Sashe 4
Gidan Misbahu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"To Anty Amaryar ,wannan shine b'angaren ki ,da fatar komai ya miki? Idan da akwai abunda kike buqata zaki iya sanar da talatu se ta fad'a mun "
Wani guntun numfashi khaltum ta sauke ,kafin tace
"Kar ki damu kanki suxee komai yayi ,nagode sosai da kulawar ki. "
"Bakomai Anty Amarya kema ai yanzu kin shigo cikin mu. Ni zan wuce sashen mu" suxee ta fad'a tare da mik'ewa.
"A huta gajiya. ki gaida mumyn taku Dan Allah kafin in shigo" khaltum ta fad'a kamar mutuniyar kirki
"Zata ji insha Allah" suxee ta bata amsa sannan tayi ficewar ta...
Sashen su ta nufa. Seda ta fara laqewa d'akin kubra taga bata nan ,sannan ta sauko k'asa zuwa d'akin su. Wanka haseena tayi sannan tawa Auta. Suxee ce ta shigo d'auke da sallama ,kan gado ta fad'a tare da fad'in
"Wash Allah! Na gaji sosai. Haseena akwai ruwan zafi a hitan toilet kuwa naga kamar kunyi wanka?"
"Eh akwai" haseena ta bata amsa a tak'aice ,Dan gaba d'aya haushin suxee take ji ,musamman data ga ta fiye zak'ewa akan auren da daddy ya k'ara.
Kaya suxee ta cire ,ta fad'a wanka. Bayan ta fito ne ,tana cikin shirya take cewa haseena "kin shiga d'akin mummy kuwa?"
D'an d'agowa haseena tayi tana duban ta lokacin tana had'awa Auta cornflakes ,maida duban ta tayi kan abunda take kafin tace
"Banje ba! Da alama ma bata gidan nan."
"Taya akayi kika gane, keda baki duba ba?"
"Ji fa Yaya suxee, to ni a abubuwan mummy wanne ne ban Riga na gama karanta ba? Muddin kika shigo baki ji tashin sauti ba ,to karki ma wahalar da kanki da zuwa duba ta ,bata nan ne kawai. Mummy na nanne zata bari kunnuwan jama'a ya sarara?"
Murmushi suxee tayi ,ko ba'a fad'a ba tasan gaskiya Haseena ta fad'i. Tace " Hakane kam. Bata ma nan Dan na duba".
"Uhm" inji haseena alamar kan ki ake ji.
Waya Haseena ta janyo tare da dialing wata number Dana ga ta saka 'MY HEADACHE'. Seda ya kusa tsinkewa sannan aka d'auka...
"Kina ina?" Haseena ta tambaya. A mamaki ne muryan kubra naji ya daki speakern wayan.
Kubra dake hotel tare da wani hamshak'in d'an siyasa suna aikata masha'an su ta amsa da
"Ina gidan hajja Fati. Ya akayi kun dawo ne?"
"Eh mun dawo ,Dan Allah ki dawo gida haka ,nace dai hajja Fatin nan koda yaushe kuna tare kamar cingom? To idan baki dawo Dan mu ba ,se ki dawo Dan kishiyar ki"!!
A zaton Haseena ko fad'in hakan ze tashi hankalin kubra ne ,amma amamakin ta ,dariya taji kubran nayi tare da cewa
"Cool down baby! Wacece kuma kishiya ,ban dawo Dan 'ya'ya naba, shine zan wani dawo Dan wata Abu wai kishiya? To ban gama abunda nake yi ba ,idan na gama ai zan dawo ko?
Haseena tantama take anya ma kubra taji abunda ta fad'a kuwa? Sake maimaita mata tayi
" mummy aure fa nace miki daddy ya k'ara shine kuma kike dariya?"
"Nasani ai Haseena, ba abunda bansani ba akan auren shi ,da naso in hana bama za'a kai yanzu ba ,banda lokacin su ne kawai." Cewar kubra
Haseena harta bud'e baki zata yi magana
"Mummy! " kubra ta katse ta
"Ke ni karki dame ni ,kisha fa mun kan Auta. Take care"...
Bata jira jin me Haseenan zata k'ara ce mata ba ,ta yanke kiran. Misalin k'arfe takwas na dare ,kubra tabar hotel d'in cikin shirin ta na zuwa club ,a cewar ta akwai babban casu da za'ayi a _shisha palace_ ,Wanda bata ka wani dalili daze sa tayi missing ba...
A b'angaren kubra kuwa ,abinci ta girka mai rai da lafiya iya k'warewar ta. Ta shirya komai akan dining sannan tayi dialing numbern daddy data rubuta wa _Alhaji na_, bugu d'aya biyu daddy ya d'auka. Cike da kissa kubra ke magana
" Dadddy na gama girki ,ka gaya wa su Hajiya k'arama ko"
Cike dajin dad'in yadda ta nuna damuwa da 'ya'yan shi yace
"To zan fad'a musu ,zaki gan su"
A shagwab'e tace "daddy to kai fa?"
Yace "karki damu ,ni bana jin yunwa ,idan ma ina da buk'ata Hajiya k'arama ce me girki na ,da abincin ta k'adai na saba. "
K'ara kashe murya tayi zatayi magana ,amma se jin tayi ya kashe wayan. Tsaki taja ,tare da fad'in
"Can da yawar ka. Tukunna ma ,ba'a fara wasar ba ai".
Daddy dase a lokacin yayi saving numbern khaltum, yana yanke kiran ya kira suxee dake kitchen ita da haseena suna shirya masa abinci, sheda mata yayi yadda yayi da khaltum ,tace
" to daddy zamu je insha Allah " shine amsar data bashi sannan ta yanke kiran. Haseena ce ta dube ta ,tare da cewa
"Keda waye kuma ?"
Suxee tace
"Daddy ne ,wai muje inji Anty Amarya ta gama mana abinci"
Baki haseena ta tab'e tana fad'in
"Ikon Allah. Wani iyayi ne wannan kuma? Da can kafin tazo wake dafa mana? Inace muke dafa wa kan mu?"
Suxee da dama tasan za'ayi haka tace
"Haba haseena daga abun azziki? Ina lefin ta?"
Haseena tace "kinga ni ban hanaki zuwa ba ,nidai bazani ba ,se kije keda Auta.
Auta dake tsakar kitchen d'in tana wasan ta ta karb'e da
" nima baza niba Yaya suxee "...
Suxee kad'ai taje taci abincin ta ta dawo.
Satin kubra d'aya a gidan ,hankalin ta a kwance ,tana cin gashin kanta ,babban abunda ke damun ta shine ,daddy ko so d'aya be tab'a neman ta da mu'amalar aure ba. A Daren ranar ta shirya tsaf Dan tunkarar shi , A wannen Daren ne kuma kubra ta dawo, wacce kusan tun tafiyar su daddy ,bata gidan se yau Allah yayi dawowar ta...
MUJE ZUWA💃
TAKU HAR KULLUM
SIDIYA...✍️
[7/14, 9:39 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠
*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_*
(On ward together)
*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*
_BABI NA SHIDA_
*_____________________*
_Kubra Kai tsaye sashen ta ta nufa. Da shigar sauti ta kunna sannan ,sannan ta shiga wanka. Kwalliya ta zauna ta tsantsara Wanda ya amshi kyaky-kyawar fuskar ta, doguwar Riga ta zuba ,Wanda ya amsa sunan shi ,gashi daka gani kai kace Dan ita akayi rigar... Wani abun se mata masu diri_
_Haseena najin kid'an na tashi ,dariyar takaici tayi ,Auta ce ta tambaye ta_
"Yaya haseena waye ya kun nawa mummy hoppers d'in ta?"
Cike da takaici haseena tace
"Waye kuwa ze kunna mata? Kakar d'an k'wairo ce ta dawo da kanta ,kyaji ma fiye da haka"
Suxee dake fito wa daga toilet ,dariya maganar haseenan ya bata ,tace
"Wllh ba kida kirki haseena! Mummyn ce ma kakar d'an k'wairo? A'ah kakar Baban gida kaka dawo ne ,shine ke tashe"
"Ai tama wuce nan alqur'qn". Haseena ta bata amsa ita fuskar ta d'auke da dariya.
A tare suke je duba ta ,Kafin sukai har auta ta riga su kaiwa. Cab'e ta kubra tayi fad'in
" Auta ta takaina! Nayi kewar ki sosai." Tsuke baki auta tayi tare da cewa
"Ni bakiyi kewa na ba ,inda haka ne shine zaki yi tafiya baki je dani ba? Ni sauke nima ,mun b'ata" ...Auta ta fad'a ciki da yarinta
Murmushi kubra tayi tare da shafo gefen fuskar ta ,tace cikin sigar lallashi
"Haba Auta ,yau kuma da mummy ake fad'a? To kiyi hak'uri ,ba gashi yanzu na dawo ba? "
Sallamar su suxee ne ya katse ta. Gaishe ta sukayi a ladabce ,kafin suka samu guri suka zaune kan lallausan kushin d'in da yayi daidai da tsarin parloun.
Suxee tace "mummy da kin gaya mana zaki dawo ai da se mu gyara miki waje ,ko musa a gyara"
Wani uwar harara haseena ta banka mata tare da cewa
"Meyasa kike bin son ran mummy ne Yaya suxee? Kafin kice haka me yasa bazaki fara tambayar ta inda taje ba harna tsawon sati d'aya. Kuma da izinin wa taje , nasan tabbas daddy be Sani ba."
Alama suxee tayiwa haseena alamar ta rufe mata baki ,amma Haseena bata ji waji ba ,ta d'ora da
"Ya ga gaskiya ga rantsuwa! Idan ma bazata dawo Dan kowa ba aise ta dawo Dan mu. Tsakanin mu da mahaifiyar mu ba wani shak'uwa ko jin k'ai ,se anyi magana tace tana son mu. Yanzu ki duba fa irin abunda sakacin ta ya janyo mata ,gashi nan daddy yaje ya k'aro aure ,kuma duk akan halayen ta ne. Sati d'aya da zuwan Anty khaltum kenan. Amma bata San mummy ba mummy bata San taba ,idan ta gane irin halin da muke ciki dake wallahi ba abunda zaki siya mana se wulaqanci, Wanda b zamu lamunce ba."
Wata uwar tsawa suxee ta daka wa haseena
"Enough haseena!!!"
"Ank'i ayi enough d'in." Haseena ta maida mata a hasale ,sannan ta maida duban ta ga kubra tace
"Idan baki gyara ma inaga an kawo wacce zata gyara ki ,idan kuma ita ma d'in ba'ayi dace ba ,ina add'uan allah ya kawo me canza ki da gaggawa.
Ya kamata ki iya takun ki Dan girman Allah karki ja mana gori da gore-gore. Yanzu bamu kad'ai bane a gidan, na rok'e ki"... Haseena ta k'arasa maganan tare had'a hannayen ta biyu alamar rok'o. Tana kaiwa nan tayi ficewar ta.
Suxee da kamar taci kanta ,kallon mummy take idon ta cike da hawaye tace " mummy kindai gani ko? Kin ga abunda son zuciyar ki yake nema yaja miki ko? Duba fa ,haseena 'yar cikin ki take tsaya wa a gaban ki ta gaggaya miki maganganu marasa dad'i, duk da akan gaskiyar ta take kuma duk abunda take fad'a nasani kum kema kinsan gaskiya ne. Dan Allah mummy...
"Ke!ke!!! Malama dakata mun Dan Allah. " kubra ta katse suxee ,sannan taci gaba da cewa...
"Naku a mene ku kuma? Rayuwa ta ko rayuwar Ku? Na hanaku kuma kuyi yadda kuke so ne? Se kune 'ya'yan ciki na zaku hanani sakata in wala? To baki isa ba, Wanda ya ajiye Ku ma yayi kad'an. Dan Allah matsa mun in wuce ,inje inyi abunda ze fish-she ni." Kubra ta fad'a kamar zata bangaje suxee. Anan tabar auta ta nufi sashen Daddy.
Wani guntun numfashi khaltum ta sauke ,kafin tace
"Kar ki damu kanki suxee komai yayi ,nagode sosai da kulawar ki. "
"Bakomai Anty Amarya kema ai yanzu kin shigo cikin mu. Ni zan wuce sashen mu" suxee ta fad'a tare da mik'ewa.
"A huta gajiya. ki gaida mumyn taku Dan Allah kafin in shigo" khaltum ta fad'a kamar mutuniyar kirki
"Zata ji insha Allah" suxee ta bata amsa sannan tayi ficewar ta...
Sashen su ta nufa. Seda ta fara laqewa d'akin kubra taga bata nan ,sannan ta sauko k'asa zuwa d'akin su. Wanka haseena tayi sannan tawa Auta. Suxee ce ta shigo d'auke da sallama ,kan gado ta fad'a tare da fad'in
"Wash Allah! Na gaji sosai. Haseena akwai ruwan zafi a hitan toilet kuwa naga kamar kunyi wanka?"
"Eh akwai" haseena ta bata amsa a tak'aice ,Dan gaba d'aya haushin suxee take ji ,musamman data ga ta fiye zak'ewa akan auren da daddy ya k'ara.
Kaya suxee ta cire ,ta fad'a wanka. Bayan ta fito ne ,tana cikin shirya take cewa haseena "kin shiga d'akin mummy kuwa?"
D'an d'agowa haseena tayi tana duban ta lokacin tana had'awa Auta cornflakes ,maida duban ta tayi kan abunda take kafin tace
"Banje ba! Da alama ma bata gidan nan."
"Taya akayi kika gane, keda baki duba ba?"
"Ji fa Yaya suxee, to ni a abubuwan mummy wanne ne ban Riga na gama karanta ba? Muddin kika shigo baki ji tashin sauti ba ,to karki ma wahalar da kanki da zuwa duba ta ,bata nan ne kawai. Mummy na nanne zata bari kunnuwan jama'a ya sarara?"
Murmushi suxee tayi ,ko ba'a fad'a ba tasan gaskiya Haseena ta fad'i. Tace " Hakane kam. Bata ma nan Dan na duba".
"Uhm" inji haseena alamar kan ki ake ji.
Waya Haseena ta janyo tare da dialing wata number Dana ga ta saka 'MY HEADACHE'. Seda ya kusa tsinkewa sannan aka d'auka...
"Kina ina?" Haseena ta tambaya. A mamaki ne muryan kubra naji ya daki speakern wayan.
Kubra dake hotel tare da wani hamshak'in d'an siyasa suna aikata masha'an su ta amsa da
"Ina gidan hajja Fati. Ya akayi kun dawo ne?"
"Eh mun dawo ,Dan Allah ki dawo gida haka ,nace dai hajja Fatin nan koda yaushe kuna tare kamar cingom? To idan baki dawo Dan mu ba ,se ki dawo Dan kishiyar ki"!!
A zaton Haseena ko fad'in hakan ze tashi hankalin kubra ne ,amma amamakin ta ,dariya taji kubran nayi tare da cewa
"Cool down baby! Wacece kuma kishiya ,ban dawo Dan 'ya'ya naba, shine zan wani dawo Dan wata Abu wai kishiya? To ban gama abunda nake yi ba ,idan na gama ai zan dawo ko?
Haseena tantama take anya ma kubra taji abunda ta fad'a kuwa? Sake maimaita mata tayi
" mummy aure fa nace miki daddy ya k'ara shine kuma kike dariya?"
"Nasani ai Haseena, ba abunda bansani ba akan auren shi ,da naso in hana bama za'a kai yanzu ba ,banda lokacin su ne kawai." Cewar kubra
Haseena harta bud'e baki zata yi magana
"Mummy! " kubra ta katse ta
"Ke ni karki dame ni ,kisha fa mun kan Auta. Take care"...
Bata jira jin me Haseenan zata k'ara ce mata ba ,ta yanke kiran. Misalin k'arfe takwas na dare ,kubra tabar hotel d'in cikin shirin ta na zuwa club ,a cewar ta akwai babban casu da za'ayi a _shisha palace_ ,Wanda bata ka wani dalili daze sa tayi missing ba...
A b'angaren kubra kuwa ,abinci ta girka mai rai da lafiya iya k'warewar ta. Ta shirya komai akan dining sannan tayi dialing numbern daddy data rubuta wa _Alhaji na_, bugu d'aya biyu daddy ya d'auka. Cike da kissa kubra ke magana
" Dadddy na gama girki ,ka gaya wa su Hajiya k'arama ko"
Cike dajin dad'in yadda ta nuna damuwa da 'ya'yan shi yace
"To zan fad'a musu ,zaki gan su"
A shagwab'e tace "daddy to kai fa?"
Yace "karki damu ,ni bana jin yunwa ,idan ma ina da buk'ata Hajiya k'arama ce me girki na ,da abincin ta k'adai na saba. "
K'ara kashe murya tayi zatayi magana ,amma se jin tayi ya kashe wayan. Tsaki taja ,tare da fad'in
"Can da yawar ka. Tukunna ma ,ba'a fara wasar ba ai".
Daddy dase a lokacin yayi saving numbern khaltum, yana yanke kiran ya kira suxee dake kitchen ita da haseena suna shirya masa abinci, sheda mata yayi yadda yayi da khaltum ,tace
" to daddy zamu je insha Allah " shine amsar data bashi sannan ta yanke kiran. Haseena ce ta dube ta ,tare da cewa
"Keda waye kuma ?"
Suxee tace
"Daddy ne ,wai muje inji Anty Amarya ta gama mana abinci"
Baki haseena ta tab'e tana fad'in
"Ikon Allah. Wani iyayi ne wannan kuma? Da can kafin tazo wake dafa mana? Inace muke dafa wa kan mu?"
Suxee da dama tasan za'ayi haka tace
"Haba haseena daga abun azziki? Ina lefin ta?"
Haseena tace "kinga ni ban hanaki zuwa ba ,nidai bazani ba ,se kije keda Auta.
Auta dake tsakar kitchen d'in tana wasan ta ta karb'e da
" nima baza niba Yaya suxee "...
Suxee kad'ai taje taci abincin ta ta dawo.
Satin kubra d'aya a gidan ,hankalin ta a kwance ,tana cin gashin kanta ,babban abunda ke damun ta shine ,daddy ko so d'aya be tab'a neman ta da mu'amalar aure ba. A Daren ranar ta shirya tsaf Dan tunkarar shi , A wannen Daren ne kuma kubra ta dawo, wacce kusan tun tafiyar su daddy ,bata gidan se yau Allah yayi dawowar ta...
MUJE ZUWA💃
TAKU HAR KULLUM
SIDIYA...✍️
[7/14, 9:39 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠
*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_*
(On ward together)
*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*
_BABI NA SHIDA_
*_____________________*
_Kubra Kai tsaye sashen ta ta nufa. Da shigar sauti ta kunna sannan ,sannan ta shiga wanka. Kwalliya ta zauna ta tsantsara Wanda ya amshi kyaky-kyawar fuskar ta, doguwar Riga ta zuba ,Wanda ya amsa sunan shi ,gashi daka gani kai kace Dan ita akayi rigar... Wani abun se mata masu diri_
_Haseena najin kid'an na tashi ,dariyar takaici tayi ,Auta ce ta tambaye ta_
"Yaya haseena waye ya kun nawa mummy hoppers d'in ta?"
Cike da takaici haseena tace
"Waye kuwa ze kunna mata? Kakar d'an k'wairo ce ta dawo da kanta ,kyaji ma fiye da haka"
Suxee dake fito wa daga toilet ,dariya maganar haseenan ya bata ,tace
"Wllh ba kida kirki haseena! Mummyn ce ma kakar d'an k'wairo? A'ah kakar Baban gida kaka dawo ne ,shine ke tashe"
"Ai tama wuce nan alqur'qn". Haseena ta bata amsa ita fuskar ta d'auke da dariya.
A tare suke je duba ta ,Kafin sukai har auta ta riga su kaiwa. Cab'e ta kubra tayi fad'in
" Auta ta takaina! Nayi kewar ki sosai." Tsuke baki auta tayi tare da cewa
"Ni bakiyi kewa na ba ,inda haka ne shine zaki yi tafiya baki je dani ba? Ni sauke nima ,mun b'ata" ...Auta ta fad'a ciki da yarinta
Murmushi kubra tayi tare da shafo gefen fuskar ta ,tace cikin sigar lallashi
"Haba Auta ,yau kuma da mummy ake fad'a? To kiyi hak'uri ,ba gashi yanzu na dawo ba? "
Sallamar su suxee ne ya katse ta. Gaishe ta sukayi a ladabce ,kafin suka samu guri suka zaune kan lallausan kushin d'in da yayi daidai da tsarin parloun.
Suxee tace "mummy da kin gaya mana zaki dawo ai da se mu gyara miki waje ,ko musa a gyara"
Wani uwar harara haseena ta banka mata tare da cewa
"Meyasa kike bin son ran mummy ne Yaya suxee? Kafin kice haka me yasa bazaki fara tambayar ta inda taje ba harna tsawon sati d'aya. Kuma da izinin wa taje , nasan tabbas daddy be Sani ba."
Alama suxee tayiwa haseena alamar ta rufe mata baki ,amma Haseena bata ji waji ba ,ta d'ora da
"Ya ga gaskiya ga rantsuwa! Idan ma bazata dawo Dan kowa ba aise ta dawo Dan mu. Tsakanin mu da mahaifiyar mu ba wani shak'uwa ko jin k'ai ,se anyi magana tace tana son mu. Yanzu ki duba fa irin abunda sakacin ta ya janyo mata ,gashi nan daddy yaje ya k'aro aure ,kuma duk akan halayen ta ne. Sati d'aya da zuwan Anty khaltum kenan. Amma bata San mummy ba mummy bata San taba ,idan ta gane irin halin da muke ciki dake wallahi ba abunda zaki siya mana se wulaqanci, Wanda b zamu lamunce ba."
Wata uwar tsawa suxee ta daka wa haseena
"Enough haseena!!!"
"Ank'i ayi enough d'in." Haseena ta maida mata a hasale ,sannan ta maida duban ta ga kubra tace
"Idan baki gyara ma inaga an kawo wacce zata gyara ki ,idan kuma ita ma d'in ba'ayi dace ba ,ina add'uan allah ya kawo me canza ki da gaggawa.
Ya kamata ki iya takun ki Dan girman Allah karki ja mana gori da gore-gore. Yanzu bamu kad'ai bane a gidan, na rok'e ki"... Haseena ta k'arasa maganan tare had'a hannayen ta biyu alamar rok'o. Tana kaiwa nan tayi ficewar ta.
Suxee da kamar taci kanta ,kallon mummy take idon ta cike da hawaye tace " mummy kindai gani ko? Kin ga abunda son zuciyar ki yake nema yaja miki ko? Duba fa ,haseena 'yar cikin ki take tsaya wa a gaban ki ta gaggaya miki maganganu marasa dad'i, duk da akan gaskiyar ta take kuma duk abunda take fad'a nasani kum kema kinsan gaskiya ne. Dan Allah mummy...
"Ke!ke!!! Malama dakata mun Dan Allah. " kubra ta katse suxee ,sannan taci gaba da cewa...
"Naku a mene ku kuma? Rayuwa ta ko rayuwar Ku? Na hanaku kuma kuyi yadda kuke so ne? Se kune 'ya'yan ciki na zaku hanani sakata in wala? To baki isa ba, Wanda ya ajiye Ku ma yayi kad'an. Dan Allah matsa mun in wuce ,inje inyi abunda ze fish-she ni." Kubra ta fad'a kamar zata bangaje suxee. Anan tabar auta ta nufi sashen Daddy.