Sashe 27
Rumfar Bayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
TEAM RUMFAR BAYI
[9/18, 3:22 PM] Aysha Galadima: *RUMFAR BAYI*
(A historical fiction)
Na Afrah bhai
Page 26
Wattpad @afreey101
******************
"Juwairiya na kallonshi har ya karaso zuwa gabanta ya tsaya..
"Kin hada min kayan?
Juwairiya tace,
yanzu na gama ranka shi dade..
Ya lumshe ido,
toh shiga ki hada min ruwa nayi wanka..
Juwairiya tace toh sannan tayi hanyar toilet da saurinta..
"Ta fito ta sanar masa ta gama,bai ce mata komai ba ya shige toilet din..
Yana shigane ta samu damar gyara masa dakin tsab..
Ta kalli kofar toilet din,ta kammala komai na aikinta amma sai ta samu kanta da rashin fita son daga cikin dakin..yau zayyi tafiya ko ba komai tana so suyi sallama..
Matse baki tayi sannan ta fita ta dawo falon ta zauna akasa dan jiransa..
Jalal na fitowa ya tarar babu ita a dakin,bai ji dadi ba kodan dan yaso ace yayi sallama da ita...
Sai daya dauki awa daya yana shiri kafin ya fito cikin shiga ta alfarma..
Caraf ya ganta a zaune ta rakube a waje daya..
Murmushi ya saki ya karasa wajen yana fadin..
"Ya baki tafi ba?
Juwairiya tayi saurin mikewa..
Uhm dama dama uhm yauwa jakadiya ce tace na jira ta a nan..
Ya jinjina kai dan zuciyarsa ta gama basa shi take jira...
Ji tayi kawai ya kamo hannunta ya nufi wajen shakatawar sa da ita..
Ya sake hannun nata sannan ya rufo kofar wajen.
Juwairiya gabanta ne ya shiga faduwa..
Jalal yace..
Yau zanyi tafiya...ya karashe mgnr cike da wani irin yanayi..
juwairiya ita kanta se dataji wani iri.. da murya me cike da sanyi ta samu kanta da fadin..
'Yaushe zaka dawo?
Ya kurawa kwayar idonta kallo..
Kwana biyune..
Juwairiya tayi murmushin yake tace..
Allah ya dawo dakai lfy ranka shi dade..
Jalal ya gyada kai..
Nagode..
Hayaniyar su shamaki ya jiyo daga waje..
Yaja lumfashi ni zan tafi..
Ta jinjina kai ta kasa furta komai..
Ya juya har ya kai bakin kofa ya sake juyowa..
Bai bata wani lkc ba ya janyo ta jikinsa..dan gaba daya kasa controlling zuciyarsa yayi..
Juwairiya taji gaba daya duniyar ta tsaya mata tsak...
Sai da suka shafe seconds talatin kafin yayi karfin halin sakinta ya juya da sauri ya fice........
*************
"Yana fitowa waje ya tarar da fadawa sun cika wajen gasu magaji da turaki suna ta jiransa suma..
Ya karasa wajen su cikin takon girma kafin suka nufi sashen gimbiya kilishi ga baki dayansu..
A nan suka tarar dasu surayya da khadija kowacce najin da kanta..
Sallama sukayi musu...sannan suka sake zuwa sashen mahaifinsu anan suka iske fulani sukayi musu sallamar suma kafin suka dau hanya..
"Sun isa kasar zazzau da yamma sosai..
Sarki ya saka aka kaisu masaukin su..
Abinci kala kala aka kawo musu suka ci sosai kafin duk suka bi lafiyar gado sbd sauke gajiya..
***************
Yau kwanan jalal daya da tafiya amma juwairiya duk ta rasa me ke mata dadi,
har fada take wa zuciyarta,ke wacece a wajensa da zaki damu dashi haka uhm?
Ta girgiza kai,yarima ka barni na huta!
Ta kalli zobensa data amso dazun wajen me siyar da kifi..ya zanyi da kai yarima?
Zabba'u ce ta shigo dakin ta sanar mata da sakon zainaba na son ganinta a sashen ta..
Tana fitowa daga rumfar bayi suka hade da umayma..
Umayma tace,sai ina haka juwairiya, ko saurayin naki zakije gani ne?
Gaban juwairiya ya fadi,ta ware ido tana dafe kirjinta..
Saurayi kuma?ta fada cike da faduwar gaba..
Umayma tayi dariya ke wasa fa nakeyi miki..
Juwairiya ta sauke ajiyar zuciya,kee kuwa kin cika uwar zolaya..
Umayma ta jinjina kai sukayi sallama kowaccen su ta kama gabanta..
"A can kasar zazzau kuwa,sarki da kansa ne ya bukaci ganinsu da safe,suka shirya suka same sa a palace dinsa..
Sun fara mgnr yarda auren zai kasance sarki ya saka a kirawo masa dansa na fari wato mahaifin yarinyar da ake son hadawa da turaki..
yana shigowa fa'da ya kwashi gaisuwa wajen mahaifinsa sannan aka saka ranar biki..
Turaki dai kallonsu kawai yakeyi dan shikam dan dole ne zai yi wannan auren.
jalal ne ya sanar dashi sakon mai martaba dayaje yaga yarinyar can a gidansu aka hada shi da wani bawa..ba da son ranshi ba ya tafi..
"Jalal tare da magaji kuwa autan sarki khaleed ne ya shiga yawo dasu a cikin masarautar..
Sun kawo sashen amaryar sarki khaleed ya hango ta tana kokarin fita da bayinta a zagaye da ita..
AMMI...!
Ya kira sunanta yana karasawa wajenta..
Jalal da mgaji ma suka bi bayansa..
Ammi ga surukan SAMIRA sunzo harda ma yayan mijin nata sarki JALALLUDEEN..
Wacce aka kira da Ammi jalal ya kura wa ido..
A ina yasan irin wannan fuskar?
Noo haba inaa...juwairiya?zuciyarsa ta raya masa..tabbas akwai kamanni a fuskokinsu..
Ya girgiza kai,amma basu da wani alaka da juna ai,mayb kawai kama ce daga Allah..
AMMI ta kallesu da kulawa suka gaisa,jalal kuwa ya kasa dauke idonsa daga kallonta yana mamakin yarda akayi matar take kama da juwairiya baiwar Rumfar bayi..
*************
"Badai kina nufin akwai wani da wannan me konannar fuskar take gani ba cikin masarautar nan?
Umayma ta gyada kai,na tabbata akwai ranki shi dade, dan danayi mata tambayar dazu wlh idanuwanta sun nuna tsoro tda fargaba..
Surayya ta jinjina kai,toh amma wane irin dolo ne banza da zai so wannan abun?fuska duk a kone..
Kuma tasan da cewa baiwa ce ita bazata taba iya aure ba,ba tare da an yanta ta ba.
Umayma ta gyada kai dole ne kuwa mu gano wanene take gani.
Surayya tace,ki saka mata ido dan akwai zargin da nakeyi...
*************
"Yau kwana biyu da tafiyar su yarima kuma a yau ne ake saka ran dawowar su..
Gimbiya kilishi da kanta ta saka ayi mata kiran du'bu dan ta sanar da ita duk shirye shiryen da za'ayi musu.
"A wajen juwairiya kuwa haka nan ta tsinci zuciyarta a cikin farin ciki sosai tun da ta lbrn..
Sai dai duk farin cikin ta bata kai ga na matan sarki ba..
Dan ba karamin shiri sukeyiwa dawowar mijin nasu ba..
Kowacce da irin kissar da take kullawa...
**************
Sai da yamma kilis su jalal suka shigo cikin masarautar,
sai da suka fara zuwa wajen sarki Abdul-Jabbar sukayi masa bayani akan amincewar sarkin zazzau acikin alliance din hada auren,kuma a take aka saka ranar biki rana daya dana hamza kamar yarda suka bukata..
Murna sosai fulani da mai martaba sukayi,sai dai shi gogan wato turaki,ko digon son yarinyar babu a cikin zuciyarsa...
"A gajiye jalal ya shigo sashen nasa,yana shiga dakinsa ya sauke ajiyar zuciya yana sakin murmushi kafin nan ya furta..
"Yau zan ganta...ya lumshe idonsa..
Kayan jikinsa ya cire sannan ya shige cikin toilet dan watsa ruwa..
"Yana fitowa ne kawai ya tarar da surayya a zaune tana jiransa..
Mikewa tayi da saurinta tazo gabansa tana amsar dan karamin towel din dake hannunsa..
Shidai da kallo kawai yake binta..
Surayya ta shiga goge masa ruwan dake jikinsa tana masa wani irin salo...
"Kirjinsa take goge masa tana yawo da hannunta a kai cikin kissa..
Yarima yayi saurin rike hannunta zayyi magana kenan kawai yaji ta fara kai masa sumbata a gaba daya jikinsa..
"Jikinsa ne yayi lakwas, surayya na ganin haka tayi murmushin samun nasara....
Dan dama tasha alwashin a yau sai yarima ya kwana da ita tun kafin khadija tama saka shi a ido..
Gashi kuma tasha maganin da yakumbo ta aiko mata dashi na daukar ciki da wuri...addu'ar kawai Allah yasa ciki ya shiga...
***************
"Juwairiya ce zaune a cikin RUMFAR BAYI tana jin haushin hanata zuwa sashen jalal da jakadiya tayi..
Gashi kuma Zuciyarta na mutukar son ganin fuskarsa..
"Rabi ce ta zauna a gefenta tana dafa kafadarta..tace..
Wai ni lafiyarki kuwa juwairiya? Kwana biyun nan kin cika zama ke kadai wlh..
Juwairiya zatayi mgn sai ga umayma ta karaso wajensu tana washe baki kamar gonar auduga..
Rabi taja tsaki..ke kuma fa?
Umayma ta dalla mata harara..da akayi me?
Rabi tace,naga se wani washe baki kikeyi sai kace baiwar da aka yan'ta ta..
Umayma ta rangwadar da kai..
Ba dole nayi murna ba tunda dai a wannan lkcn ina kyautata tsanmanin uwar dakina na can akan shinfidar sarki JALALLUDEEN....
"Ba rabi ba har juwairiya dake sauraren su sai da zuciyarta ta buga..
Tayi saurim dafe kirjinta..
Me ke shirin faruwa da ita..."kishi"
Ah ah me yasa zatayi kishin sarki da matarsa...
Ta dafe kirjinta..
Rabi taja dogon tsaki sannan ta mike da gudu tabar wajen dan zuwa sanarwa khadija..
Umayma tahau gu'da...sai can ta hango yarda juwairiya dafe kirji..
Yanayinta ta karanta kawai kafin tace..
Yadai juwairiya lafiya?
Juwairiya ta kakaro murmushi sannan ta mike da sauri ta shige dakinsu...
Kwanciya tayi tana sauke lumfashi me dumi..
Ya kamata kisan abunda ya dace dake juwairiya ta fadawa kanta..
"Take taji jikinta ya dau rawa dan dama tana jin signs din zazzabi ajikinta tun satin daya wuce..
"Hansai ce ta shigo da fitilar kwai a hannunta cikin dakin..
Har ta fara mitar kwanciyar wuri da juwairiya ta tsira..
Sai hango ta tayi tana rawar sanyi..
Ai da sauri tayi kanta..
Juwairiya ke miye ke damunki haka?
juwairiya ta kasa mgn dan harcenta yayi mata nauyi..
Hansai ta fita da gudu tayi kiran du'bu da laure..
Laure na taba jikin juwairiya tace,zazzabi ne mai zafi ya rufe ta..
Du'bu tace subhanallahi..
Hansai ta girgiza kai,ai dama dole ne zazzabi ya kama juwairiya tunda ta maida gaban kogi wajen zamanta duk iskar duniya ya kare akanta..
Du'bu tace bari naje na hado mata magani....
******************
"Da safe jakadiya ta shiga dakinsu juwairiya, ta ganta a kwance jiki kam sai a hankali..
Hansai ta kalla tace,Allah ya bata lfy ni bari na karasa wajen aikina,zan saka wasu bayin suyi mata (covering)aikinta..
Hansai ta jinjina kai dan itama in ba dan dole ba bazata iya fita tabar diyar ta acikin wannan halin ba..
***************
Tunda sassafe jalal ya farka yayi wa surayya kora da hali..
Ya zauna yana ta jiran shigowar juwairiya..
[9/18, 3:22 PM] Aysha Galadima: *RUMFAR BAYI*
(A historical fiction)
Na Afrah bhai
Page 26
Wattpad @afreey101
******************
"Juwairiya na kallonshi har ya karaso zuwa gabanta ya tsaya..
"Kin hada min kayan?
Juwairiya tace,
yanzu na gama ranka shi dade..
Ya lumshe ido,
toh shiga ki hada min ruwa nayi wanka..
Juwairiya tace toh sannan tayi hanyar toilet da saurinta..
"Ta fito ta sanar masa ta gama,bai ce mata komai ba ya shige toilet din..
Yana shigane ta samu damar gyara masa dakin tsab..
Ta kalli kofar toilet din,ta kammala komai na aikinta amma sai ta samu kanta da rashin fita son daga cikin dakin..yau zayyi tafiya ko ba komai tana so suyi sallama..
Matse baki tayi sannan ta fita ta dawo falon ta zauna akasa dan jiransa..
Jalal na fitowa ya tarar babu ita a dakin,bai ji dadi ba kodan dan yaso ace yayi sallama da ita...
Sai daya dauki awa daya yana shiri kafin ya fito cikin shiga ta alfarma..
Caraf ya ganta a zaune ta rakube a waje daya..
Murmushi ya saki ya karasa wajen yana fadin..
"Ya baki tafi ba?
Juwairiya tayi saurin mikewa..
Uhm dama dama uhm yauwa jakadiya ce tace na jira ta a nan..
Ya jinjina kai dan zuciyarsa ta gama basa shi take jira...
Ji tayi kawai ya kamo hannunta ya nufi wajen shakatawar sa da ita..
Ya sake hannun nata sannan ya rufo kofar wajen.
Juwairiya gabanta ne ya shiga faduwa..
Jalal yace..
Yau zanyi tafiya...ya karashe mgnr cike da wani irin yanayi..
juwairiya ita kanta se dataji wani iri.. da murya me cike da sanyi ta samu kanta da fadin..
'Yaushe zaka dawo?
Ya kurawa kwayar idonta kallo..
Kwana biyune..
Juwairiya tayi murmushin yake tace..
Allah ya dawo dakai lfy ranka shi dade..
Jalal ya gyada kai..
Nagode..
Hayaniyar su shamaki ya jiyo daga waje..
Yaja lumfashi ni zan tafi..
Ta jinjina kai ta kasa furta komai..
Ya juya har ya kai bakin kofa ya sake juyowa..
Bai bata wani lkc ba ya janyo ta jikinsa..dan gaba daya kasa controlling zuciyarsa yayi..
Juwairiya taji gaba daya duniyar ta tsaya mata tsak...
Sai da suka shafe seconds talatin kafin yayi karfin halin sakinta ya juya da sauri ya fice........
*************
"Yana fitowa waje ya tarar da fadawa sun cika wajen gasu magaji da turaki suna ta jiransa suma..
Ya karasa wajen su cikin takon girma kafin suka nufi sashen gimbiya kilishi ga baki dayansu..
A nan suka tarar dasu surayya da khadija kowacce najin da kanta..
Sallama sukayi musu...sannan suka sake zuwa sashen mahaifinsu anan suka iske fulani sukayi musu sallamar suma kafin suka dau hanya..
"Sun isa kasar zazzau da yamma sosai..
Sarki ya saka aka kaisu masaukin su..
Abinci kala kala aka kawo musu suka ci sosai kafin duk suka bi lafiyar gado sbd sauke gajiya..
***************
Yau kwanan jalal daya da tafiya amma juwairiya duk ta rasa me ke mata dadi,
har fada take wa zuciyarta,ke wacece a wajensa da zaki damu dashi haka uhm?
Ta girgiza kai,yarima ka barni na huta!
Ta kalli zobensa data amso dazun wajen me siyar da kifi..ya zanyi da kai yarima?
Zabba'u ce ta shigo dakin ta sanar mata da sakon zainaba na son ganinta a sashen ta..
Tana fitowa daga rumfar bayi suka hade da umayma..
Umayma tace,sai ina haka juwairiya, ko saurayin naki zakije gani ne?
Gaban juwairiya ya fadi,ta ware ido tana dafe kirjinta..
Saurayi kuma?ta fada cike da faduwar gaba..
Umayma tayi dariya ke wasa fa nakeyi miki..
Juwairiya ta sauke ajiyar zuciya,kee kuwa kin cika uwar zolaya..
Umayma ta jinjina kai sukayi sallama kowaccen su ta kama gabanta..
"A can kasar zazzau kuwa,sarki da kansa ne ya bukaci ganinsu da safe,suka shirya suka same sa a palace dinsa..
Sun fara mgnr yarda auren zai kasance sarki ya saka a kirawo masa dansa na fari wato mahaifin yarinyar da ake son hadawa da turaki..
yana shigowa fa'da ya kwashi gaisuwa wajen mahaifinsa sannan aka saka ranar biki..
Turaki dai kallonsu kawai yakeyi dan shikam dan dole ne zai yi wannan auren.
jalal ne ya sanar dashi sakon mai martaba dayaje yaga yarinyar can a gidansu aka hada shi da wani bawa..ba da son ranshi ba ya tafi..
"Jalal tare da magaji kuwa autan sarki khaleed ne ya shiga yawo dasu a cikin masarautar..
Sun kawo sashen amaryar sarki khaleed ya hango ta tana kokarin fita da bayinta a zagaye da ita..
AMMI...!
Ya kira sunanta yana karasawa wajenta..
Jalal da mgaji ma suka bi bayansa..
Ammi ga surukan SAMIRA sunzo harda ma yayan mijin nata sarki JALALLUDEEN..
Wacce aka kira da Ammi jalal ya kura wa ido..
A ina yasan irin wannan fuskar?
Noo haba inaa...juwairiya?zuciyarsa ta raya masa..tabbas akwai kamanni a fuskokinsu..
Ya girgiza kai,amma basu da wani alaka da juna ai,mayb kawai kama ce daga Allah..
AMMI ta kallesu da kulawa suka gaisa,jalal kuwa ya kasa dauke idonsa daga kallonta yana mamakin yarda akayi matar take kama da juwairiya baiwar Rumfar bayi..
*************
"Badai kina nufin akwai wani da wannan me konannar fuskar take gani ba cikin masarautar nan?
Umayma ta gyada kai,na tabbata akwai ranki shi dade, dan danayi mata tambayar dazu wlh idanuwanta sun nuna tsoro tda fargaba..
Surayya ta jinjina kai,toh amma wane irin dolo ne banza da zai so wannan abun?fuska duk a kone..
Kuma tasan da cewa baiwa ce ita bazata taba iya aure ba,ba tare da an yanta ta ba.
Umayma ta gyada kai dole ne kuwa mu gano wanene take gani.
Surayya tace,ki saka mata ido dan akwai zargin da nakeyi...
*************
"Yau kwana biyu da tafiyar su yarima kuma a yau ne ake saka ran dawowar su..
Gimbiya kilishi da kanta ta saka ayi mata kiran du'bu dan ta sanar da ita duk shirye shiryen da za'ayi musu.
"A wajen juwairiya kuwa haka nan ta tsinci zuciyarta a cikin farin ciki sosai tun da ta lbrn..
Sai dai duk farin cikin ta bata kai ga na matan sarki ba..
Dan ba karamin shiri sukeyiwa dawowar mijin nasu ba..
Kowacce da irin kissar da take kullawa...
**************
Sai da yamma kilis su jalal suka shigo cikin masarautar,
sai da suka fara zuwa wajen sarki Abdul-Jabbar sukayi masa bayani akan amincewar sarkin zazzau acikin alliance din hada auren,kuma a take aka saka ranar biki rana daya dana hamza kamar yarda suka bukata..
Murna sosai fulani da mai martaba sukayi,sai dai shi gogan wato turaki,ko digon son yarinyar babu a cikin zuciyarsa...
"A gajiye jalal ya shigo sashen nasa,yana shiga dakinsa ya sauke ajiyar zuciya yana sakin murmushi kafin nan ya furta..
"Yau zan ganta...ya lumshe idonsa..
Kayan jikinsa ya cire sannan ya shige cikin toilet dan watsa ruwa..
"Yana fitowa ne kawai ya tarar da surayya a zaune tana jiransa..
Mikewa tayi da saurinta tazo gabansa tana amsar dan karamin towel din dake hannunsa..
Shidai da kallo kawai yake binta..
Surayya ta shiga goge masa ruwan dake jikinsa tana masa wani irin salo...
"Kirjinsa take goge masa tana yawo da hannunta a kai cikin kissa..
Yarima yayi saurin rike hannunta zayyi magana kenan kawai yaji ta fara kai masa sumbata a gaba daya jikinsa..
"Jikinsa ne yayi lakwas, surayya na ganin haka tayi murmushin samun nasara....
Dan dama tasha alwashin a yau sai yarima ya kwana da ita tun kafin khadija tama saka shi a ido..
Gashi kuma tasha maganin da yakumbo ta aiko mata dashi na daukar ciki da wuri...addu'ar kawai Allah yasa ciki ya shiga...
***************
"Juwairiya ce zaune a cikin RUMFAR BAYI tana jin haushin hanata zuwa sashen jalal da jakadiya tayi..
Gashi kuma Zuciyarta na mutukar son ganin fuskarsa..
"Rabi ce ta zauna a gefenta tana dafa kafadarta..tace..
Wai ni lafiyarki kuwa juwairiya? Kwana biyun nan kin cika zama ke kadai wlh..
Juwairiya zatayi mgn sai ga umayma ta karaso wajensu tana washe baki kamar gonar auduga..
Rabi taja tsaki..ke kuma fa?
Umayma ta dalla mata harara..da akayi me?
Rabi tace,naga se wani washe baki kikeyi sai kace baiwar da aka yan'ta ta..
Umayma ta rangwadar da kai..
Ba dole nayi murna ba tunda dai a wannan lkcn ina kyautata tsanmanin uwar dakina na can akan shinfidar sarki JALALLUDEEN....
"Ba rabi ba har juwairiya dake sauraren su sai da zuciyarta ta buga..
Tayi saurim dafe kirjinta..
Me ke shirin faruwa da ita..."kishi"
Ah ah me yasa zatayi kishin sarki da matarsa...
Ta dafe kirjinta..
Rabi taja dogon tsaki sannan ta mike da gudu tabar wajen dan zuwa sanarwa khadija..
Umayma tahau gu'da...sai can ta hango yarda juwairiya dafe kirji..
Yanayinta ta karanta kawai kafin tace..
Yadai juwairiya lafiya?
Juwairiya ta kakaro murmushi sannan ta mike da sauri ta shige dakinsu...
Kwanciya tayi tana sauke lumfashi me dumi..
Ya kamata kisan abunda ya dace dake juwairiya ta fadawa kanta..
"Take taji jikinta ya dau rawa dan dama tana jin signs din zazzabi ajikinta tun satin daya wuce..
"Hansai ce ta shigo da fitilar kwai a hannunta cikin dakin..
Har ta fara mitar kwanciyar wuri da juwairiya ta tsira..
Sai hango ta tayi tana rawar sanyi..
Ai da sauri tayi kanta..
Juwairiya ke miye ke damunki haka?
juwairiya ta kasa mgn dan harcenta yayi mata nauyi..
Hansai ta fita da gudu tayi kiran du'bu da laure..
Laure na taba jikin juwairiya tace,zazzabi ne mai zafi ya rufe ta..
Du'bu tace subhanallahi..
Hansai ta girgiza kai,ai dama dole ne zazzabi ya kama juwairiya tunda ta maida gaban kogi wajen zamanta duk iskar duniya ya kare akanta..
Du'bu tace bari naje na hado mata magani....
******************
"Da safe jakadiya ta shiga dakinsu juwairiya, ta ganta a kwance jiki kam sai a hankali..
Hansai ta kalla tace,Allah ya bata lfy ni bari na karasa wajen aikina,zan saka wasu bayin suyi mata (covering)aikinta..
Hansai ta jinjina kai dan itama in ba dan dole ba bazata iya fita tabar diyar ta acikin wannan halin ba..
***************
Tunda sassafe jalal ya farka yayi wa surayya kora da hali..
Ya zauna yana ta jiran shigowar juwairiya..