← Book details Rumfar Bayi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 43 OF 53

Sashe 43

Rumfar Bayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Samira ta kalli turaki..
Yanzu me kake gani zamu iya yiwa yaya jalal na auren sa..
Turaki ya mike daga kwanciyar da yayi..
Ni a tunanina kawai mu hada masa liyafa ta gani ta fada..
Samira tadan muskuta tace ah ah ba wannan ba..ni nafi son muyi masa abun da zai bashi mamaki ko ya kika ce zainaba?
Zainaba data buga tagumi ta dago a sanyaye ta kallesu, ni kam bani da wani abun cewa duk abunda kukayi yayi min..
Nafisa ta dafa ta,kanwar mu kamar fa akwai abunda ke damun ki kwanan nan?
Hamza ya jaa hancinta yace,ai nafisa ki bar tambayar ta ma..
indai wannan ce yanzu haka fada tayi da wani..
Zainaba ta turo baki,haba ya hamza ni ka maida uwar fada ko?
Magaji ya kai wa hamza duka..
Wai me yasa kake matsa wa yar kanwarmu ne?
Turaki yace,wai ni fa wlh mamaki nakeyi,wai ya jalal ne da kansa ya samo wacce yake so....

Zainaba tace ai shine,mutum sai shegen girman kai da kasaita,ko fa matan sa naji ance hakuri sukeyi da shi..
Magaji yace, ai wlh dan baku ga wannan yarinyar nan bane ba,ta hadu karshe ne,amma duk da haka nayi mamaki nima dan Amale bai ma tsaya ganin ta ba ko a ina kuma suka hade oho?..

Samira tace,yanzu dai mu koma kan shawarar mu dan inaso idan su goggo Amina sunzo kawo amarya su sha mamaki..ko ba haka bane?
Nafisa tace, hakane kam..
amma ke baki san amaryar tamu bane samira?naji ance goggo ce matar sarkin kanon..
Samira ta girgiza kai,gsky ban san taba nima...
A haka dai sukayi ta shan fitar su cike da nishadi...

"Jalal kuwa tunda ya dawo yake ta faman shirye shiryen sa,sashen dake kusa da na nasa ya saka ake ta faman gyarawa..dan yana so sosai ya burge juwairiyyar tasa..

********************
*biki ya matso*

"Shirye shirye kawai akeyi babu kama hannu yaro...
Masarautun biyu duka basu zauna ba..
Ana ta gayyace gayyacen mutane..

Gimbiya kilishi da fulani sune a kan gaba wajen shirya bikin dan kuwa matan sarki kowacce langwabe wa tayi akan basa jin dadin jikinsu..

Khadija kanta taji saukin laulayin cikin nata,amma kishi ne kawai ya sake kwantar da ita dan har a cikin zuciyarta bata so wannan karin auren da yarima yake shirin yi ba.
gashi sai rawar jiki yake yi musu ita abun ma tsoro yake bata kada wannan amaryar ta sa ta shigo ta dauke masa hankali daga gare su..
Lallai suna da aiki jaa a gabansu..

*"Masarautar kanon dabo...*

      AMMI da sauran yan uwa daga kasar zazzau har sun sauka..
Yan biyu ne tare da juwairiya a can sashen nata inda gimbiya jamila ta dauko mata wata me gyaran jiki daga can kasar chadi tun ana saura sati uku daurin aure..

Gyara dai kam ba'a mgn dan kuwa fatar juwairiya kamar ta jajirai ta koma..
ga maganguna ana ta dirka mata ita har abun ma ya fara fita kanta..

"Ko yanzu ma Ammi ce ta shigo dakin nata da wani tsumin cikin kofi ta mika mata..
Yatsine fuska tayi,ammi tace amsa mana ki shnaye..

juwairiya ta amshi kofin tana fadin..
Wlh ammi na gaji ne da shan wadan nan magagungunan..ga daci wasu ke garesu..
Ammi tayi murmushi,shanye kedai bana son gardama..
Juwairiya ta daga kofin sama ta shanye shi duka tana yastine fuska..
Ammi tace ko ke fa?
Yan biyu ne suka dakin tare da yarimaADO..

   Ammi tace toj sarakan yawo se yanzu?
Hassana tace,kai ammi yarima ne fa yadan fita damu siyayya a waje..
Ammi ta mike zata fice take fadin..
Nidai kada ku riga jan hankalin juwairiya dan bana son tana yawan yawace yawacen nan..

Ammi na fita yan biyu suka haye kan gadon da juwairiya take a zaune..
YarimaADO yace,yaya kinga..
Ya nuna mata wata wasika..
juwairiya tace menene hakan?
hussaina tace,wasika ce daga angonki yarinya..
Hassana tace,lallai wannan sarki da iya soyayya yake..
Juwairiya ta saki murmushi..cikin kunya..
Yarima yace,yanzu ya za'ayi kenan yaya?tunda ba karatun kika gama iyawa ba..
Yan biyu suka kwashe da dariya kawai karanta kowa yaji Ado..ai mu iyayenta ne..

Juwairiya tayi saurin mikewa tayi wajen ado ta fisge wasikar daga hannunsa tana boyewa a bayanta...
Dariya sosai suka shigayi mata kafin duk suka fice daga dakin..

Juwairiya ta koma ta zauna a gefen gadon tana ji wani irin dadi na ratsa ta..Amalen ta ya aiko mata da wasika?wasikar soyayya....

Ta bude wasikar da sauri ta kura mata ido..
DAGA SARKI JALALLUDEEN zuwa SARAUNIYA JUWAIRIYYA haka ta gani a saman takardai..

  Murmushi ta saki,Allah ya sota ta dage wajen koyan karatun ta..
Kwanciya tayi shame shame kan gadon ta shiga karanta wasikar da kyal kyal tana hada(words)din....

Ta dauki kusan awa hudu...tana krnt wasikar..
Sai ga Hanne ta shigo tace,ki fito ranki ya dade me gyaran jiki na jiran ki..
juwairiya ta turo baki,nifa wlh na gaji da wannan gyaran..
Hanne tayi dariya,amma ai baki ga yarda kika canza bane?
Taso muje dan Allah..
Da kyal hanne taja ta suka tafi...

""""Sarki abu-turab sashe guda ya gyara dan saukar manyan bakinsa..
(ni kuwa ina yan RUMFAR BAYI grp,ko BQ ne ma a tanadar musu😅)

An kira mawaka da masu ki'da daga kowane yanki na nigeria, ga yan busa algaita da masu hawan doki sunzo daga kasashe daban daban..

   Masarautar kano ta cika ta batse,gobe kawai suke jira...dan shafa fatiha..

Mai martaba sarkin zazzau ma ya shigo da mutanen sa,su khaleed da sauran yaransa...
An shirya babbar kilisa a filin hawa...
Sannan a cikin gidan kuma mata na can ta hada'hadar KAMUN amarya...

"Tunda ga kasar Sudan gimbiya amina tayi odar kayan da juwairiya zata saka a wannan ranar..

Wayyo Allah zanso kuga irin kyau da kwarjinin da juwairiya tayi,tasha gwalagwalai har ta gaji,ga jan lalle da akayi mata ya fito da ita shar...

    Wajen KAMU kansa jakadiya ce da kanta da sauran bayin dake masarautar suka gyara shi...gwanin ban sha'awa..

   Abinci kam da kayan kwalam ba'a mgn dan sai anci an ture..ga masu gashin nama a gefe an yanka shanu bila adadin,farfesu dai na kowane dabba a kwashi a nan wajen..

  A can na hango muku yan Team rumfar bayi groups anja layi wajen rabon abinci...
Yan pherty novels anci anko din lace sai baza ido akeyi..
Yan WATTPADIANS kuwa har da su gayyar Sodi irinsu 😅😅 deejaaat,ceecyblack,haliemahtou 530_khadeejat da sauran su..
,sai ga kuma jama'ar Taskar marubuta suma sun shigo..
Kai waje dai ya cika ya batse da mutane..

Ammi na hango rike da hannun amarya juwairiya,sai PHERTY a dayan gefen(su babbar kawa manya😉)manya..
Wajen da aka tanadar domin ta suka zaunar da ita..
Juwairiya kanta na kasa dan gani takeyi kamar mafarki ne takeyi,wai yau itace zata auri sarki jalal..?

Pherty ce ta kamo hannunta..
Juwairiya ta kalleta tace,anty faty se nake ganin kamar mafarki ne nakeyi wlh?

Pherty ta girgirza mata kai,ba mafarki kike ba juwairiya ,me yasa bazaki yarda da CANJIN kaddarar da Allah yayi miki bane?
Muna bayanki dari bisa dari kada ki damu kinji?
Juwairiya ta saki murmushin murna nagode anty faty,sannan ki tayani mika godiyata a wajen anty Afrah,wadan nan bakin da sukazo domin Ni Allah ya biyasu da gidan aljanna.......

*********

A masarautar daura.....
An kammala komai da komai..
Jakadiya ta tara su hansai da laure a cikin daki ta warware musu zari da abawa..

   Suma ne kawai basuyi ba sbd tsananin mamaki..
Hansai harda kwallar farin ciki..
Shiyasa naga babanta ya dawo da yancinsa?oh shine ko ya sanar min..
Laure tace,amma naji dadi wlh,kice diyarmu zata dawo garemu..
Jakadiya tace,kwarai kuwa zata dawo amma a matsayin matar Sarki jalal..
   Wani sabon farin cikine suka sake shiga..
Allah me iko....
Ai gaba daya wani karfi ne yazo musu suka ci gaba da shirye shiryen da aka saka su na tarbar bakin gobe...

"""Gimbiya kilishi da fulani ne tsohon sarki Abdul-Jabbar yayi kiran su.
Yace,ina son gobe zainaba,turaki da matarsa sannan da magaji suka bi mu zuwa daurin auren  can kanon..
Fulani tace hakan ma yayi..
Gimbiya kilishi tace,nafisa da hamza se su tsaya a nan dan tayamu tarar bakin kenan?.
Abba ya jinjina kai..
Eh haka za'ayi...

"Umayma ce ta kalli surayya,ranki ya dade ya jikin naki?
Surayya ta dake dafe da cikinta tace,anya kuwa wannan maganin na malam bazai kashe ni ba umayma?.
Kinji azabar da nake sha kuwa?cikina tun jiya ko barcin kirki ban samu ba..

Umayma ta girgiza kai,kici gaba da daurewa uwar dakina..
  Surayya zatayi mgn sai ji sukayi ana sanar da shigowar jalal....
Ai da sauri surayya ta lulluba bargo a kanta tana wani sakin lumfashi kamar wata me shan jiki sosai da sosai din na..

  Jalal ya shigo ciki umayma ta gaishe shi ta fice..
Ya zauna a gefen gado yana kurawa surayya ido..
Ya jikin naki?
Ta bude ido ta kalleshi cike da kissa tace,da sauki sarkina ya shirin bikin kuma?
Jalal ya jinjina kai,muna tayi,yanzu ma nazo ne nayi miki sallama dan gobe da sassafe zamu tafi can kanon..
Surayya kamar ta fasa ihu..
Amma ta daure..
Ai da ace lfy ta kalau da dani za'aje na dauko kanwata..
Jalal ya saki murmushi har cikin zuciyarsa yana tausayawa matansa,tunda aka fara mgnr aurensa duk suka kwanta ciwo....

Ya mike yana ajiye mata wani kulli..
Ga wannan sarka ce ta gwal da na siya muku keda khadija na cin biki..
Surayya ta washe baki,mun gode sarkina Allah ya dawo mana daku lfy..
Ya duka ya sumbaci goshinta,nagode sosai surayya....sannan ya fice tani bayan sa da kallon takaici..

*RANA BATA KARYA***

Masarautar kano ta cika ta batse da mutane daga kowane lungu da sa'ko na nigeria...
      Sarki abu-turab ba karamin farin ciki yake ciki ba zai aurar da diyarsa..

Karfe sha daya na safe sai ga yan DAURA..sun dira..
Tsohon sarki Abdul-Jabbar suka hade da mai martaba sarkin zazzau fira ta dinke a tsakanin su..

Su Jalal kuwa sarki abu-turab ya saka yarimaADO da shamaki su kaisu can masaukin su dan hutawa kafin lkcn daurin auren yayi..

Su zainaba kuwa samira ce taja su zuwa cikin gidan nan dan ita kam masarautar ba bakuwar ta bace ba...
Chapter 43 · 0% Book details