabba'u muje...
Can sashen surayya ta shiga kai tsaye,ta tarar da ita hakimce tana cin kayan marmari ga bayi nan nata mata hidima..
Zainaba rai a bace tace..
Matar yaya,inaso kije ki saka a saki juwairiya yanzu..
Surayya tayi murmushi,tace..
Zainaba ina tunanin kin manta da wacce kike mgn ko?
Ta nuna kanta,gimbiya surayya ce fa uwar gidan sarki jalal..
Kuma akan mgnr wannan yarinyar bazan taba bari ta tafi ba tare da an hukunta min ita ba,dan haka zaki iya tafiya..
Zainaba a fusace ta fita..
Ta koma sashen fulani,nan ma babu sa'a,
'samira kawai ce tabi bayanta tana dan bata baki akan tayi hakuri sannan tayi tunani idan akwai wanda take ganin ze iya taimaka mata taje wajensa..
Zainaba ta jinjina kai kafin ta mike da gudu ta fice...
*******
Jalal kuwa baya da masaniya a kan komai ke faruwa.
Dan tunda ya shigo fada bai samu fita ba..
Ga zuciyarsa dake ta azazzalar sa da son ganin juwairiya, kome ya hanata zuwa yau da safe oho?ko rashin lafiyar ne ya dawo?
Magaji ne ya dafa sa..
AMELE ina ganin ya kamata kaje ka huta hakanan..
Jalal yayi mika cike da gajiya yace..
Yanzun nan kuwa dan ba karamin aiki nasha yau din nan ba..
Magaji yayi dariya ai na lura hanklinka ma ya fara barin wajen nan..
Jalal ya mike fadawa suka zo suka zagaye shi suna masa kirari..
Har ya fito daga fa'da sai ga zainaba ta karaso wajen hankalinta a tashe...
Jalal ya kalleta yace,lafiya zainaba?
Zainaba ta karasa kusa dashi tace ya jalal ina son mgn dakai a sirri..
Jalal cike da mamaki ya sallami fadawan wajen sannan ya maida hankalinsa wajenta..
Zainaba ta fashe da kuka...
Ya jalal bani da wanda zai taimake ni sai kai..
Jalal yace taimakon me kike so kanwata?
Zainaba tace,dan Allah ya jalal kaje ka umarci surayya da ta dauke hukuncin da ta saka ayi wa Juwairiya a RUMFAR HUKUNTA BAYI...
Dum dum dum kakaji zuciyar jalal na bugawa..
Mai!!!!!kike nufi da surayya na hukunta juwairiya? ????
ya fada cikin mugun tashin hankali...!!!!
Zainaba tace,nima ban san dalili ba amma wlh yaya juwairiya na cikin halin taimakon mu..
A rikice sosai jalal yace muje...
Zainaba ta sauke ajiyar zuciya dama ta sani ya jalal ne kawai zai iya ceton juwairiya daga wajen surayya tunda taje har wajen fulani amma tace bazata saka baki a cikin harkar surukan kilishi ba dan bata son wani tashin hankali ya shiga tsakani....
(Haka gidan sarauta yake,kowa na kokarin minding business dinsa)
********
"Juwairiya ba karamin jigata tayi ba dan har tafin kafarta sai da duk ya fashe jini nata fita..
Surayya ce ta shigo wajen tare da umayma a bayanta..
Sarkin dorina ta kalla..
Ina fata ka samo min amsar tambayata..waye wannan mutumin da aka kama ta da shi jiya!!!!
"NI NE NAN"
taji an fada daga bayansu...
Gaba dayansu suka juya cikin tsantsar mamaki suke kallonsa....
surayya da umayma idanuwansu kamar zasu fado kasa...
Bakinta na rawa tace....
Dama kaine...?
Ya karaso har gabanta yace..
NI NE na kirata jiya daddare..
Surayya ta kura masa ido..