Sashe 29
Gidan Misbahu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Khaltum da idanuwan ta ya cika da hawaye tace "Kubra ba zama ya kawo ni ba. Ina so ki gaya mun ta yadda kika saka aka cire mun mahaifa ,da kuma lokacin da aka yi bansani ba ,Dan nasan ba ke ce za ki yi da kan ki ba ,saka wa za ki yi ayi."
Wani irin guntun murmushi kubra ta yi tare da cewa "Na fuskanci kin d'au zafi da yawa. Amma ga wannan kisha ko zaki ji sanyi a ran ki." Ta k'arasa maganan tare da mik'a mata ragowar lemun dake Kofi a kusa da ita.
Kau da kai Khaltum ta yi gefe tare da cewa "Ba na buqata. Ki amsa min tambaya ta kawai".
Baki kubra ta tab'e tare da cewa " Gaggawar me kike yi? Da kin kwantar da hankalin ki ma har d'akin ki zan zo in gaya miki yadda komai ya wakana. Khaltum ban so tsiya ya had'a mu. Ke kika ja wa kan ki. Dan naji lokacin da kike waya da wata qawar ki a qasar Germany cewa idan har kika samu da ma zaki kawar da ni. Ni ko se naga duk zaman amanar da nake dake Ashe ke ba da zuciya d'aya kike zauna dani ba. Daga wannan lokacin na shirya komai da wata qawata da ke aiki a babban asibitin Germany ,na baki wata k'waya me k'arfi kika sha Dan in d'auke miki hankali ,na kuma Nasara k'wayar ta yi miki cikin sauqi ,na d'auke ki cikin mota na kai ki asibitin na kuma fad'a musu yadda nake so ayi ,cikin minti talatin akayi komai aka gama. Satin mu d'aya a asibitin ba tare da kin sani ba sakamakon allurori da ake miki masu qarfin gaske. Kinji yadda na tsara komai. Ni Kubra kuma kowa yaci tuwo dani miya sha ,bana yafe wa duk Wanda na yadda dashi yake k'ok'arin cin Amanata. Idan akwai Wanda na kama ta in d'aga wa k'afa be wuce Hajja Fati ba ,nasan kinsan yadda take a wuri na ,amma taci Amanata yanzu haka na turo wa Mijin ta videon iskancin da tayi da babban aminin shi ,da duk wani shiri da suke yi na ganin sun raba shi da kujerar daya ke kai na sarauta. Na tabbata komai ya dagule mata kawo yanzu. Idan wannan ne ya kawo ki zaki iya tafiya..." Kubra ta fad'a tare da d'aukar kofin lemun nan ta kai bakin ta...
Da sauri ta janye kofin lemun daga bakin ta ,tare da shaqar iska Dan ta tabbatar da k'amshin da take ji.
"Wannan kamar warin gass nake ji?"" Kubra ta fad'a tare da waiga wa..
Khaltum dake shawaye tace "ba wai bane. Warin gas ki ke ji. Idan kinsan me za ki aikata to baki San me za'a aikata miki ba Kubra. Fad'an wasa shi ake yi wa matsaya ,amma fad'ar gaske kuwa kwana ake yi ana yi. Ni Khaltum jinjirar d'an tsako ce me kwarjini a idon d'an angulla. Gonar sama mai wuyar kai taki... Tabbas kin samu Nasara a karo na farko ,amma ina me baki albishir da cewa kin yi na farko kuma kin yi d'an Autan k'arshe. Ni ni kad'ai kika yi wa amma daga ke har 'ya'yan ki da kike magana akan su wannan ita ce ranar Ku ta k'arshe a duniya...
Kubra furzar da lemun dake bakin ta tayi tare da cewa " Me kike shirin aikata mana haka?"
"Kashe Ku Zan yi. Wannan warin gas d'in da kike ji ,tukunyar gas d'in ki ce na bud'e ,nasan zuwa yanzu ya karad'e ko ina dako ina. Na fi son ayi mutuwar kasko wallahi d'a kwance uwa kwance. Kamar yadda na d'au alwashi ,nima nafi son in rasa rai na matuqar buri na ze ciki..."
Cike da tsaro kubra ta mik'e tsaye tana zaro ido tare da cewa "kin kuwa San me kike yi Khaltum? Rai fa zaki kashe? Menene amfanin hakan? Wallahi Allah baze bar ki ba. Wallahi wuta zaki je"
"Dalla malama dakata!!" Khaltum ta katse ta, sannan taci gaba da cewa "ke har kinsan Allah. Nasan ke abunda kika aikata mun aljannah zaki ce tunda a gidan uban ki ake raba ta. Muguwa kawai me zuciyar 'yan wuta. Nafi son tun a duniya wutar Allah ta fara kama ki kafin kije ki taradda babban azabar ki."
Jin haka yasa kubra rugawa ta gudu ta nufe hanyar fita ,tare da ihun a taimake ta. Se dai bata yi sa'a ba ,dan duk k'ofar data je a kulle gam take jin ta. Ganin haka yasa ta saduda ,ta dawo ta zube k'asa kan guiwar ta kusa da Khaltum tana rok'on ta akan tayi hakuri tayi mata rai ,wallahi ba zata sake ba.
Khaltum na kuka tace "Lokacin Neman afuwa ya k'are miki kubra. Yanzu lokacin girbar abunda kika shuka ne. " tana gama fad'in haka ta kunna ashanar dake hannun ta ,kubra na ihu tana Neman taimako haka Khaltum ta cilla wutar ashanan nan.
Nan take wuta ta fara ci ,ko ina da ko ina ya ka ma a lokaci d'aya. Wuta ne yake ce a sashen kubra sosai. Nan danan hankalin mutanen ciki Dana wajen gida ya dawo nan.
Dummmm! Kake ji kamar ta ya ta fashe. Wannan k'arar ne yasa daddy dake garden ya ankaro. Da sauri ya taso Dan ganin me ke faruwa. Kafin ya k'araso sai mutane ya gani suna shigowa ,ga gate an bud'e motar kashe wuta na shigo wa. Ai da gudu shima ya isa.
A hankali hayaqi ya fara zagaye d'akin qasa da su haajar ke kwance ,tari suka fara ita da haseena ,Suxee dake band'aki da sauri ta fito Dan ganin meke faruwa. Aifa nan taga hayaqi ,ko gaban ta bata gani sosai ,tari ta fara yi sosai. Tana k'ok'arin kiran sunan Haajar Dana suxee...
Da lalube har ta isa bakin gadon, ta lalubo hannun Haajar ,ba tare da tana ganin gaban ta ba saboda hayaqin daya yi yawa a d'akin. K'ok'arin kiran junan su suke yi ,yayin da mutanen waje ke k'ok'arin fasa k'ofar Dan shiga ceton su.
Daddy se fad'in yake " 'ya'yana na ciki Ku taimake ni,,,Ku taimake ni 'ya'ya na. Wannan Wani irin musiba ba ne??? A karo na farko dukiya ta yanzu kuma 'ya'yana... Na shiga uku ni MISBAHU na ga ta kaina...
Ihun Sunan Haajar ya fara yi kafin ya shiga kiran sunayen su suxee...
A wannan karon daddy kusan zautuwa yayi. Dan yana ji yana gani wuta na ci ga 'ya'yan shi a ciki. K'arshe fad'a wa yayi da shi aka yi ta k'ok'arin k'ofar baya. Amma ba alamun k'ofar zata bud'e...
MUJE ZUWA💃
TAKU HAR KULLUM
SIDIYA...✍️
[8/15, 7:27 AM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠
*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_*
(On ward together)
*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*
_BABI NA TALATIN DA TARA_
*_________________________________*
_Da k'yar masu k'ok'arin ceton rayuwar iyalin daddy suka yi nasarar fasa k'ofar baya, a lokacin har wutar ta fara ruzga gini. Sama suka nufa 'kofar da suke iya jiyo ihun Kubra. Sun yi iya bakin k'ok'arin su wajen bud'e k'ofar amma ina hakan bai yiwu ba. Dan khaltum ta datse ko ina da ko ina ,bayan makulli sai da ta saka hadda mab'allin kwad'o ,hakan yayi tasiri da kuma wutar dake ci a wannan lokacin. Ganin da suka yi wutar sai dad'a ruruwa take yi ga shi basu iya Ciro ko da mutum d'aya ba ,yasa suka bar wannan k'ofar Dan dole, suka koma ta k'ofar da su Haajar ke ciki._
Sai da suka yi da gaske kafin suka yi nasarar b'alle k'ofar. Da taimakon Allah suka iya Ciro mutum biyu daga ciki da ba iya tantance ko su waye ba ,sakamakon rud'ani da kuma yanayin tashin hankalin da ake ciki...
Ana fito wa dasu daidai lokacin da motar asibiti ta k'arasa. Kai tsaye asibiti aka wuce dasu Dan ba su agajin gaggawa. Sannan suka koma a karo na biyu dan sake ceto sauran mutanen da ke ciki. Sai dai ina ,,,a wannan karon ba hanyar shiga, Dan kuwa wutar ta kama ko ina da ko ina. Wani daga cikin su me suna Auwal ne ya ke k'ok'arin ganin ko ta halin yaya ya kutsa dan ceton rai. A daidai lokacin da ya kai jiki ze shiga ciki ,wata Katanga dake famar ci da wuta ta ruguzo masa sai akan k'afa, da sauri sauran mutanen dake wajen suka k'araso suka d'auke shi. Yayin da masu kashe wuta wato (fire service) ke iya k'ok'arin su na ganin sun kashe wutar...
Su na ji su na gani haka wuta taci gaba da ci. Jim kad'an suka jiyo wani k'ara tussss ,alamar kayan cikin mutum ya fashe. Duk Wanda ke wurin sai da ya razana ,wasu daga ciki har zubarda k'walla suke yi dan tsabar tausayi. Ba jima wa suka sake jiyo irin wannan sautin alamar kayan cikin wani ya sake fashewa. Cike da gigita daddy yayi kukan kura yana so ya fad'a ciki ,yana fad'in "rayukan 'ya'yana!! Allah ka taimake ni!!! Ku ban ni in shiga in ciro yarana! Kuna kallo wuta na cin iyalina!!!" Haka daddy ya dinga sambatu iri daban-daban. Kusan duk wanda ke wurin sai da ya tausaya mass. K'arar sautin fashewar kayan cikin mutum suka sake jiyo wa a karo na uku. A wannan karon daddy yanke jiki yayi ya fad'i, sai da aka kwashe shi a k'asa sumamme se asibiti...
Wannan al-amari ba kad'an ba yayi masifar tayar wa mutane da hankali. Har kusan yamma kafin aka samu nasarar kashe wutar da ke ciki. Dak'yar aka yi nasarar zaqulo gawawwakin su ,dan kusan sun k'one qurmusus. A irin qonewar da su ka yi ,ba na tunanin ko rayuwa suka yi za su yi wani amfani a duniya ,mutuwar dai itace Hutu a gare su...
Gawar mutum uku aka fitar ,Wanda ba'a iya tantance su waye da waye ba. Nan da nan gari ya d'auka. Hajj jamil shine Wanda yayi ruwa yayi tsaki akan mamatan. Washe gari da safe aka sallata gawawwakin aka kai su gidan su na gaskiya. A nan sai dai muce Allah ya jiqan wa'ayanda suka Riga mu gidan gaskiya...
Wani irin guntun murmushi kubra ta yi tare da cewa "Na fuskanci kin d'au zafi da yawa. Amma ga wannan kisha ko zaki ji sanyi a ran ki." Ta k'arasa maganan tare da mik'a mata ragowar lemun dake Kofi a kusa da ita.
Kau da kai Khaltum ta yi gefe tare da cewa "Ba na buqata. Ki amsa min tambaya ta kawai".
Baki kubra ta tab'e tare da cewa " Gaggawar me kike yi? Da kin kwantar da hankalin ki ma har d'akin ki zan zo in gaya miki yadda komai ya wakana. Khaltum ban so tsiya ya had'a mu. Ke kika ja wa kan ki. Dan naji lokacin da kike waya da wata qawar ki a qasar Germany cewa idan har kika samu da ma zaki kawar da ni. Ni ko se naga duk zaman amanar da nake dake Ashe ke ba da zuciya d'aya kike zauna dani ba. Daga wannan lokacin na shirya komai da wata qawata da ke aiki a babban asibitin Germany ,na baki wata k'waya me k'arfi kika sha Dan in d'auke miki hankali ,na kuma Nasara k'wayar ta yi miki cikin sauqi ,na d'auke ki cikin mota na kai ki asibitin na kuma fad'a musu yadda nake so ayi ,cikin minti talatin akayi komai aka gama. Satin mu d'aya a asibitin ba tare da kin sani ba sakamakon allurori da ake miki masu qarfin gaske. Kinji yadda na tsara komai. Ni Kubra kuma kowa yaci tuwo dani miya sha ,bana yafe wa duk Wanda na yadda dashi yake k'ok'arin cin Amanata. Idan akwai Wanda na kama ta in d'aga wa k'afa be wuce Hajja Fati ba ,nasan kinsan yadda take a wuri na ,amma taci Amanata yanzu haka na turo wa Mijin ta videon iskancin da tayi da babban aminin shi ,da duk wani shiri da suke yi na ganin sun raba shi da kujerar daya ke kai na sarauta. Na tabbata komai ya dagule mata kawo yanzu. Idan wannan ne ya kawo ki zaki iya tafiya..." Kubra ta fad'a tare da d'aukar kofin lemun nan ta kai bakin ta...
Da sauri ta janye kofin lemun daga bakin ta ,tare da shaqar iska Dan ta tabbatar da k'amshin da take ji.
"Wannan kamar warin gass nake ji?"" Kubra ta fad'a tare da waiga wa..
Khaltum dake shawaye tace "ba wai bane. Warin gas ki ke ji. Idan kinsan me za ki aikata to baki San me za'a aikata miki ba Kubra. Fad'an wasa shi ake yi wa matsaya ,amma fad'ar gaske kuwa kwana ake yi ana yi. Ni Khaltum jinjirar d'an tsako ce me kwarjini a idon d'an angulla. Gonar sama mai wuyar kai taki... Tabbas kin samu Nasara a karo na farko ,amma ina me baki albishir da cewa kin yi na farko kuma kin yi d'an Autan k'arshe. Ni ni kad'ai kika yi wa amma daga ke har 'ya'yan ki da kike magana akan su wannan ita ce ranar Ku ta k'arshe a duniya...
Kubra furzar da lemun dake bakin ta tayi tare da cewa " Me kike shirin aikata mana haka?"
"Kashe Ku Zan yi. Wannan warin gas d'in da kike ji ,tukunyar gas d'in ki ce na bud'e ,nasan zuwa yanzu ya karad'e ko ina dako ina. Na fi son ayi mutuwar kasko wallahi d'a kwance uwa kwance. Kamar yadda na d'au alwashi ,nima nafi son in rasa rai na matuqar buri na ze ciki..."
Cike da tsaro kubra ta mik'e tsaye tana zaro ido tare da cewa "kin kuwa San me kike yi Khaltum? Rai fa zaki kashe? Menene amfanin hakan? Wallahi Allah baze bar ki ba. Wallahi wuta zaki je"
"Dalla malama dakata!!" Khaltum ta katse ta, sannan taci gaba da cewa "ke har kinsan Allah. Nasan ke abunda kika aikata mun aljannah zaki ce tunda a gidan uban ki ake raba ta. Muguwa kawai me zuciyar 'yan wuta. Nafi son tun a duniya wutar Allah ta fara kama ki kafin kije ki taradda babban azabar ki."
Jin haka yasa kubra rugawa ta gudu ta nufe hanyar fita ,tare da ihun a taimake ta. Se dai bata yi sa'a ba ,dan duk k'ofar data je a kulle gam take jin ta. Ganin haka yasa ta saduda ,ta dawo ta zube k'asa kan guiwar ta kusa da Khaltum tana rok'on ta akan tayi hakuri tayi mata rai ,wallahi ba zata sake ba.
Khaltum na kuka tace "Lokacin Neman afuwa ya k'are miki kubra. Yanzu lokacin girbar abunda kika shuka ne. " tana gama fad'in haka ta kunna ashanar dake hannun ta ,kubra na ihu tana Neman taimako haka Khaltum ta cilla wutar ashanan nan.
Nan take wuta ta fara ci ,ko ina da ko ina ya ka ma a lokaci d'aya. Wuta ne yake ce a sashen kubra sosai. Nan danan hankalin mutanen ciki Dana wajen gida ya dawo nan.
Dummmm! Kake ji kamar ta ya ta fashe. Wannan k'arar ne yasa daddy dake garden ya ankaro. Da sauri ya taso Dan ganin me ke faruwa. Kafin ya k'araso sai mutane ya gani suna shigowa ,ga gate an bud'e motar kashe wuta na shigo wa. Ai da gudu shima ya isa.
A hankali hayaqi ya fara zagaye d'akin qasa da su haajar ke kwance ,tari suka fara ita da haseena ,Suxee dake band'aki da sauri ta fito Dan ganin meke faruwa. Aifa nan taga hayaqi ,ko gaban ta bata gani sosai ,tari ta fara yi sosai. Tana k'ok'arin kiran sunan Haajar Dana suxee...
Da lalube har ta isa bakin gadon, ta lalubo hannun Haajar ,ba tare da tana ganin gaban ta ba saboda hayaqin daya yi yawa a d'akin. K'ok'arin kiran junan su suke yi ,yayin da mutanen waje ke k'ok'arin fasa k'ofar Dan shiga ceton su.
Daddy se fad'in yake " 'ya'yana na ciki Ku taimake ni,,,Ku taimake ni 'ya'ya na. Wannan Wani irin musiba ba ne??? A karo na farko dukiya ta yanzu kuma 'ya'yana... Na shiga uku ni MISBAHU na ga ta kaina...
Ihun Sunan Haajar ya fara yi kafin ya shiga kiran sunayen su suxee...
A wannan karon daddy kusan zautuwa yayi. Dan yana ji yana gani wuta na ci ga 'ya'yan shi a ciki. K'arshe fad'a wa yayi da shi aka yi ta k'ok'arin k'ofar baya. Amma ba alamun k'ofar zata bud'e...
MUJE ZUWA💃
TAKU HAR KULLUM
SIDIYA...✍️
[8/15, 7:27 AM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠
*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_*
(On ward together)
*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*
_BABI NA TALATIN DA TARA_
*_________________________________*
_Da k'yar masu k'ok'arin ceton rayuwar iyalin daddy suka yi nasarar fasa k'ofar baya, a lokacin har wutar ta fara ruzga gini. Sama suka nufa 'kofar da suke iya jiyo ihun Kubra. Sun yi iya bakin k'ok'arin su wajen bud'e k'ofar amma ina hakan bai yiwu ba. Dan khaltum ta datse ko ina da ko ina ,bayan makulli sai da ta saka hadda mab'allin kwad'o ,hakan yayi tasiri da kuma wutar dake ci a wannan lokacin. Ganin da suka yi wutar sai dad'a ruruwa take yi ga shi basu iya Ciro ko da mutum d'aya ba ,yasa suka bar wannan k'ofar Dan dole, suka koma ta k'ofar da su Haajar ke ciki._
Sai da suka yi da gaske kafin suka yi nasarar b'alle k'ofar. Da taimakon Allah suka iya Ciro mutum biyu daga ciki da ba iya tantance ko su waye ba ,sakamakon rud'ani da kuma yanayin tashin hankalin da ake ciki...
Ana fito wa dasu daidai lokacin da motar asibiti ta k'arasa. Kai tsaye asibiti aka wuce dasu Dan ba su agajin gaggawa. Sannan suka koma a karo na biyu dan sake ceto sauran mutanen da ke ciki. Sai dai ina ,,,a wannan karon ba hanyar shiga, Dan kuwa wutar ta kama ko ina da ko ina. Wani daga cikin su me suna Auwal ne ya ke k'ok'arin ganin ko ta halin yaya ya kutsa dan ceton rai. A daidai lokacin da ya kai jiki ze shiga ciki ,wata Katanga dake famar ci da wuta ta ruguzo masa sai akan k'afa, da sauri sauran mutanen dake wajen suka k'araso suka d'auke shi. Yayin da masu kashe wuta wato (fire service) ke iya k'ok'arin su na ganin sun kashe wutar...
Su na ji su na gani haka wuta taci gaba da ci. Jim kad'an suka jiyo wani k'ara tussss ,alamar kayan cikin mutum ya fashe. Duk Wanda ke wurin sai da ya razana ,wasu daga ciki har zubarda k'walla suke yi dan tsabar tausayi. Ba jima wa suka sake jiyo irin wannan sautin alamar kayan cikin wani ya sake fashewa. Cike da gigita daddy yayi kukan kura yana so ya fad'a ciki ,yana fad'in "rayukan 'ya'yana!! Allah ka taimake ni!!! Ku ban ni in shiga in ciro yarana! Kuna kallo wuta na cin iyalina!!!" Haka daddy ya dinga sambatu iri daban-daban. Kusan duk wanda ke wurin sai da ya tausaya mass. K'arar sautin fashewar kayan cikin mutum suka sake jiyo wa a karo na uku. A wannan karon daddy yanke jiki yayi ya fad'i, sai da aka kwashe shi a k'asa sumamme se asibiti...
Wannan al-amari ba kad'an ba yayi masifar tayar wa mutane da hankali. Har kusan yamma kafin aka samu nasarar kashe wutar da ke ciki. Dak'yar aka yi nasarar zaqulo gawawwakin su ,dan kusan sun k'one qurmusus. A irin qonewar da su ka yi ,ba na tunanin ko rayuwa suka yi za su yi wani amfani a duniya ,mutuwar dai itace Hutu a gare su...
Gawar mutum uku aka fitar ,Wanda ba'a iya tantance su waye da waye ba. Nan da nan gari ya d'auka. Hajj jamil shine Wanda yayi ruwa yayi tsaki akan mamatan. Washe gari da safe aka sallata gawawwakin aka kai su gidan su na gaskiya. A nan sai dai muce Allah ya jiqan wa'ayanda suka Riga mu gidan gaskiya...