Sashe 2
Gidan Misbahu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ai ki manta kawai hajia kubra ,dika dika suxee guda nawa ne ,yarinya ce bata San inda duniyar tasa gaba ba. Ina ganin wannan ma yayi mu bata lokaci ,nasan idan ta k'ara girma zata gane abunda muke ba kuskure bane kamar yadda take tunani ,ke wallahi ma se ta nemi ki d'ora ta a hanya ma" ...cewar hajja Fati
"Allah ko?" Kubra ta fad'a cike da jin dad'i
"Sosai ma kuwa" inji hajja Fati ,tana wani murmushin su na 'yan duniya. Hannu kubra ta bata suka kashe.
A lokacin Wasu sababbin hawayen bak'in ciki ya shiga wanke wa Suxee fuska. Cikin muryar kuka ta fara magana
"Tir da irin wannan shed'aniyar rayuwar taku ,dahar kuke tunanin zaku wayi gari Ku ganni a tawagar Ku, to idan ma mafarki kuke gara Ku farka ,Ku kuma sake tunani ,ni suxee bazan tab'a kasancewa a cikin Ku ba ,a yayin da bazan tab'a aikata abun da kuke so na aikata ba na sab'on Allah."
Lubcy dake daga gefe tana jin ruguntsumin da ake tafkawa. Tasowa tayi cikin tafiyar ta ta k'asaita ta k'araso inda suke ,tafe take tana busar da hayak'in sigarin da take zuk'a. Tafa kafad'ar Suxee tayi a lokaci d'aya kuma tana zagaya ta ,kai kace me shirin lashe mata kurwa. Murya can k'asa kamar me rad'a ,lubcy tace
"Cool down mana 'ya ta ! Dube ki fa yadda kike ta asarar hawayen ki ,kan abunda be taka kara ya karya kiyashi ba. Ki kwantar da hankalin ki ,wannan d'in da kike ganin muna yi bakomai bane ,waye ce da zamani. Suxee ki kalle ki ,kina da kyan fuska Dana sura ,zaki yi fitting ko wani namiji ehn. Ki ajiye guntun wa'azin ki a gefe kizo ki mori rayuwar ki ,kai kima gode wa Allah dahar ya baki uwa me tunani da hangen nisa."
Kwab'e hannun lubcy suxee tayi dake kafad'an ta ,ta gudu ta fice daga parloun tana k'ara fashewa da wani kuka me ban tausayi. Ta gama sauka stairs kenan taji tayi karo da mutum ,d'agowar da zatayi ta duba ,se taga daddyn ta yana sakar mata murmushi. Fad'awa jikin shi tayi tare da sake wani sabon kukan, lallashin ta ya shiga yi yana bubbuga bayan ta, kamar wata k'aramar yarinya 'yar goye ,ko be tambayi me ya same ta ba ,yasan baze wuce ita da ballagazar mahaifiyar taba. Janta yayi suka k'arasa cikin parloun ,ya zaunar da ita kan kujera ,sannan ya mik'e ya nufi parloun sama a fusace
"Kubra!" Ya kira ta cikin kakkausar murya. Wani kallon raini ta d'ago tana bin shi dashi.
Be jira ta amsa ba ya fara mata gargad'i
"Duk iskanci da shed'anancin da kika San kina ji ko kike yi ,ya tsaya iya kan ki ,kar ki kuskura ki tsoma 'ya'ya na a ciki ,hakan kuwa ba k'aramin sab'ani zamu samu ba, zaki iya mun komai ,ya tsaya iya kaina amma kar ya shafi 'ya'ya na. Na gaya miki". Ya k'arasa naganan tare da nuna ta da d'an yatsa.
Kallon lallai kinyi sake d'an zaki ya girma hajja Fati take yi mata ganin bata ce masa komai ba. Ita ma ido tayi mata alamar kar ta damu.
Daddy ci gaba yayi
" sannan Ku kuma..." Cak ya tsaya kamar Wanda aka zare wa lakka, sakamakon wani kambu da kubra ta murza Wanda ke mak'ale a tsintsiyar hannun ta.
"Fita ka bani waje sakarai kawai" shine kawai abunda kubra ta furta ,a mamaki na se naga daddy ya fita da sauri. Dariya dikkan su suka saka ,hajja Fati tace
"Haba yanzu dai naji magana ,amma yazo ze wani ishe mu da wak'e-wak'en shi na banza da wofi".
" Dama na barshi ne ya sarara kwana biyu ,amma tunda be San azziki ba ,yanzu ze dawo yin rayuwar kambu ,se yadda kambu yayi dashi." Kubra ta fad'a cikin isa da gadara.
Wani dariyar shed'anancin suka sake fashewa dashi, a lokaci d'aya suna mata wani irin kirari Wanda su kad'ai suka San me hakan ke nufi...
MUJE ZUWA💃
TAKU HAR KULLUM
SIDIYA...✍️
[7/12, 3:07 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠
*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_*
(On ward together)
*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*
_BABI NA UKU_
*_____________________*
_Da daddare misalin k'arfe goma sha d'aya na dare ,kubra ce a side d'in ta cikin shigarta na bacci , har ta kwanta ,se kuma ta tuna cewar gobe zata je k'asar NIJAR ita da hajja Fati Dan sako kambun ta, gashi ba wani isash-shen kud'i a hannun ta, wani guntun tsaki taja ,kafin ta sauko daga kan gadon._
_makeken wardrobe d'in ta ta bud'e ,ta d'auki kambun ta ,murza shi tayi sannan ta mak'ala shi a hannun ta. Gaban daddy ne yayi wani mummunan fad'uwa a lokacin da kubra ta murza kambun ta ,duk se yaji ya rasa me ke masa dad'i a wannan lokacin. Kai tsaye sashen shi ta nufa ,a d'aki ta same shi zaune da system a gaban shi ,sedai ga dikkan alama hankalin shi ba a wajen yake ba. Kamar ba kubran daya Sani ba ,k'arasowa tayi har inda yake zaune ,tad'an matsar da system din da ke gaban shi sannan ta samu guri ta zauna. D'an d'agowa yayi da mamaki yana bin ta da ido ,sanin kanshi ne azziki baya kawo kubra sashen shi._
_wani irin shu'umin murmushi ta sakar mishi tare da shafo gefen fuskar shi ,a lokaci d'aya kuma tace_
"Makullin drawer-n kud'in ka zaka bani" ta fad'a kamar me rad'a. Wani irin d'agowa daddy yayi yana mata kallon baki da hankali. Magana ze yi ,kawai se ta murza kambun hannun ta, nan take yaji kanshi yayi wani mumunan sarawa ,murmushin zaka bani ko Yaya ta masa ,sannan ta sake tambayar sa
"Ina keys d'in?"... Jiki a sanyaye daddy ya tashi ,ya d'auko mata makullan ya mik'a mata. Karb'a tayi tana bubbuga k'afad'ar shi tare da cewa
" wise man!" Sannan ta mik'e ta nufi drawern da kud'in suke. Bud'e wa tayi bata wani sha wahala ba dan tasan pin d'in bud'e akwatin kud'in. Kud'i kubra ta iba bani da kud'i ba ,kud'i bana wasa ba ,ni kaina bazan ce ga adadin kud'in ba. Bayan ta iba ,maida wa tayi ta rufe tare kai masa sambata a goshi ,sannan ta cillamai makullin ta fice abunta. Bayan ta fita ne daddy ya fara tunanin Maya faru dashi cikin 'yan mintunan nan ,yadai ga shigowar kubra har zuwa zaman da tayi ,amma baya nan kuma baze iya tuna komai ba. Kai ya dafe tare da furta "innalillahi wa'inna ilaihi raji'un! Hasbunallahu wani'imal wakil" har so uku ,nan danan yaji komai daya faru kamar a mafarki ne ,tashi yayi ya d'auro alwala ,ya gabatar da sallan nafila ,yana kan dadduma har aka kira sallan asuba ,seda ya shiga d'akin su suxee ya tashe su sannan ya fito da niyyar zuwa masallaci ,fitowar shi keda wuya, yaga wucewar hasken motar kubra ,alamar fita tayi. D'an tsayawa yayi kamar me tunani ,se kuma ya girgiza kai ya wuce abun shi...
Misalin k'arfe Tara na safe ,suxee da haseena suka fara shirye-shiryen breakfast kamar yadda suka saba. Ruwan zafin tea suka fara d'orawa ,sannan suka soya Doya da k'wai ,indomie suka dafa wa auta ,Dan bata da abun breakfast daya wuce wannan ,shi kuma daddy suka dama masa kunun gyad'a ,kasancewar yafi qaunar karyawa dashi sama da komai.
Goma da rabi daidai suka kammala tare da tsaftace ko ina. parlorn daddy suka kai komai ,akan dining suka jera. Suxee tace
"Yauwa haseena tunda mun gama komai inaga ,kije ki ta do Auta ,ni kuma in taso daddy! Kuma Dan Allah kiyi mata a hankali nasan halin ki"
Kwashewa da dariya haseena tayi tana cewa
"Kai Yaya suxee, ai Autar ce wata sa'in da k'ule me rai wallahi "
Suxee tace "nidai na gaya miki...
Bayan sun kammala karyawa ,daddy Yace
" inaga tunda kun samu Hutu ,kamata yayi mu shirya muje mu gaida Hajiya ta(mahaifiyar shi kenan). Tsalle auta ta daka tana cewa
"Daddy yaushe zamu je?"
Murmushi daddy yayi irin nasu na manya ,kafin yace
"A yau ma idan kuna so ai se muje Auta, kano aina maida ta kamar gida ,inaga se mubi jirgi kawai ma"
Nan danan suka cika parloun da ihu ,murna sosai suke yi zasu je ganin Hajiya. Cikin tsantsar so da qauna daddy ke bin su da kallo daya bayan daya ,idan akwai abunda daddy yafi so a duniya be fi sama da farin cikin 'ya'yan shiba.
cikin k'ank'anin lokaci suka shirya komai nasu ,a akwati daya suka shirya komai, misalin k'arfe biyu suka fita ,koda ukku tayi suna garin kano...
_Nijar..._ kubra ce zaune ita da hajja Fati a gaban boka RUBATSI... Wani arnen dariya RUBATSI ya fashe dashi irin nasu na abokan Iblis ,a lokaci d'aya kuma yana duba tsatsubar tsafin sa.
Ihu ya saki Wanda ya k'are d'e gaba d'aya dajin tarnak'aki , nan take tsuntsaye suka fara tashi ,wasu kuma sedai suka fad'o k'asa a mace ,saboda tsananin girman tsafin RUBATSI...
Wani bak'in madubi ya daka ,cikin k'ank'anin lokaci se ga daddy ya fito a ciki. Dariyar shi me tsinka hanjin me saurare ya sake fashewa dashi ,kafin ya gimtse fuska a take kamar be tab'a dariya a duniya ba.
"A yanzu haka mijin ki yana kano tare da 'ya'yan ki ,sannan wannan zuwan nashi ba alkhairi bane Dan kuwa ,a wannan zuwan mahaifiyar shi ta gama shirya komai Dan tabbatar da ya sake k'ara aure"...
Wani zaro ido kubra da hajja Fati suka shiga yi ,a lokaci d'aya hanjin kubra ya shiga k'ugi...
MUJE ZUWA💃
TAKU HAR KULLUM
SIDIYA...✍️
[7/13, 1:13 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠
*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_*
(On ward together)
*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*
_BABI NA HUD'U_
*_____________________*
_Tsabar kad'uwa da mamaki ne ya cika kubra ,Wanda ya assassa mata tunani iri daban daban._ _A tunanin ta tunda take da Misbahu bai tab'a tunanin k'arin aure ba sama da shekara goma sha takwas makamancin wannan be tab'a tasowa ba se ayau kuma ayanzu kamar yadda boka RUBATSI ya sheda mata._
_Hajja Fati ce tayi k'arfin halin cewa_
"Tsafi ya da fa! Yanzu menene abun yi kenan?"
"Allah ko?" Kubra ta fad'a cike da jin dad'i
"Sosai ma kuwa" inji hajja Fati ,tana wani murmushin su na 'yan duniya. Hannu kubra ta bata suka kashe.
A lokacin Wasu sababbin hawayen bak'in ciki ya shiga wanke wa Suxee fuska. Cikin muryar kuka ta fara magana
"Tir da irin wannan shed'aniyar rayuwar taku ,dahar kuke tunanin zaku wayi gari Ku ganni a tawagar Ku, to idan ma mafarki kuke gara Ku farka ,Ku kuma sake tunani ,ni suxee bazan tab'a kasancewa a cikin Ku ba ,a yayin da bazan tab'a aikata abun da kuke so na aikata ba na sab'on Allah."
Lubcy dake daga gefe tana jin ruguntsumin da ake tafkawa. Tasowa tayi cikin tafiyar ta ta k'asaita ta k'araso inda suke ,tafe take tana busar da hayak'in sigarin da take zuk'a. Tafa kafad'ar Suxee tayi a lokaci d'aya kuma tana zagaya ta ,kai kace me shirin lashe mata kurwa. Murya can k'asa kamar me rad'a ,lubcy tace
"Cool down mana 'ya ta ! Dube ki fa yadda kike ta asarar hawayen ki ,kan abunda be taka kara ya karya kiyashi ba. Ki kwantar da hankalin ki ,wannan d'in da kike ganin muna yi bakomai bane ,waye ce da zamani. Suxee ki kalle ki ,kina da kyan fuska Dana sura ,zaki yi fitting ko wani namiji ehn. Ki ajiye guntun wa'azin ki a gefe kizo ki mori rayuwar ki ,kai kima gode wa Allah dahar ya baki uwa me tunani da hangen nisa."
Kwab'e hannun lubcy suxee tayi dake kafad'an ta ,ta gudu ta fice daga parloun tana k'ara fashewa da wani kuka me ban tausayi. Ta gama sauka stairs kenan taji tayi karo da mutum ,d'agowar da zatayi ta duba ,se taga daddyn ta yana sakar mata murmushi. Fad'awa jikin shi tayi tare da sake wani sabon kukan, lallashin ta ya shiga yi yana bubbuga bayan ta, kamar wata k'aramar yarinya 'yar goye ,ko be tambayi me ya same ta ba ,yasan baze wuce ita da ballagazar mahaifiyar taba. Janta yayi suka k'arasa cikin parloun ,ya zaunar da ita kan kujera ,sannan ya mik'e ya nufi parloun sama a fusace
"Kubra!" Ya kira ta cikin kakkausar murya. Wani kallon raini ta d'ago tana bin shi dashi.
Be jira ta amsa ba ya fara mata gargad'i
"Duk iskanci da shed'anancin da kika San kina ji ko kike yi ,ya tsaya iya kan ki ,kar ki kuskura ki tsoma 'ya'ya na a ciki ,hakan kuwa ba k'aramin sab'ani zamu samu ba, zaki iya mun komai ,ya tsaya iya kaina amma kar ya shafi 'ya'ya na. Na gaya miki". Ya k'arasa naganan tare da nuna ta da d'an yatsa.
Kallon lallai kinyi sake d'an zaki ya girma hajja Fati take yi mata ganin bata ce masa komai ba. Ita ma ido tayi mata alamar kar ta damu.
Daddy ci gaba yayi
" sannan Ku kuma..." Cak ya tsaya kamar Wanda aka zare wa lakka, sakamakon wani kambu da kubra ta murza Wanda ke mak'ale a tsintsiyar hannun ta.
"Fita ka bani waje sakarai kawai" shine kawai abunda kubra ta furta ,a mamaki na se naga daddy ya fita da sauri. Dariya dikkan su suka saka ,hajja Fati tace
"Haba yanzu dai naji magana ,amma yazo ze wani ishe mu da wak'e-wak'en shi na banza da wofi".
" Dama na barshi ne ya sarara kwana biyu ,amma tunda be San azziki ba ,yanzu ze dawo yin rayuwar kambu ,se yadda kambu yayi dashi." Kubra ta fad'a cikin isa da gadara.
Wani dariyar shed'anancin suka sake fashewa dashi, a lokaci d'aya suna mata wani irin kirari Wanda su kad'ai suka San me hakan ke nufi...
MUJE ZUWA💃
TAKU HAR KULLUM
SIDIYA...✍️
[7/12, 3:07 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠
*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_*
(On ward together)
*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*
_BABI NA UKU_
*_____________________*
_Da daddare misalin k'arfe goma sha d'aya na dare ,kubra ce a side d'in ta cikin shigarta na bacci , har ta kwanta ,se kuma ta tuna cewar gobe zata je k'asar NIJAR ita da hajja Fati Dan sako kambun ta, gashi ba wani isash-shen kud'i a hannun ta, wani guntun tsaki taja ,kafin ta sauko daga kan gadon._
_makeken wardrobe d'in ta ta bud'e ,ta d'auki kambun ta ,murza shi tayi sannan ta mak'ala shi a hannun ta. Gaban daddy ne yayi wani mummunan fad'uwa a lokacin da kubra ta murza kambun ta ,duk se yaji ya rasa me ke masa dad'i a wannan lokacin. Kai tsaye sashen shi ta nufa ,a d'aki ta same shi zaune da system a gaban shi ,sedai ga dikkan alama hankalin shi ba a wajen yake ba. Kamar ba kubran daya Sani ba ,k'arasowa tayi har inda yake zaune ,tad'an matsar da system din da ke gaban shi sannan ta samu guri ta zauna. D'an d'agowa yayi da mamaki yana bin ta da ido ,sanin kanshi ne azziki baya kawo kubra sashen shi._
_wani irin shu'umin murmushi ta sakar mishi tare da shafo gefen fuskar shi ,a lokaci d'aya kuma tace_
"Makullin drawer-n kud'in ka zaka bani" ta fad'a kamar me rad'a. Wani irin d'agowa daddy yayi yana mata kallon baki da hankali. Magana ze yi ,kawai se ta murza kambun hannun ta, nan take yaji kanshi yayi wani mumunan sarawa ,murmushin zaka bani ko Yaya ta masa ,sannan ta sake tambayar sa
"Ina keys d'in?"... Jiki a sanyaye daddy ya tashi ,ya d'auko mata makullan ya mik'a mata. Karb'a tayi tana bubbuga k'afad'ar shi tare da cewa
" wise man!" Sannan ta mik'e ta nufi drawern da kud'in suke. Bud'e wa tayi bata wani sha wahala ba dan tasan pin d'in bud'e akwatin kud'in. Kud'i kubra ta iba bani da kud'i ba ,kud'i bana wasa ba ,ni kaina bazan ce ga adadin kud'in ba. Bayan ta iba ,maida wa tayi ta rufe tare kai masa sambata a goshi ,sannan ta cillamai makullin ta fice abunta. Bayan ta fita ne daddy ya fara tunanin Maya faru dashi cikin 'yan mintunan nan ,yadai ga shigowar kubra har zuwa zaman da tayi ,amma baya nan kuma baze iya tuna komai ba. Kai ya dafe tare da furta "innalillahi wa'inna ilaihi raji'un! Hasbunallahu wani'imal wakil" har so uku ,nan danan yaji komai daya faru kamar a mafarki ne ,tashi yayi ya d'auro alwala ,ya gabatar da sallan nafila ,yana kan dadduma har aka kira sallan asuba ,seda ya shiga d'akin su suxee ya tashe su sannan ya fito da niyyar zuwa masallaci ,fitowar shi keda wuya, yaga wucewar hasken motar kubra ,alamar fita tayi. D'an tsayawa yayi kamar me tunani ,se kuma ya girgiza kai ya wuce abun shi...
Misalin k'arfe Tara na safe ,suxee da haseena suka fara shirye-shiryen breakfast kamar yadda suka saba. Ruwan zafin tea suka fara d'orawa ,sannan suka soya Doya da k'wai ,indomie suka dafa wa auta ,Dan bata da abun breakfast daya wuce wannan ,shi kuma daddy suka dama masa kunun gyad'a ,kasancewar yafi qaunar karyawa dashi sama da komai.
Goma da rabi daidai suka kammala tare da tsaftace ko ina. parlorn daddy suka kai komai ,akan dining suka jera. Suxee tace
"Yauwa haseena tunda mun gama komai inaga ,kije ki ta do Auta ,ni kuma in taso daddy! Kuma Dan Allah kiyi mata a hankali nasan halin ki"
Kwashewa da dariya haseena tayi tana cewa
"Kai Yaya suxee, ai Autar ce wata sa'in da k'ule me rai wallahi "
Suxee tace "nidai na gaya miki...
Bayan sun kammala karyawa ,daddy Yace
" inaga tunda kun samu Hutu ,kamata yayi mu shirya muje mu gaida Hajiya ta(mahaifiyar shi kenan). Tsalle auta ta daka tana cewa
"Daddy yaushe zamu je?"
Murmushi daddy yayi irin nasu na manya ,kafin yace
"A yau ma idan kuna so ai se muje Auta, kano aina maida ta kamar gida ,inaga se mubi jirgi kawai ma"
Nan danan suka cika parloun da ihu ,murna sosai suke yi zasu je ganin Hajiya. Cikin tsantsar so da qauna daddy ke bin su da kallo daya bayan daya ,idan akwai abunda daddy yafi so a duniya be fi sama da farin cikin 'ya'yan shiba.
cikin k'ank'anin lokaci suka shirya komai nasu ,a akwati daya suka shirya komai, misalin k'arfe biyu suka fita ,koda ukku tayi suna garin kano...
_Nijar..._ kubra ce zaune ita da hajja Fati a gaban boka RUBATSI... Wani arnen dariya RUBATSI ya fashe dashi irin nasu na abokan Iblis ,a lokaci d'aya kuma yana duba tsatsubar tsafin sa.
Ihu ya saki Wanda ya k'are d'e gaba d'aya dajin tarnak'aki , nan take tsuntsaye suka fara tashi ,wasu kuma sedai suka fad'o k'asa a mace ,saboda tsananin girman tsafin RUBATSI...
Wani bak'in madubi ya daka ,cikin k'ank'anin lokaci se ga daddy ya fito a ciki. Dariyar shi me tsinka hanjin me saurare ya sake fashewa dashi ,kafin ya gimtse fuska a take kamar be tab'a dariya a duniya ba.
"A yanzu haka mijin ki yana kano tare da 'ya'yan ki ,sannan wannan zuwan nashi ba alkhairi bane Dan kuwa ,a wannan zuwan mahaifiyar shi ta gama shirya komai Dan tabbatar da ya sake k'ara aure"...
Wani zaro ido kubra da hajja Fati suka shiga yi ,a lokaci d'aya hanjin kubra ya shiga k'ugi...
MUJE ZUWA💃
TAKU HAR KULLUM
SIDIYA...✍️
[7/13, 1:13 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠
*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_*
(On ward together)
*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*
_BABI NA HUD'U_
*_____________________*
_Tsabar kad'uwa da mamaki ne ya cika kubra ,Wanda ya assassa mata tunani iri daban daban._ _A tunanin ta tunda take da Misbahu bai tab'a tunanin k'arin aure ba sama da shekara goma sha takwas makamancin wannan be tab'a tasowa ba se ayau kuma ayanzu kamar yadda boka RUBATSI ya sheda mata._
_Hajja Fati ce tayi k'arfin halin cewa_
"Tsafi ya da fa! Yanzu menene abun yi kenan?"