Sashe 34
Gidan Misbahu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hajiya khairi na kuka ta shiga Neman yafiyar hajiya akan abubuwan da suka faru. Duk da hajiya na takaicin sanin hajiya khairi da ta yi. Be hana ta yafe mata ba. K'anwar mahaifin Khaltum da aka zo tare da ita ne ta dinga maidawa Hajiya khairi da martanin abubuwan da suka faru. Hajiyar daddy ta yi ta mata fad'a akan ya kamata su yadda da qaddara komai ya wuce. Mahaifin Khaltum har hawaye sai da ya zubar lokacin da ya halin da 'yar shi ke ciki. Da Hajiya khairi ta nema yafiyar sa ko kad'an bai yi qasa a guiwa ba wajen yafe ta ba saboda 'yar shi.
Dikkan su suna zaune kowa sai sannu yake wa Khaltum da bata San suna yi ba. A hankali Khaltum ta bud'e idon ta ta zuba su kan k'ofar shigowa. Hannu take k'ok'arin d'agawa tana nuna k'ofar ,amma ba su ga kowa ba. Jini ne ya shiga fito ma ta hanci da baki, a gefe d'aya kuma tana ci gaba da nuna k'ofa.
Da sauri Haajar ta je ta kira likitocin da ke kula da ita. Amma kafin su k'araso rai yayi halin shi. Dan kuwa Allah ya yiwa Khaltum rasuwa.
Hajiya khairi ta yi kuka kamar ba gobe. Kowa sai da ya tausaya mata. A ranar da jimamin abun su hajiya su ka koma gida. Washe gari aka wuce aka wuce da gawar Khaltum Dan ayi mata sutura akai ta gidan ta na gaskiya, Wanda tare da mahaifin Khaltum d'in aka wuce...
MUJE ZUWA💃
TAKU HAR KULLUM
SIDIYA...✍️
[8/20, 12:19 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠
*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_*
(On ward together)
*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*
_BABI NA ARBA'IN DA UKU_
*___________________________*
Washe gari da yamma su Haajar na zaune a sashen Hajiya su na ta qara ji manta al-amarin da ya faru jiya a asibiti, sai ga wani al-amarin ya sake zuwa. Dan kuwa Barr Kabir ne ya zo musu da labarin cewa an yanke wa Lubabatu kisa ta hanyar rataya ,sakamakon kisan kai da ta yi har so biyu ta kuma yi yunqurin sake aikwatar da wani a karo na uku ,wannan ne yasa babu wani hukunci da alqalin ya ga yafi cancanta da Lubabatu bisa ga doka sama da rataye ta ,a hakan mai wai an yi mata da sauqi ne. Wannan labari shi ma ba kad'an ba ya sake d'aga hankalin su hajiya ,Haajar hadda zubar da 'yar k'walla saboda tausayi. Barr tambayar Hajiya ya yi akan ina Daddy? Hajiya tace "ai tun lokacin da komai ya warware Daddy ba ya zama Dan yanzu ma harkokin kasuwancin sai dad'a bud'e masa suke yi". Abu mai San yi Haajar ta kawo wa Barr tace wa hajiya " ni zan je in kwanta kai na ne ke d'an mun ciwo ". Hajiya tace " to Allah yasa kaffara ne. Ki tabbatar kin sha magani kafin ki kwantan. Tukunna ma kin ci abinci?" D'an sosa k'eya Haajar ta yi tare da cewa "Na sha shayi d'azu hajiya" hajiya tace "to ai ka ji shashanci. Wai shayi? Naga shayi ai ruwa ne ba abinci ba. Mutum yasan ba shi kad'ai ba amma sai sakaci. To maza kije ki nema abinci ki ci kafin ki fara aikin baccin". Murmushi Haajar ta yi tace " To insha Allahu zan ci hajiya". Hajiya tace "to ai shikenan. Sai kin fito" daga haka Haajar ta yi sallama da Barr ta wuce sashen ta. Kusan duk lokacin da Haajar za ta ji abunda ya d'aga mata hankali sai kan ta ya yi ciwo Wanda idan ba bacci ta samu ba bata samun sauqi, ita kuma da haka laulayin yazo mata.
Barr kafe Suxee da ido ya yi, da ke kwance tana aikin daddanna waya. Hajiya tace "tashi Hajiya k'arama ki canza mana tasha zuwa sunnah tv saboda k'aratowar magriba." Ta shi suxee ta yi ta canza tasha kamar yadda Hajiya tace sannan ta dawo ta kwanta. Barr yace "Hajiya na ji kince Hajiya k'arama? Ba dai ita bata wannan ta girma haka?" Murmushi Hajiya ta yi irin na su na manya tace "Yo kai da kabiru da wautar ka da wacece?" Yace "wallahi Hajiya ban d'auka ita bace ,saboda nasan ai ke d'in ta mutane ce ba'a raba ki da jama'a. Na ga ta girma ne sosai". Hajiya tace " Lallai kuwa ga ta nan dai. An gama makaranta tuni ,banda Hajiya Gwaggo ma ta hana da yanzu ta yi nisa a karatun jami'a. Ina ga ko dan ba'a k'asar ka ke zaune bane tun wancan lokacin shiyasa ,kuma kaga ba Ku tab'a had'u wa a kano waje na ba. Lokacin da zasu zo sai sun tafi da jimawa kai kuma sai ka zo."
Da mamaki Barr yace "wannan haka yake. Amma kuwa na ji kunya ,mutum da jinin shi ace ya kasa gane shi". Iya Murmushi kawai Hajiya ta yi. Barr yace " To ai ita d'in ne ma naga bata fiye magana ba". Hajiya tace "Ai haka ta ke Hajiya k'arama ba ta wani fiye magana ba musamman ma idan ba ta San mutum ba. Da dai marigayiya Haseena ce idan ka zo sai ka gaji da surutu" Barr yace "Allah sarki. Allah ya gafarta mata yasa ta huta. Hajiya ta amsa da " ameen". Daga haka tace "bari in shiga daga ciki kafin lokacin sallah ya k'arato." Har k'asa Barr ya zuqunna yace "a fito lafiya hajiya". Hajiya ta shige ,shi kuma ya koma ya zauna. Sun dad'e a zaune tsakanin shi da Suxee ba Wanda yace wa kowa komai ,ganin haka yasa ya kauda shirun da d'an d'auko wa Suxee hira. Sama sama dai suka d'an dinga hira anan har yake gaya mata yadda alaqar shi ta ke da Hajiya. Sai a lokacin ne ma suxee ta d'an sakar masa fuska. Ranar anan Barr ya ci abincin dare ,ya ta jiran daddy ya dawo su gaisa amma bai dawo da wuri ba ,ganin dare na yi yasa ya yi musu sallama ya tafi.
Wani daren asabar Haajar na zaune tare da daddy suna hira. Ya na bata labarin irin ci gaban da ya samu a harkar kasuwancin shi cikin d'an k'ank'anin lokaci, Wanda duk ya ta'allaqa samun nasarorin akan Haajar. Haajar ta nuna jin dad'in ta ma matuqa game da yabon da ta samu a wajen daddy tare da yi masa fatar samun nasorin da ya fi wannan.
Wani abunda mai karatu bai sani ba shine. Tun bayan lokacin da wancan al-amarin ya faru ,daddy bai sake kusantar Haajar ba, ba kuma Wani abun bane daban ,tsabar nauyin Haajar d'in yake ji ,ya ke kuma ganin idan ya nema ta kamar bai kyauta ba sakamakon abunda ya faru tsakani shi da ita a baya. Dukda kuwa yaji cewar a wancan lokacin duk Haajar d'in na a matsayin matar shi, amma ya kasa yafe wa kan shi. Tun Haajar na tunanin ko akwai wata matsalar ce a k'asa Wanda bata San da shi ba da yasa daddy ya k'i Neman ta a shimfid'a, har ta gano ba komai kawai nauyin ta daddy ke ji ba kuma Dan baya sha'awar ta ba ,kawai yana kai zuciyar shi nisa ne. Ganin haka yasa Haajar ta shirya tsaf Dan k'arawa kan ta daraja da k'ima a idon mijin ta. Washe gari da daddare bayan ta yi sallama da su Hajiya ta dawo sashen ta. Ta sake yin wani sabon girkin da ta San mijin ta ya fi son shi sama da kowani abinci. Bayan ta gama ta ci ado matakin k'arshe ,sannan ta zauna tana jiran dawowar farin cikin ta.
Sai wuraren goma na dare daddy ya shigo gida. Sashen hajiya ya fara zuwa ya taradda sun yi bacci, bai yi k'ok'arin ta shin su ba. Ya wuce zuwa sashen Haajar. Tun farkon shigar shi ya ga wasu sababbin sauyi. Da wani irin k'amshi mai matuqar sanyaya ruhi ya fara cin karo. Haajar ce ta fito cikin wasu k'ananan kaya Riga da wando masu matuqar d'aukar hankalin mai kallon ta. Wannan ya k'ara tabbatar wa daddy da cewa yau d'in na musamman ne. Wani salo na mai tafiyar da nutsuwa ta dinga yi masa. Ruwan wanka ta fara had'a nasa ,ta taimaka masa ya cire kayan sa. Daddy shi dai sai bin ta da ido ya ke yi yana kallon ikon Allah, Haajar d'in ce duk ta canza masa yau d'in kamar ba ita ba.
Wani abun mamakin ma bai wuce ta yaga alamar cewa tare take son suyi wankan ba. Dan bai tab'a ganin tsaraicin ta ba. Kullo band'akin tare da zare kayan da ke jikin ta d'aya bayan d'aya. Zaro ido daddy ya shiga yi yana mazurai kamar yau ne rana ta farko daya fara ganin tsaraicin mace. Kusan sumar tsaye ya yi lokacin da ya yi tozali da kyaky-kyawar surar jikin Haajar mai matuqar rikitarwa.
Salo ta dinga yi masa ko a wajen wankan ,da k'yar daddy ya iya k'arfin halin had'i yawun sa. Bayan sun fito ba shi wuri ta yi ya kimtsa ita kuma ta koma d'ayan d'akin ta shiryo cikin wasu kayan bacci masu masifar kyau ,Wanda kusan da su da babu ba suda banbanci. Abinci ta fara gaba to wa daddy. Da kanta ta dinga ba shi a baki ,daddy kuwa dak'yar abincin ke wuce masa a mak'oshi Dan kusan ma ko gard'in abincin baya ji saboda abun da yake gaban sa ya kauda duk wani d'and'ano dake bakin sa. Bai wani ci sosai ba sakamakon ya k'agu. Haajar kuwa da ta ga yana bakin hanya ,sai ruwan shagwab'a take zuba masa tana wani narke masa a jiki. Wannan yanayi da daddy ke ciki a yau sai yake jin kamar kar ya wuce. Iya soyayya, salo da k'arshen kissa da kisisi na irin na mu na manta wajen Jan hankalin namiji sai da Haajar ta baje shi a wannan Daren.
Daga nan ta ja su sai d'akin baccin su da ta k'awata da nau'in furai launin jajaye, ga wasu k'yandura a aka kunna suna fidda d'oruwar wuta. K'awa irin na masoya. Tsarin ya yi matuqar burge Daddy Wanda har sai da ya furta "ya yi kyau".
Dikkan su suna zaune kowa sai sannu yake wa Khaltum da bata San suna yi ba. A hankali Khaltum ta bud'e idon ta ta zuba su kan k'ofar shigowa. Hannu take k'ok'arin d'agawa tana nuna k'ofar ,amma ba su ga kowa ba. Jini ne ya shiga fito ma ta hanci da baki, a gefe d'aya kuma tana ci gaba da nuna k'ofa.
Da sauri Haajar ta je ta kira likitocin da ke kula da ita. Amma kafin su k'araso rai yayi halin shi. Dan kuwa Allah ya yiwa Khaltum rasuwa.
Hajiya khairi ta yi kuka kamar ba gobe. Kowa sai da ya tausaya mata. A ranar da jimamin abun su hajiya su ka koma gida. Washe gari aka wuce aka wuce da gawar Khaltum Dan ayi mata sutura akai ta gidan ta na gaskiya, Wanda tare da mahaifin Khaltum d'in aka wuce...
MUJE ZUWA💃
TAKU HAR KULLUM
SIDIYA...✍️
[8/20, 12:19 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠
*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_*
(On ward together)
*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*
_BABI NA ARBA'IN DA UKU_
*___________________________*
Washe gari da yamma su Haajar na zaune a sashen Hajiya su na ta qara ji manta al-amarin da ya faru jiya a asibiti, sai ga wani al-amarin ya sake zuwa. Dan kuwa Barr Kabir ne ya zo musu da labarin cewa an yanke wa Lubabatu kisa ta hanyar rataya ,sakamakon kisan kai da ta yi har so biyu ta kuma yi yunqurin sake aikwatar da wani a karo na uku ,wannan ne yasa babu wani hukunci da alqalin ya ga yafi cancanta da Lubabatu bisa ga doka sama da rataye ta ,a hakan mai wai an yi mata da sauqi ne. Wannan labari shi ma ba kad'an ba ya sake d'aga hankalin su hajiya ,Haajar hadda zubar da 'yar k'walla saboda tausayi. Barr tambayar Hajiya ya yi akan ina Daddy? Hajiya tace "ai tun lokacin da komai ya warware Daddy ba ya zama Dan yanzu ma harkokin kasuwancin sai dad'a bud'e masa suke yi". Abu mai San yi Haajar ta kawo wa Barr tace wa hajiya " ni zan je in kwanta kai na ne ke d'an mun ciwo ". Hajiya tace " to Allah yasa kaffara ne. Ki tabbatar kin sha magani kafin ki kwantan. Tukunna ma kin ci abinci?" D'an sosa k'eya Haajar ta yi tare da cewa "Na sha shayi d'azu hajiya" hajiya tace "to ai ka ji shashanci. Wai shayi? Naga shayi ai ruwa ne ba abinci ba. Mutum yasan ba shi kad'ai ba amma sai sakaci. To maza kije ki nema abinci ki ci kafin ki fara aikin baccin". Murmushi Haajar ta yi tace " To insha Allahu zan ci hajiya". Hajiya tace "to ai shikenan. Sai kin fito" daga haka Haajar ta yi sallama da Barr ta wuce sashen ta. Kusan duk lokacin da Haajar za ta ji abunda ya d'aga mata hankali sai kan ta ya yi ciwo Wanda idan ba bacci ta samu ba bata samun sauqi, ita kuma da haka laulayin yazo mata.
Barr kafe Suxee da ido ya yi, da ke kwance tana aikin daddanna waya. Hajiya tace "tashi Hajiya k'arama ki canza mana tasha zuwa sunnah tv saboda k'aratowar magriba." Ta shi suxee ta yi ta canza tasha kamar yadda Hajiya tace sannan ta dawo ta kwanta. Barr yace "Hajiya na ji kince Hajiya k'arama? Ba dai ita bata wannan ta girma haka?" Murmushi Hajiya ta yi irin na su na manya tace "Yo kai da kabiru da wautar ka da wacece?" Yace "wallahi Hajiya ban d'auka ita bace ,saboda nasan ai ke d'in ta mutane ce ba'a raba ki da jama'a. Na ga ta girma ne sosai". Hajiya tace " Lallai kuwa ga ta nan dai. An gama makaranta tuni ,banda Hajiya Gwaggo ma ta hana da yanzu ta yi nisa a karatun jami'a. Ina ga ko dan ba'a k'asar ka ke zaune bane tun wancan lokacin shiyasa ,kuma kaga ba Ku tab'a had'u wa a kano waje na ba. Lokacin da zasu zo sai sun tafi da jimawa kai kuma sai ka zo."
Da mamaki Barr yace "wannan haka yake. Amma kuwa na ji kunya ,mutum da jinin shi ace ya kasa gane shi". Iya Murmushi kawai Hajiya ta yi. Barr yace " To ai ita d'in ne ma naga bata fiye magana ba". Hajiya tace "Ai haka ta ke Hajiya k'arama ba ta wani fiye magana ba musamman ma idan ba ta San mutum ba. Da dai marigayiya Haseena ce idan ka zo sai ka gaji da surutu" Barr yace "Allah sarki. Allah ya gafarta mata yasa ta huta. Hajiya ta amsa da " ameen". Daga haka tace "bari in shiga daga ciki kafin lokacin sallah ya k'arato." Har k'asa Barr ya zuqunna yace "a fito lafiya hajiya". Hajiya ta shige ,shi kuma ya koma ya zauna. Sun dad'e a zaune tsakanin shi da Suxee ba Wanda yace wa kowa komai ,ganin haka yasa ya kauda shirun da d'an d'auko wa Suxee hira. Sama sama dai suka d'an dinga hira anan har yake gaya mata yadda alaqar shi ta ke da Hajiya. Sai a lokacin ne ma suxee ta d'an sakar masa fuska. Ranar anan Barr ya ci abincin dare ,ya ta jiran daddy ya dawo su gaisa amma bai dawo da wuri ba ,ganin dare na yi yasa ya yi musu sallama ya tafi.
Wani daren asabar Haajar na zaune tare da daddy suna hira. Ya na bata labarin irin ci gaban da ya samu a harkar kasuwancin shi cikin d'an k'ank'anin lokaci, Wanda duk ya ta'allaqa samun nasarorin akan Haajar. Haajar ta nuna jin dad'in ta ma matuqa game da yabon da ta samu a wajen daddy tare da yi masa fatar samun nasorin da ya fi wannan.
Wani abunda mai karatu bai sani ba shine. Tun bayan lokacin da wancan al-amarin ya faru ,daddy bai sake kusantar Haajar ba, ba kuma Wani abun bane daban ,tsabar nauyin Haajar d'in yake ji ,ya ke kuma ganin idan ya nema ta kamar bai kyauta ba sakamakon abunda ya faru tsakani shi da ita a baya. Dukda kuwa yaji cewar a wancan lokacin duk Haajar d'in na a matsayin matar shi, amma ya kasa yafe wa kan shi. Tun Haajar na tunanin ko akwai wata matsalar ce a k'asa Wanda bata San da shi ba da yasa daddy ya k'i Neman ta a shimfid'a, har ta gano ba komai kawai nauyin ta daddy ke ji ba kuma Dan baya sha'awar ta ba ,kawai yana kai zuciyar shi nisa ne. Ganin haka yasa Haajar ta shirya tsaf Dan k'arawa kan ta daraja da k'ima a idon mijin ta. Washe gari da daddare bayan ta yi sallama da su Hajiya ta dawo sashen ta. Ta sake yin wani sabon girkin da ta San mijin ta ya fi son shi sama da kowani abinci. Bayan ta gama ta ci ado matakin k'arshe ,sannan ta zauna tana jiran dawowar farin cikin ta.
Sai wuraren goma na dare daddy ya shigo gida. Sashen hajiya ya fara zuwa ya taradda sun yi bacci, bai yi k'ok'arin ta shin su ba. Ya wuce zuwa sashen Haajar. Tun farkon shigar shi ya ga wasu sababbin sauyi. Da wani irin k'amshi mai matuqar sanyaya ruhi ya fara cin karo. Haajar ce ta fito cikin wasu k'ananan kaya Riga da wando masu matuqar d'aukar hankalin mai kallon ta. Wannan ya k'ara tabbatar wa daddy da cewa yau d'in na musamman ne. Wani salo na mai tafiyar da nutsuwa ta dinga yi masa. Ruwan wanka ta fara had'a nasa ,ta taimaka masa ya cire kayan sa. Daddy shi dai sai bin ta da ido ya ke yi yana kallon ikon Allah, Haajar d'in ce duk ta canza masa yau d'in kamar ba ita ba.
Wani abun mamakin ma bai wuce ta yaga alamar cewa tare take son suyi wankan ba. Dan bai tab'a ganin tsaraicin ta ba. Kullo band'akin tare da zare kayan da ke jikin ta d'aya bayan d'aya. Zaro ido daddy ya shiga yi yana mazurai kamar yau ne rana ta farko daya fara ganin tsaraicin mace. Kusan sumar tsaye ya yi lokacin da ya yi tozali da kyaky-kyawar surar jikin Haajar mai matuqar rikitarwa.
Salo ta dinga yi masa ko a wajen wankan ,da k'yar daddy ya iya k'arfin halin had'i yawun sa. Bayan sun fito ba shi wuri ta yi ya kimtsa ita kuma ta koma d'ayan d'akin ta shiryo cikin wasu kayan bacci masu masifar kyau ,Wanda kusan da su da babu ba suda banbanci. Abinci ta fara gaba to wa daddy. Da kanta ta dinga ba shi a baki ,daddy kuwa dak'yar abincin ke wuce masa a mak'oshi Dan kusan ma ko gard'in abincin baya ji saboda abun da yake gaban sa ya kauda duk wani d'and'ano dake bakin sa. Bai wani ci sosai ba sakamakon ya k'agu. Haajar kuwa da ta ga yana bakin hanya ,sai ruwan shagwab'a take zuba masa tana wani narke masa a jiki. Wannan yanayi da daddy ke ciki a yau sai yake jin kamar kar ya wuce. Iya soyayya, salo da k'arshen kissa da kisisi na irin na mu na manta wajen Jan hankalin namiji sai da Haajar ta baje shi a wannan Daren.
Daga nan ta ja su sai d'akin baccin su da ta k'awata da nau'in furai launin jajaye, ga wasu k'yandura a aka kunna suna fidda d'oruwar wuta. K'awa irin na masoya. Tsarin ya yi matuqar burge Daddy Wanda har sai da ya furta "ya yi kyau".