Sashe 40
Gidan Misbahu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ranar hutun k'arshen mako wato weekend Hajj jamil da Matar shi Hajiya zaliha tare da d'an su suka je gidan daddy. Fad'a sosai tare da nasihohi mai shiga jiki Hajiyar daddy ta dinga yi ma ta. Hajiya zaliha hadda hawayen ta. Ta yi wa Hajiya alqawarin insha Allahu za ta gyara. Yadda Haajar ke tafiyar da rayuwar ta yayi matuqar burge Hajiya zaliha ,wannan ya sa Hajiya zaliha ta so su had'a k'awance duk da cewar za ta girmi Haajar d'in. Kuma Haajar 'yar yayan mijin ta ne. Sai dai da yake babu wata shaquwa mai qarfi tsakanin su. Amma ta tabbata girman huhun goro ba shi bane. Saboda haka suka sha hirar yaushe rabo da Haajar. Har dare su Hajiya zaliha su na gidan daddy kafin su ka tafi. Tun daga ranar Hajiya zaliha ta samu wurin zuwa dan ta maida Haajar tamkar qawarta. Bayan sati d'aya sati biyu haka takan zo su sha hira sosai da Haajar. Shakka babu Hajj jamil ya ga amfanin zaman Matar shi da Haajar. Dan ba iya rayuwar su komai ya canza ba ,hatta a shimfid'a ya ji bambamcin na daban.
Bayan wata tara Haajar ta haifo santala santalan 'ya'yan ta mace da namiji. Namijin kama yake da daddy sak macen kuma kama ta ke da marigayiya Haseena. Murna a wurin wannan ahali abun Sai Wanda ya gani. Tun randa aka haihun Hajiya zaliha kullum ta na gidan ta na yiwa Haajar d'awainiya. Saura kwana biyu biki ,dangi na kusa da na nisa suka halatto ,da ma ga shi an dad'e ba'a yi sha'ani a gidan daddy ba. Musamman dangin Haajar d'in da wasu daga ciki sai dai suka ji labarin d'aurin auren. Yayyin ta da k'annen ta rankatakaf babu Wanda aka baro ,tare da Matar mahaifin su da ta zamo tamkar uwa a gare su. Kai! Haajar ranar ina ruwa ta tsoma kan ta Dan murna. Daga b'angaren daddy ma anga gayyar mutanen kano da kewaye. Hajiya zaliha ma ba'a barta a baya ba wurin yo tata gayyata. Ranar suna namijin yaci sunan Hajj jamil ana masa laqani da Hassan d'in shi, macen kuma taci sunan marigayiya Haseena ana kiran ta da hussaina. Taro ya yi taro anci ansha ,mai jego da 'ya'yan ta sun yi shiga daban-daban gwanin ban sha'awa. Duk Wanda ya zo taron suna da abun azziki yake tafiya. Banda kyaututtuka da zunzurutun kud'i da jariran suka samu daga wurin abokan su daddy. Hajj jamil kuwa kamar shi aka yi wa haihuwa ,Dan kusan komai shi ya yi. Barr Kabir ma sai da ya yiwa yaran kyautar naira dubu d'ari tare da akwatin kayan jarirai biyu. Hajiya ma ba'a barta a baya ba ,Dan kyauta ta yi Haajar d'in na musamman. Hatta Dr. Imam mahaifin Haajar sai da ya yo aike. Kai lissafa tarin alkhairan da Haajar da yaran ta suka sa mu b'ata lokaci na. Dan idan za mu kwana mu wuni ba zamu gama lissafe adadin abubuwan azzikin ba. Bayan su na mutane na ta watsewa. Ranar da 'yan uwan Haajar za su tafi ,kyauta daddy ya musu ba ni da kyauta ba. Sun ji dad'i matuqa sun kuma yaba da irin mijin ta Haajar ta samu. Bayan kowa ya gama tafiya. Haajar Sai da ta nemi inda za ta ajiye kayan yaran ,dan tsabar sun mata yawa. Uban gayyar kuwa wato daddy ,kyutar gidan gonar shi sukutum ya yiwa yaran shi. Haajar ba ta so ba Dan gani take abun ya yi yawa. Ga wa'yancan ga kuma wannan. Hadda k'wallan ta Dan farin ciki. Account Daddy ya bud'ewa yaran ya zuba musu duk kud'ad'en da suka samu. Haajar ta tambaye sa akan ya za'ayi da su yace ta yi amfani da su idan ta na da buqata Dan shi dai idan bai qara musu ba bazai karb'a sisi ba. Shawartar shi Haajar ta yi akan to ko ta bud'e gidauniya na taimakawa gajiyayyu da nakasassu. Daddy yace wannan shawara ce mai kyau. Hakan kuwa aka yi. Kafin kace me sunan Haajar da tallafin ta ya zaga sakkwato da kewaye.
Bayan sun yi arba'in. Suka shirya Dan zuwa gano Hajiya Gwaggo da ta dad'e a kwance ba tada lafiya. Gaba d'ayan su suka tafi. Yadda su ka samu Hajiya gwaggo kam rai hannun Allah. Washe garin zuwan su wata tsohuwa mai suna TANI ta zo gidan. Hannun ta d'aya a shanye. Aka tambaye ta wa take nema? Tace Hajiya Gwaggo. Nan aka kaita taga yadda jikin Hajiya gwaggon ya yi. Matar nan ta fashe da kuka. Nan ta soma basu labarin abunda ya wuce shekaru aru-aru. Ga Hajiya sakina a zaune kishiyar Hajiya Gwaggo ,ga hajiyar daddy da daddyn kan shi ,ga wasu daga cikin 'ya'yan Hajiya sakina. Haajar ma na daga gefe a zaune. Matar mai suna TANI tace "Tun suna 'yan mata sun gina rayuwar su akan Neman duniya da son zuciya ita da Hajiya Gwaggo. Ba su da aiki sai shiga malamai. A haka har suka yi aure. Ko da mijin Hajiya Gwaggo zai auro Hajiya sakina babu inda ba su shiga ba Dan su hana wannan auren ,amma duk inda suka shiga sai a ce musu wannan aure ba fa shi. A haka aka zo aka yi auren har Hajiya sakina ta fara haihuwa. Duk lokacin da Hajiya sakina ta samu ciki sai sun je an yi musu duba. Har lokacin da ta samu cikin mahaifin daddy aka fad'a musu cewa namiji za'a haifa, kuma mai arziki. Nan fa muka dinga k'ulla tuggu akan yadda za mu zubar da cikin amma Allah ya yi sai abunda ke cikin nan ya ta ka doran k'asa. To dama a lokacin Hajiya Gwaggon itama tana da ciki. Allah kuma yasa lokacin haihuwar su yazo rana d'aya. Mu ka yi amfani da wannan damar muka canza 'ya'yan. A inda muka d'auke d'an Hajiya sakina wato mahaifin daddy mu ka sauya shi da 'yar Hajiya Gwaggon Dan ace ita ta haifa. Ashe da ma 'yar da muka sauya wa muka ba Hajiya sakina ba mai zama bace, Dan tun kafin a yi suna Allah ya yi Mata rasuwa. Hajiya Gwaggo kuma ta ci gaba da rik'e d'an Hajiya sakina a matsayin na ta." Tsohuwar nan ta sake fashewa da kuka. Tace "Na ga jarabawar rayuwa da mugayen qaddarori da bazan so ace na mutu a ciki ba. Duk Wanda muka zalunta na yi ta k'ok'arin ganin na nema inda yake na ba shi hakuri. Nan ma kusan sama da shekaru goma ina Neman gidan amma Allah bai sa na gane gidan ba Sai yau." Tsohuwar na kuka tana Neman gafarar su. Hajiya sakina tace ta yafe mata ta ta shi ta tafi. Hajiya Gwaggo ko hawaye ne ya shiga wanke mata fuska ,tana so ta nemi yafiyar su amma ba dama ciwo ya ci qarfin ta. Hajiya sakina na hawaye tace wallahi ta yafe mata har ga Allah ta kuma gargad'e su akan ba ta yadda a fitar da zancen ba. Tun da har Wanda ake yi Dan shi ya mutu. Ranar kowa da abun ya kwana a rai. Abu sai kace wasan kwaikwayo. Washe gari kiran sallar farko na asubahi Hajiya Gwaggo ta amsa kiran ubangiji. Hajiya sakina ta yi kuka kamar ba gobe ,Dan ita har ga ba ta tab'a rik'e Hajiya Gwaggo a ran ta ba. Tana kuma matuqar qaunar ta har cikin zuciyar ta ,musamman jiya da ta ji ance ta riqe d'an da ta haifa. Abunda ta yadda da shi shine ,babu Wanda zai so naka har ya rik'e face masoyin ka...
MUJE ZUWA💃
TAKU HAR KULLUM
SIDIYA...✍️
[8/26, 7:29 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠
*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_*
(On ward together)
*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*
_BABI NA ARBA'IN DA BAKWAI_
*____________________________*
Misalin k'arfe Tara da safe aka yi jana'izar Hajiya Gwaggo aka kai ta makwancin ta. Kusan duk Wanda ya bud'e baki Allah wadai yake da halayyar Hajiya Gwaggo. Banda Hajiya sakina da ke ta faman kuka tana fad'in ta yafewa Hajiya Gwaggo duk abunda ta yi mata duniya da lahira. A gefe d'aya kuma ahalin gidan sai k'ara jimanta lamarin suke yi wai Hajiya Gwaggo ba ita ce ta haifi Baba Alhaji ba mahaifin Daddy,,, kai wannan Abu da d'aure kai yake. Ran da aka yi addu'an uku jama'a suka fara watsewa, yayinda wasu daga cikin ahalin wannan gida ke jin dad'in mutuwar Hajiya Gwaggo, a cewar wasu daga ciki ,ta gallaza musu ta addaba musu, su da gidan mahaifin su amma ba su da saqat. 'Ya'yan Hajiya sakina sai murna suke yi na kasancewar daddy d'an d'an uwan su ne. Suka zauna suka tattauna akan yadda za su k'arfafa zumuncin su, a ka saida magana cewa za'a dinga had'uwa anan gida duk bayan wata uku lokacin 'ya'yan su dake makaranta sun samu hutu, ya ka ma zama hud'u kenan a shekara. Wannan batu ya yi wa kowa dad'i. Daga su Haajar ba su baro ba sai da aka sanya ranar auren Suxee da Barr Kabir nan da wata uku me kamawa. Aka sanya na wasu 'yan matan wa'yan da 'ya'yar daddy wata biyu bayan bikin Suxee. Ba'a tashi daga taron ba saida Hajiya sakina ta yi musu wasu 'yan nasihohi masu ratsa jiki. Kusan dikkanin su da farin ciki suka watse cike da d'aukin junan su. Daga haka kowa ya watse, ciki yadda su daddy. Rayuwa ta dawo musu sabuwa.
Bayan wata tara Haajar ta haifo santala santalan 'ya'yan ta mace da namiji. Namijin kama yake da daddy sak macen kuma kama ta ke da marigayiya Haseena. Murna a wurin wannan ahali abun Sai Wanda ya gani. Tun randa aka haihun Hajiya zaliha kullum ta na gidan ta na yiwa Haajar d'awainiya. Saura kwana biyu biki ,dangi na kusa da na nisa suka halatto ,da ma ga shi an dad'e ba'a yi sha'ani a gidan daddy ba. Musamman dangin Haajar d'in da wasu daga ciki sai dai suka ji labarin d'aurin auren. Yayyin ta da k'annen ta rankatakaf babu Wanda aka baro ,tare da Matar mahaifin su da ta zamo tamkar uwa a gare su. Kai! Haajar ranar ina ruwa ta tsoma kan ta Dan murna. Daga b'angaren daddy ma anga gayyar mutanen kano da kewaye. Hajiya zaliha ma ba'a barta a baya ba wurin yo tata gayyata. Ranar suna namijin yaci sunan Hajj jamil ana masa laqani da Hassan d'in shi, macen kuma taci sunan marigayiya Haseena ana kiran ta da hussaina. Taro ya yi taro anci ansha ,mai jego da 'ya'yan ta sun yi shiga daban-daban gwanin ban sha'awa. Duk Wanda ya zo taron suna da abun azziki yake tafiya. Banda kyaututtuka da zunzurutun kud'i da jariran suka samu daga wurin abokan su daddy. Hajj jamil kuwa kamar shi aka yi wa haihuwa ,Dan kusan komai shi ya yi. Barr Kabir ma sai da ya yiwa yaran kyautar naira dubu d'ari tare da akwatin kayan jarirai biyu. Hajiya ma ba'a barta a baya ba ,Dan kyauta ta yi Haajar d'in na musamman. Hatta Dr. Imam mahaifin Haajar sai da ya yo aike. Kai lissafa tarin alkhairan da Haajar da yaran ta suka sa mu b'ata lokaci na. Dan idan za mu kwana mu wuni ba zamu gama lissafe adadin abubuwan azzikin ba. Bayan su na mutane na ta watsewa. Ranar da 'yan uwan Haajar za su tafi ,kyauta daddy ya musu ba ni da kyauta ba. Sun ji dad'i matuqa sun kuma yaba da irin mijin ta Haajar ta samu. Bayan kowa ya gama tafiya. Haajar Sai da ta nemi inda za ta ajiye kayan yaran ,dan tsabar sun mata yawa. Uban gayyar kuwa wato daddy ,kyutar gidan gonar shi sukutum ya yiwa yaran shi. Haajar ba ta so ba Dan gani take abun ya yi yawa. Ga wa'yancan ga kuma wannan. Hadda k'wallan ta Dan farin ciki. Account Daddy ya bud'ewa yaran ya zuba musu duk kud'ad'en da suka samu. Haajar ta tambaye sa akan ya za'ayi da su yace ta yi amfani da su idan ta na da buqata Dan shi dai idan bai qara musu ba bazai karb'a sisi ba. Shawartar shi Haajar ta yi akan to ko ta bud'e gidauniya na taimakawa gajiyayyu da nakasassu. Daddy yace wannan shawara ce mai kyau. Hakan kuwa aka yi. Kafin kace me sunan Haajar da tallafin ta ya zaga sakkwato da kewaye.
Bayan sun yi arba'in. Suka shirya Dan zuwa gano Hajiya Gwaggo da ta dad'e a kwance ba tada lafiya. Gaba d'ayan su suka tafi. Yadda su ka samu Hajiya gwaggo kam rai hannun Allah. Washe garin zuwan su wata tsohuwa mai suna TANI ta zo gidan. Hannun ta d'aya a shanye. Aka tambaye ta wa take nema? Tace Hajiya Gwaggo. Nan aka kaita taga yadda jikin Hajiya gwaggon ya yi. Matar nan ta fashe da kuka. Nan ta soma basu labarin abunda ya wuce shekaru aru-aru. Ga Hajiya sakina a zaune kishiyar Hajiya Gwaggo ,ga hajiyar daddy da daddyn kan shi ,ga wasu daga cikin 'ya'yan Hajiya sakina. Haajar ma na daga gefe a zaune. Matar mai suna TANI tace "Tun suna 'yan mata sun gina rayuwar su akan Neman duniya da son zuciya ita da Hajiya Gwaggo. Ba su da aiki sai shiga malamai. A haka har suka yi aure. Ko da mijin Hajiya Gwaggo zai auro Hajiya sakina babu inda ba su shiga ba Dan su hana wannan auren ,amma duk inda suka shiga sai a ce musu wannan aure ba fa shi. A haka aka zo aka yi auren har Hajiya sakina ta fara haihuwa. Duk lokacin da Hajiya sakina ta samu ciki sai sun je an yi musu duba. Har lokacin da ta samu cikin mahaifin daddy aka fad'a musu cewa namiji za'a haifa, kuma mai arziki. Nan fa muka dinga k'ulla tuggu akan yadda za mu zubar da cikin amma Allah ya yi sai abunda ke cikin nan ya ta ka doran k'asa. To dama a lokacin Hajiya Gwaggon itama tana da ciki. Allah kuma yasa lokacin haihuwar su yazo rana d'aya. Mu ka yi amfani da wannan damar muka canza 'ya'yan. A inda muka d'auke d'an Hajiya sakina wato mahaifin daddy mu ka sauya shi da 'yar Hajiya Gwaggon Dan ace ita ta haifa. Ashe da ma 'yar da muka sauya wa muka ba Hajiya sakina ba mai zama bace, Dan tun kafin a yi suna Allah ya yi Mata rasuwa. Hajiya Gwaggo kuma ta ci gaba da rik'e d'an Hajiya sakina a matsayin na ta." Tsohuwar nan ta sake fashewa da kuka. Tace "Na ga jarabawar rayuwa da mugayen qaddarori da bazan so ace na mutu a ciki ba. Duk Wanda muka zalunta na yi ta k'ok'arin ganin na nema inda yake na ba shi hakuri. Nan ma kusan sama da shekaru goma ina Neman gidan amma Allah bai sa na gane gidan ba Sai yau." Tsohuwar na kuka tana Neman gafarar su. Hajiya sakina tace ta yafe mata ta ta shi ta tafi. Hajiya Gwaggo ko hawaye ne ya shiga wanke mata fuska ,tana so ta nemi yafiyar su amma ba dama ciwo ya ci qarfin ta. Hajiya sakina na hawaye tace wallahi ta yafe mata har ga Allah ta kuma gargad'e su akan ba ta yadda a fitar da zancen ba. Tun da har Wanda ake yi Dan shi ya mutu. Ranar kowa da abun ya kwana a rai. Abu sai kace wasan kwaikwayo. Washe gari kiran sallar farko na asubahi Hajiya Gwaggo ta amsa kiran ubangiji. Hajiya sakina ta yi kuka kamar ba gobe ,Dan ita har ga ba ta tab'a rik'e Hajiya Gwaggo a ran ta ba. Tana kuma matuqar qaunar ta har cikin zuciyar ta ,musamman jiya da ta ji ance ta riqe d'an da ta haifa. Abunda ta yadda da shi shine ,babu Wanda zai so naka har ya rik'e face masoyin ka...
MUJE ZUWA💃
TAKU HAR KULLUM
SIDIYA...✍️
[8/26, 7:29 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠
*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_*
(On ward together)
*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*
_BABI NA ARBA'IN DA BAKWAI_
*____________________________*
Misalin k'arfe Tara da safe aka yi jana'izar Hajiya Gwaggo aka kai ta makwancin ta. Kusan duk Wanda ya bud'e baki Allah wadai yake da halayyar Hajiya Gwaggo. Banda Hajiya sakina da ke ta faman kuka tana fad'in ta yafewa Hajiya Gwaggo duk abunda ta yi mata duniya da lahira. A gefe d'aya kuma ahalin gidan sai k'ara jimanta lamarin suke yi wai Hajiya Gwaggo ba ita ce ta haifi Baba Alhaji ba mahaifin Daddy,,, kai wannan Abu da d'aure kai yake. Ran da aka yi addu'an uku jama'a suka fara watsewa, yayinda wasu daga cikin ahalin wannan gida ke jin dad'in mutuwar Hajiya Gwaggo, a cewar wasu daga ciki ,ta gallaza musu ta addaba musu, su da gidan mahaifin su amma ba su da saqat. 'Ya'yan Hajiya sakina sai murna suke yi na kasancewar daddy d'an d'an uwan su ne. Suka zauna suka tattauna akan yadda za su k'arfafa zumuncin su, a ka saida magana cewa za'a dinga had'uwa anan gida duk bayan wata uku lokacin 'ya'yan su dake makaranta sun samu hutu, ya ka ma zama hud'u kenan a shekara. Wannan batu ya yi wa kowa dad'i. Daga su Haajar ba su baro ba sai da aka sanya ranar auren Suxee da Barr Kabir nan da wata uku me kamawa. Aka sanya na wasu 'yan matan wa'yan da 'ya'yar daddy wata biyu bayan bikin Suxee. Ba'a tashi daga taron ba saida Hajiya sakina ta yi musu wasu 'yan nasihohi masu ratsa jiki. Kusan dikkanin su da farin ciki suka watse cike da d'aukin junan su. Daga haka kowa ya watse, ciki yadda su daddy. Rayuwa ta dawo musu sabuwa.