← Book details Life Partner Part 1 Complete Hausa Novel.txt Local reading mode
READING PART 16 OF 59

Sashe 16

Life Partner Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read

_Two week ltr_
Rafi'ah ce kwance a gefen Abba tana fada mishi abubuwan da zatai na saukarta, Abba ya dan kalleta yana shafa kanta ya ce "Bafa aure bane Mamana" ta dan turo baki cikin shagwa6a ta ce "But Abba ya kamata amin duk abinda nace gaskiya, nice fa first born dinka" yana murmushi ya ce "Kuma Mamana hakama, to kimin list din duk abinda kikeso" ta washe baki ta ce "Insha Allah, i will do so when i have time" Abba ya ce "Good, are u not celebrating world heart day today?" Ta mike zaune tana kallan Abbannata ta ce "I am Abba" ya ce "What have u done for the day?" Ta saki murmushi tana kallansa ta ce "Nayi addu'a Allah ya bani lafiya, dama duk wanda yake suffering da wannan ciwan, and i thank God for giving me such a loving parents like you, i love u Abbana" daga haka ta rungumeshi, Abba ya shafa bayanta gentle ya ce "Allah ya miki albarka ya kuma baki lafiya, but i think u have to go and celebrate there" ta zame jikinta a nashi ta ce "Zanje Abba, ina jiran Ummi ta dawo a office, because i can't leave you alone" Abba yaja hancinta yana dariya ya ce "Thank u mother, zo ki gayamin me ake a taron naku idan kunje" ta gyara zamanta ta ce "Firstly we introduce ourselves but not all, after then ana bada shawarwari akan yadda mutum zai kula da kansa sabida kar yana samun attack sosai, da kuma what medicine to take idan ka samu attack, after then u rushed for emergency, but the main abinda ake ta fada is heart rest, anaso a kullum mutum ya dinga nutsuwa ya daina sawa kansa damuwa da yawa" Abba ya bata side hug ya ce "Excellent, i hope kina bin duk abinda aka fada?" Ta daga masa kai ta ce "Sosai ma Abba, i really enjoyed this day in life that's 29 of September" Abba ya bata light kiss a forehead dinta ya ce "Proud to have u daughter, gobe insha Allah zan kaiku gidan Umma tinda yanzu kinji sauki sosai" Rafi'ah ta sauke ajiyar zuciya ta ce "Do u mean gidansu Anty Amina?" Ya ce "Of course, Ita kadai ce uwar data ragemana a yanzu" Rafi'ah ta kwantar da kanta akan shoulder dinsa ta ce "Allah ya jikan Baban Kaduna" Abba ya ce "Ameen" ta dago kuma tana kallan Abba ta ce "Wai Abba da Babanka da Umman Anty Amina waye babba?" Ya ce "Babana ne babba, sai Baba Mu'azu sai kuma Umma" Rafi'ah ta ce "Ohk, i was thinking itace Babba fa" Abba ya girgiza kai ya ce "No, just because she a female".
Karfe 3 da rabi Ummi ta shigo gidan, a tare suka amsa sallamarta, Rafi'ah ta mike tayi hugging dinta tana mata sannu da zuwa, Abba ya kalleta ya ce "U are welcome, but u look so tired Ummu Rafi'ah" Ummi ta danyi murmushi ta ce "Na gaji kam, yau nayi lectures biyu two~two hours, after then mukai meeting sai to 3 muka fito" Abba ya mata sannu sannan ya mike yana kallan Rafi'ah ya ce "Call Abdul for me, it's time for prayer" Rafi'ah ta nufi dakinsa tana fadin "Tin da muka dawo a school yau Abdul yake bacci, wallahi Ummi babanki ya zama kasa" Ummi ta dalla mata harara ta ce "Be careful with me" dariya sosai take ta shige dakin Abdul ta hau kan gadon ta dinga mintsilinsa a baya tana ya tashi, da kyar ya mike ya shiga toilet sannan ta fito tana dariya ta ce "Ummi yau 29 of September, zanje taron heart day" Ummi ta ce "But not alone, Mustapha ya kaiki ya jiraki, sannan karki yarda magrib yayi maki a titi" ta ce "To insha Allah, in kawo maki abinci?" Ummi ta girgiza kai ta ce "I want to bath first" Rafi'ah ta nufi upstairs zuwa dakinta ta shiga wanka, ba dadewa ta fito shafa body lotion sannan tasa peach din doguwar riga, kanta ta fara combing tana ta aush tana 6ata rai kamar an sata dole, bayan ta gama ta saka scarf sannan ta yafa veil din rigar tayi simple make up, woooow!!! fans just say masha Allah here, the beauty can't be describe in one sentence, saina gama page dinma ban gama gaya muku irin kyau din datai ba loooool, turare masu kamshin gaske ta fesa sannan ta dauki flat shoe ta saka ta dauka small side bag ta jefa phone dinta da tissue a ciki sannan ta fita. Tana saukowa downstairs ta samu Ummi zaune nan inda ta barta, ta danyi murmushi ganin kallan da mahaifiyarta ke mata ta ce "Nasan nayi kyau ko Ummi?" Ummi ta maida hankalinta ga TV ta ce "Karki kai magrib Rafi'ah, fatan kuma kinyi sallan la'asar?" Ta ce "Insha Allah Ummi bazan kai magrib ba" Ummi ta ce "Sallan fa?" Ta ce "I'm on period" daga haka ta nufi kofa ta ce "Saina dawo" Ummi ta ce "Allah ya tsare" da Ameen ta amsa sannan ta fita ta kullo kofar, a parking lot ta samu Mustapha yana ta goge mota, yana kallanta ya washe baki ya bude mata back seat ya ce "Kaga turawan asali, Gaskiya Hajiya karama saurayinki yaji dadi, koda wannan kyan aka barshi yaci nasara, bare aje ga hankali, nutsuwa, kyauta, mutunci ga kuma kin fito gidan manya" Rafi'ah couldn't hold her laugh, ta dinga dariya kafin ta ce "Nikam naji dadina da wannan zancen" Mustapha ya ce "Allah kuwa gaskiya nake fada miki hajiya karama, sai wani walkiya kike kina haske ido" Ita dai dariya kawai take yaja motar suka fita a gidan.
15 minutes ya kaisu inda zasuje, bayan yayi parking Rafi'ah ta fito tana kallansa ta ce "Ka jirani anan, ba dadewa zanyi ba" ya duka cikin girmamawa ya ce "An gama kyakkyawa" daga haka ta juya tana dariya ta shiga cikin hall din, everywhere is silent sai muryar mutumin dake kan stage yana magana da loud speaker, Rafi'ah ta samu seat ta zauna ta maida hankalinta gun mai maganar, shawarwari sosai ya bayar ga masu fama da ciwan zuciya, kusan minti 10 yana bayani sannan yayi musu fatan alkhairi ya bayar da loud speaker, mutumin daya kar6i loud speaker ya danyi karin bayani sannan ya kira Doctor Yusuf akan shima ya fito ya bada tasa gudummawar a matsayinsa na likita kuma mai fama da wannan cuta, cikin light steps Yusuf ya karasa kan stage din ya kar6i loud speaker, shadda ce fara ajikinsa tsaha aiki sai hula baka da half shoes dinsa baki, daga hannunsa kuma kana iya hango wristwatch dinsa black colour sai zoben azurfa dake kyalli a yatsarsa ta tsakiya, cikin sweet voice dinsa yayi wa kowa sallama sannan ya fara bayani da english kamar haka "If you are opting to celebrate this day, it is important to try and be more attentive to your own heart health. There are a number of different ways that you can do this. This includes following a healthy diet, quitting alcohol, stopping smoking, and getting involved in physical exercises..." The hall is so quite harya gama bayaninsa in his good and meaningful English, bayan ya gama ya mikawa na gefensa loud speaker sannan ya sakko akan stage din, daga haka the audience break into rapturous applause. Saurin mayar da kanta gefe tayi ganin ya nufo inda take, bayan ya karaso yaja kujera ya zauna yana kallanta ya ce "Hy" ba tare data juyo ba ta ce "Why not salamu alaikum?" Yusuf ya shafa beard dinsa yana kallanta ya ce "I'm sorry, Assalamu alaikum" ta danyi murmushi ta ce "Wa'alaikumus salaam" ya ce "How are u?" Ta ce "I'm fine and u?" Ya ce "Alhamdulilah also" tayi shiru tana kallan mutum dake bayani akan stage, Yusuf ya ja chair dinsa kusan nata ya ce "Is that all for d greeting?" ta ce "What again? Naga ai mun gaisa" ya girgiza kai ya ce "Actually no, wannan karan shine na hudu da muka hadu, i think we have to introduce ourselves to each other" Rafi'ah ta danyi murmushi ta ce "Ok, but u start" ya ce "Noo, u start" ta dan turo baki sannan ta ce "Ai kasan sunana" ya ce "Amma kuma na manta" ta dan harareshi ta ce "Ohk Sunana Yusuf Muhammad, I'm the first born of the family, kanina guda daya sunansa Abduljalal, my father works with CBN in Abuja, mother is a lecturer, i'm in SS2 now, ina hadda 5 a islamiyya, Abbana dan Kaduna, shi kadai iyayensa suka haifa, Ummi na kuma 'yar nan Kano ce, su biyu a familyn su ita da yayarta Anty Halima, she is living here in kano also, amma bata ta6a haihuwa ba, Matan Abbana guda biyu ne, so i think this should be my brief history" Yusuf ya saki murmushi yana kallanta ya ce "Nice to meet u Yusuf, hope u are ready to hear mine?" Ta daga masa kai tana murmushi, ya ce "As u know sunana Fatima Muhammad, but they do called me Rafi'ah, ni kadai iyayena suka haifa, sun rasu ta dalilin accident when i was 18 then, lokacin dana gama secondary school dina, both Father and mother are from kano, i did my first degree in Dubai where i studied Medicine, and then goes for PHD where i specialize in Pediatrics, i'm now staying with my father's sister and her daughter, Ammina ma su biyu ne agidansu, akwai sister dinta dake unguwar rimi" Rafi'ah ta sauke ajiyar zuciya jin iyayensa duk sun rasu, a hankali ta ce "Allah ya musu rahama" ya ce "Amee, Can u pls help me with your digit?"...

_More comments is needed pls, let me see how much u appreciate the book SHARIK HAYATI_

*Join my Facebook grp @Real~Teemarh fans*

*Follow me on wattpad @Real~Teemarh192*

*SHARIK HAYATI*

_08103810398_
[6/9, 11:00 AM] Teemarh: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation
*_...شريك حياتي..._*
_{MY LIFE PARTNER}_

*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️
_We are here to Educate, Motivate and Entertain our Readers_
〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️

*BY FATIMA* _{Real~Teemarh}_

_17~18_
Chapter 16 · 0% Book details