← Book details Idan An Ciza Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 93

Sashe 28

Idan An Ciza Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

A kofar gida suka samu keɓewa da Baba Ɗanjuma ya yi masa mganar Walida da Mariya ya ce zaman su ne ya ishe sa ba sun gama karatu ba?
Mansoor ya ce" Eh sun gama matakin sakandiri ba, Ina so su cigaba har matakin jami'a in sha Allahu."
Baba ya yi shuru kafin ya ce"A'a ni na fi son kowacce ta kama É—akin ta kamar sauran Æ´ayana."
Mansoor ya ce"To Baba, sun samu maneman ne?
Baba ÆŠanjuma ya gyara zama kafin ya ce" To ban sani ba, amman abin da ya sa na kira ka kenan, ka kira su dukkansu ka zauna da su ka ji in akwai waÉ—anda ke nenan su, in ka ji akwai sai a bincika in an aminta da nagartansu shikenan."
Mansoor ya yi shuru kafin ya ce"In kuma babu fa? Baba ÆŠanjuma ya ce shikenan sai ka ba su daman fara yin zence har Allah yasa a dace.
Bai yi gaddama ba ya ce zai yi mgana da su in ya shiga cikin gida anan waje ya bar Baban wajen abokinsa Mallam Hashimu ya na ko shiga da Mariya ya fara cin karo tana wankin kayan da za ta saka gobe a dara nan shi bai ma ganeta ba sai da ya ji tana gaishe shi sannan ya tsaya ya na kallonta shi ya daÉ—e ma bai ganta ba.

"Ke ina kike zuwa, ba na ganin ki a cikin gidan nan?

Haka ya faÉ—a lokaci É—aya yana kallonta da sauri ta ce" E. mm ina gidan Yaya Zuwaira ne."
Kai tsaye ya ce"Me ya sa kika je can?
Sai ta kasa mgana kanta na kasa dai dai lokacin da magajiya, ta É—ago labule ta Fito ta na kallon su, shi kuma ko kallo bata ishe sa ba kawai sai ya juya ya na faÉ—in" Barka da dare, ke Mariya ki same ni a É—akin Inna zan yi mgana da ku."
Yana gama faÉ—in haka ya yi wucewarsa Magajiya ta bi shi da harara. Bai ma san tana na yi ba tsaki ta yi lokaci É—aya tana Kallon Mariya" Ko zai ce ki daina zuwa gidan Zuwairan ne tunda shi ne uban ÆŠanjuma?
Mariya ta kalleta kafin ta ce"Kai  Magajiya."
hararanta ta yi kafin tac e" Dilla ta fi can sakara, kuma kije ki dawo ki gayamin abin da ya ce."
Mariya ba ta kara mgana ba ta dai shanya kayanta daman ɗauraya take yi, ta wuce Bangaren Inna Meri ta samu ɗakin Maeesha a sakaye tunda Yaya Saddiqun na gari tun shekaranjiya ya shigo garin sai firita take yi tana shwagaɓa ita mai ciki, a falon Innar Daga Walida sai shi Junior ma ya yi barci Inna Meri kuma barci take ji bayan sun gaisa ta ce za ta shiga ta kwanta ta huta amman ba ta fara barcin ba ta ji yana tambayansu ko suna da ma su son su?

Mariya da Walida suka kalli juna cikin mamaki, ita dai Mariya tana da samari ita kuma Walida ba ta da wani takammame, Tunda ba tsayawa take yi da samarin ba, Samnan ba ta da waya Inna ko yar ganin dama ce, in ta ga dama ko wayar ma walida sai ta yini ba ta gani ba Innar ta yi boyon kayanta mariya ko tana da waya wani Saurayin ta dake sonta ya siya mata.
Ganin duk sun yi shuru ya sa ya yi gyaran murya yana faÉ—in" Baba na son ya aurar da ku, ni kuma ina son ku yi karatu wacce take ganin ta na da wanda ke sonta sai ta yi mgana."
Walida ta yi shuru, kafin ta ce"Ni dai ba kowa, zan fi son na cigaba da karatuna Yar jarida nake son zama kamar Anty Mimi"
Bai ce mata komai ba tunda hankalinsa na kan wayar hannunsa ne.

"Ke fa?

Ya faɗa ya na cigaba da duba wayarsa, murya can ƙasa mariya ta ce"Ni.. ni akwai wani."
"Ina yake?
Ya haka ya katseta da sauri ta ce" A tudum wada. Yaya Auwalu ma ya san ashi."
Kai ya girgiza kafin ya ce"Ok zan yi mgana da Auwalu ɗin, ke kuma tunda ba ki ci Jamb ba  ba za ki zauna hakanan ba zan nema miki ko yar diploma ki je ki yi a kan na'ura mai ƙwalƙwala, kafin wata shekara sai ki sake rubuta Jamb ɗin mu ga Abin d Allah zai yi."
Gabaɗayansu su ka yi masa godiya,  nan ya bar su ya fita bayan ya ce Walida ta gaya ma Inna ya tafi, ya so ya gaya mata gobe zai je kano amman kuma bai samu fuska ba, Ita ko Innar ta na jinsa mirmishi kawai ta yi, ko da ace shi ɗin yana da fitina amman kuma yana da kyakyawan hallayan da fole a ɗaga masa kafa. Tana jin su walida na kuskus a falo, Ko da ce ma Mariyan ba ta da saurayin Magajiya ba za ta bari ta cigaba da karatu ba, aure za ta ce ƴarta za ta yi, Walida kuma ta san ba ta da wani saurayi sai tarkace ita ba za ta saka baki ba tana da uba da Sauran yayyenta abin da su ka yanke a kanta ba za ta ja ba.

Yana fita su ka kusa cin karo da Saddiqu da ya fito daga cikin ɗakin sa daga shi sai gajeran ƙaramin wando, Kallo kallo suka yi ma juna shi da Aji, kwarjini ya yi masa yasa ya ba shi hannu su ka yi musabaha duk da ya sha alwashin ba zai ƙara gaishe shi ba, sannan ga gulmar da Aishar ta kai masa amman ga shi ga Mansoor ɗin ya kasa masa wata mgana.
Shi ko kallon kasa da sama ya yi masa kafin ya ce" ya kamata dai kasan a yanayin da za ka riƙa fitowa, nan gidan akwai iyayenmu akwai ƙannen mu bai kamata ka riƙa fitowa haka ba."

Yana gama faÉ—in, ya saki hannun shi ya yi wucewarsa ya bar Saddiqu na bin shi da harara sai da ya tabbatar da ya bar shashensa sannan ya saki tsaki yana faÉ—in" Æ´an Æ´an, sarkin iyayi ai sai ka hanani ni da gidan ubana."
Daga baya kenan.

********

*03rd Febuary 2023*

Ba a motarsa ya shirya tafiyan ba. Sai ya shirya tafiyar tasa a motar haya. Takwas na safe yana tasha kafin tara motar kano ta É—aga da Aji aciki kuma har a lokacin yana kiran wayar mimi amman amsar É—aya ne tana kashe ne, Daman tun kwanaki ya saka Mu'azzam ya tura masa lambar Dr. sulaiman É—in bai kuma kira shi ba sai da ya sauka tashawajen sha biyun saura na rana sannan ya kira shi.

Wajen kira biyu ya yi masa ana uku ne ya ji an É—aga kiran da sallama, shima sai ya amsa masa suka gaisa.

"Ba ka gane wa ke mgana ba ko?

Dagacan bangaren Dr. sulaiman dake haraban asibitin Aminu kano ya fito daga duba Patient É—in da ya yi ma tiyata jiya ya samu Kiran Aji.

"E wlh ban gane ba. Lambar ba bu suna.".

"Sunana Mansoor Aji, mijin ƙanwar ka Fatima Mimi."

Mirmishi ya suɓuce ma Dr. Sulaiman yana gyara zaman gilashin da ke idonsa ya ce" Allah sarki, kasan da ya ke ba mu taɓa waya ba shi ya sa ban ɗauki muryan ba."
Aji ya jinjina kai kafin ya ce" Gani na sauka a tashar Kano. Adireshin gidanka nake so, na zo wajen matata ne."
Ciki mamakin da har ya bayyana saman fuskar Dr Sulaiman ya ce"Ikon Allah, ok to yanzu na shigo asibiti ne na duba patient ka gaya min tashar da ka sauka sai na ƙariso  na ɗauke ka ko?
Sai Aji ya waiwaya ya ga sunan Tashar ya faÉ—a masa sai Dr ya ce ga shi nan tafe in sha Allahu.
Sannan suka yi sallama ya ƙarisa wajen motarsa ya buɗe ya shiga. Sai da ya hana Mimi tafiya amman Daddy ya ce a kyaleta tunda dai har ya ji labarin ya bita wajen Hajiiya kuma ya taka har Abuja saboda ita amman kuma ba ta bari sun haɗu ba, Ya yi mata faɗan ta koma Gombe amman Mimi taki jin mganarsa yanzu kuma bai san da wani yare zai faɗa masa Mimi ta bi Madiha da mijinta zuwa Umra ba.

Yana wannan tunanin cikin lokaci ya isa ta shar Allah ya taimake shi bai haÉ—u da mugun Goslow É—in kano ba, daga bakin tashar ya tsaya saboda in ya shiga wajen fitowa ne matsalan tunda tashar Kano Line ne sai ya kira layin da Aji ya kira shi da farko ya ce ya É—an Fito daga tashar ya na nan a bakin tashar a wata mota mai ruwan toka.
Ba su sha wahalan gane juna ba, Dr Sulaiman ya fara gane Aji tunda ya san shi, shi kuma Aji fuskar Mimi ya gani a fuskar shi sannan ya É—aga masa hannu kuma ga shi a jikin mota mai ruwan toka.
Aji ya na sanye da shadda mai ruwan toka É—inki zamani ya dora bakar dara a kansa takalmin kafarsa sahu waje ne. Sai wayarsa kawai dake hannunsa.
Bayan ya ƙariso suka yi musabaha sannan Dr Sulaiman ya buɗe mai gaban mota ya shiga suka ɗauki hanyar cikin gari. Gidan Dr na anguwan sharaɗa ne.
Chapter 28 · 0% Book details