Sashe 38
Gidan Misbahu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Karatun qurni Dr. Imam ya fara yi na Neman yaddar Allah kan aikin da ze yi. Haajar sai wani dariya ta ke yi tana zage-zage. Wani kundi Dr. Imam ya d'auko ya bud'e. Haajar na ganin shi ta fara ihu tana kururuwa. Duk Wanda ke wurin sai da ya zubar mata da hawaye. Wani magani Dr. Imam ya je ya bud'e bakin ta ya zuba mata. Sannan ya doki tsakiyar kan ta da qarfi tare da take qafar ta na hagu. Shak'e mata wuya ya yi a lokaci d'aya yana ci gaba da karanto alqur'ani. Shak'ar da Ya yiwa Haajar kowa sai da ya d'auka mutuwa za ta yi a yadda take kakari. Zuwa can sai ga shi tayi wani irin amai baqiqirin na sare saren zare. Kundin nan Dr. Imam ya ajiye a gaban ta ,ya danna yatsanta a ciki. Nan da nan hannun ya kama da wuta. Wani haske ne ya mamaye inda Haajar d'in ke tsaye. Can sai ga Haajar ta fad'i a gefe ga kuma wata siffa mai kama da Kubra sak an fitar a gefe. Duk Wanda ke wurin sai da ya girgiza. Nan Dr. Imam ya shiga yi wa wannan sifa tambayoyi ita kuma tana bashi amsa cikin wani yare Mara dad'in saurare da ba Wanda ke iya gane mai take cewa sai shi kad'ai. Hannun ta d'aya ya dad'a dannawa a cikin kundin, tana ihu tana qarawa a haka dai da jikin ta ya k'one gaba d'aya, daga k'arshe sai ga wani haske na bartsi. Daga nan ta watse. Dr. Imam ya yi hamdala tare da komawa ya zauna. Wani magani ya had'a San nan ya dawo kan Haajar da ke kwance kamar gawa. Tsakiyar kanta ya bud'e ya zuba wani magani na gari sannan ya fara yi mata yayyafi da wani ruwan magani da ke cikin kwalba fari. Ya dad'e a zaune kusa da ita yana karanto mata ayoyin waraka daga ubangiji. Kusan mintuna ashirin sai ga Haajar ta mik'e kamar ba ita ba tare da yin salati. Mamaki tayi yadda taga an tattaru akan ta. Ga mahaifin ta zaune kusa da ita. Tace "Me ke faruwa ne? Dan Allah Ku gaya mun"
Ruwan zamzam da aka yi wa addu'o'in shifa mahaifin ta ya d'auka ya bata. Da ido ta ni shi alamar mai zata yi da shi yace "ki karb'a ki sha" ba musu ta karb'a ta shanye tas.. Sannan yace a bata d'ankwali ta d'aura a kanta.
Wani zufa ne ya shiga tsatsafo wa Haajar ta ko ina ,sharkaf ta yi kamar wacce aka tsamo da teku. Nan Dr. Imam ya ce a kunna mata na'urar sanyi Wanda kafin ya fara aiki ya ce a kashe. Hajiya da kanta ta tashi ta kunna panka da kuma na'urar sanyi ,nan da nan iska da sanyi ya karad'e ko ina a parlourn. Sai wani ajiyar zuciya Haajar d'in ke saukewa kamar wacce tayi gudun tsere. Shima Dr. Imam ajiyar zuciyar ya sauke tare da zaro k'yallen goge zufa ya goge zufan fuskar shi ,sannan ya soma da hamdala tare da yiwa annabi salati, kafin ya d'ora da cewa "Dukkan godia ya tabbata ga Allah. Na San dikkan Ku kun ga abunda ya faru a yanzu ,za kuma kuyi mamakin wani irin nau'in al-amara ne wannan?" Hajiya tace "wannan gaskiya ne" Dr. Imam yaci gaba da cewa "Ciwon nan da Haajar d'in ake ta sanya mata jini alal haqiqa ba ita ake sanya wa jinin ba ,saboda masu shanye shi daban. Idan kuma da za'a yi shekarun annabi Nuhu A.S ana sanya mata jini ko makamancin wannan ba za Ku tab'a ganin ci gaba ba, sai dai ma daga k'arshe Ku rasata ma'ana ta mutu ,saboda jinin jikin ta da ake zuqa daga wani wurin daban. Wannan siffar da na fiddo daga jikin ta nasan kunsan ta?" Hajiya tace "shakka babu wannan Abokiyar zaman Haajar ce data mutu a gobarar da akayi a gidan ba da jimawa ba". Dr. Imam yace " to ta mutu ne amma kuruwar ta na nan na yawo. Ta kuma lashi takobin hana wannan ahali zaman lafiya. To amma da yake Allah ke yi ba wanin shi ba. Wannan kundi da kuka gani ,kundi ne na k'ona rauhanai. Saboda haka na nayi nasarar k'ona kuruwar wannan baiwar Allah da ke cikin jikin Haajar. Ba'anan matsalar take ba. Wannan ba ita bace asalin ruhin. Kuma muddin ba'a Nema ta asalin an k'ona ta ba ,to fa akwai gagaruwar matsala. Saboda haka na yi mata tambayoyi tun kafin na qona ta. Ta kuma gayamin inda za'a samu wannan babban kundin ,da an d'auko shi aka k'ona komai zai zama tarihi da izinin Allah." Wani irin ajiyar zuciya Hajiya ta sauke tare da cewa "To yanzu a ina za'a samu wannan kundi malam?" Sunan wani daji Dr. Imam ya fad'a mai matuqar hatsarin gaske. Wanda ba lallai ka shiga wannan dajin ka dawo ba ,idan kuwa ka dawo to ba shakka zaka iya tab'uwar hankali. Ya kuma shaida musu akan lallai lallai Haajar d'in ake buqatar da ta je da kanta. "Kai ina!" Inji daddy "bazan tab'a barin Haajar ta je wannan wurin ba". Dr. Imam yace " Wannan itace mafitar mu ta k'arshe ,idan ba haka kuruwar zata dawo ,kuma idan ta dawo to dawowar bazai wa kowa kyau ba". Shiru kowa ya yi yana jimanta al-amarin. Kafin Dr. Imam yaci gaba da cewa "Zan shirya komai a Daren yau insha Allahu rabbi." Daga haka yace a rufe sashen Haajar d'in kowa da kowa ya koma sashen Hajiya. Haka kuwa aka yi.
Misalin k'arfe sha biyu na dare babu Wanda ya iya runtsawa banda suxee da auta da basu San wainar da ake toya wa ba. Wata farar mata ce ta shigo su Dr. Na zaune. Dr.imam yace ta zauna. Bayan ta zauna suka tattauna da shi cikin harshen larabci. Suna gama magana daddy yace wa Haajar "ki yi wa baquwa ta rakiya". Ba musu Haajar ta bi bayan wannan farar mata ,ita kuma Matar ta rik'e hannun Haajar suka fita.
Bayan sun fita daddy ya dubi Dr. Imam tare da cewa "Wannan wacece da suka fita da Haajar?" Gyara zama Dr. Imam ya yi tare da cewa "Wannan da kuke gani ba mutum bace aljana ce, Sunan ta maimunatu. Maimunata aljanar zuri'a ta ce ta amana." Cike da tashin hankali daddy yace "ina kuma zata kai Haajar?" Dr. Imam yace "dajin da fad'a muku za'a d'auko wannan kundin. Da taimakon Allah da taimakon maimunatu Haajar zata kai ga wannan kundi". A gigice daddy ya fita da gudu yana kiran suna Haajar! Dr. Imam yace " da'ace zaka dawo ka kwantar da hankalin ka da ya fiye maka kwanciyar hankali. Dan babu Haajar take so a wurin mu yanzu sama da addu'a." Kuka daddy ya fashe da shi ya na mai ci gaba da kiran sunan Haajar d'in babu qaqqautawa Sai da ya bawa kowa tausayi. Aiki Dr. Imam ya shiga yi tuk'uru. Dan kusan saida ya yi saukar alqur'ani. Su Hajiya kuwa alwala suka yi suka duqufa sallah har garin Allah ya waye. Banda daddy dake zaune cunkus kamar wani Mara lakka ,tun yana kukan mai sauti har ya koma sai dai hawaye kawai ke yi masa zuba.
MUJE ZUWA💃
TAKU HAR KULLUM
SIDIYA...✍️
[8/24, 12:09 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠
*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_*
(On ward together)
*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*
_BABI NA ARBA'IN DA SHIDA_
*____________________________*
Har wuraren shida na safe babu Haajar babu alamar ta. Gaba d'aya ahalin gidan sun shiga damuwa ainun. Shida da rabi, Dr. Imam ya fito wajen sashen da suke ciki. A bakin k'ofa ya ga Haajar d'in a yashe ta yi wani irin baqi ta sauya kala kamar ba ita ba. Koma wa ciki ya yi ya yiwa daddy magana akan yazo ya d'auko matar shi. Da sauri daddy ya miqe yana fad'in "Ina take?" Ganin kwance a qasa a k'ofar shiga ya sa yayo saurin yowa kanta ba shiri ,ya shiga jijjiga ta yana kiran sunan ta. Dr. Imam yace "ka shigo da ita ciki". Daga haka ya yi shigewar shi. Ba shiri daddy ya sunkuci Haajar d'in ya bi bayan Dr. Imam. A tsakar d'aki Dr. Imam yace ya ajiye ta. D'ankwalin dake k'ulle a jikin zanin ta ya kwanto tare da warware k'ullin ya furta " Alhamdulillahi! Wannan shi ne kundin da ake da buqata". K'ok'arin k'ona kundin ya shige yi da ayoyin Allah. Nan take wannan kundin ya ka ma da wuta ,wani bak'in hayak'i na tashi. Sai da ya cinye tas sannan ya yiwa Haajar d'in yayyafin ruwan magani. A zabure ta tashi zata ruga a guje ,ya rik'o ta, Tare da ci gaba da karanto mata ayoyin waraka daga ubangiji. Sambatu Haajar d'in ta shiga yi kamar wata zararriya. Addu'o'i sosai Dr. Imam ya dinga yi mata, daga haka wani irin nannauyan bacci ya yi awon gaba da ita. Ya sake furta "Alhamdulillahi! Sauqi ya samu daga Allah! Yanzu ta samu bacci. Sannan wannan baccin idan zata kai sati d'aya tana yin sa kar a tashe ta ,sai lokacin da ta farka da kanta. Kar kuma Ku damu, babu abunda zai sake faruwa da izinin Allah. Za kuma Ku iya ci gaba da sabgogin ku". Hajiya tace " Insha Allahu za mu yi k'ok'arin kiyaye wa. Sannu da aiki malam, Allah ya saka maka da alkhairi. Da ba Dan kazo ba bansan yadda za mu yi da wannan rikitaccen al-amarin ba mai kama da al-mara. Duk da cewar Haajar 'yar ka ce ,amma mu ka yi wa wannan taimakon, Dan Haajar wata jigo ce daga cikin wannan ahali da ba zamu tab'a qaunatar abunda zai same ta na rashin dad'i ba. Mun gode sosai". Dr. Imam yace "Allah ya tsare gaba".
Ruwan zamzam da aka yi wa addu'o'in shifa mahaifin ta ya d'auka ya bata. Da ido ta ni shi alamar mai zata yi da shi yace "ki karb'a ki sha" ba musu ta karb'a ta shanye tas.. Sannan yace a bata d'ankwali ta d'aura a kanta.
Wani zufa ne ya shiga tsatsafo wa Haajar ta ko ina ,sharkaf ta yi kamar wacce aka tsamo da teku. Nan Dr. Imam ya ce a kunna mata na'urar sanyi Wanda kafin ya fara aiki ya ce a kashe. Hajiya da kanta ta tashi ta kunna panka da kuma na'urar sanyi ,nan da nan iska da sanyi ya karad'e ko ina a parlourn. Sai wani ajiyar zuciya Haajar d'in ke saukewa kamar wacce tayi gudun tsere. Shima Dr. Imam ajiyar zuciyar ya sauke tare da zaro k'yallen goge zufa ya goge zufan fuskar shi ,sannan ya soma da hamdala tare da yiwa annabi salati, kafin ya d'ora da cewa "Dukkan godia ya tabbata ga Allah. Na San dikkan Ku kun ga abunda ya faru a yanzu ,za kuma kuyi mamakin wani irin nau'in al-amara ne wannan?" Hajiya tace "wannan gaskiya ne" Dr. Imam yaci gaba da cewa "Ciwon nan da Haajar d'in ake ta sanya mata jini alal haqiqa ba ita ake sanya wa jinin ba ,saboda masu shanye shi daban. Idan kuma da za'a yi shekarun annabi Nuhu A.S ana sanya mata jini ko makamancin wannan ba za Ku tab'a ganin ci gaba ba, sai dai ma daga k'arshe Ku rasata ma'ana ta mutu ,saboda jinin jikin ta da ake zuqa daga wani wurin daban. Wannan siffar da na fiddo daga jikin ta nasan kunsan ta?" Hajiya tace "shakka babu wannan Abokiyar zaman Haajar ce data mutu a gobarar da akayi a gidan ba da jimawa ba". Dr. Imam yace " to ta mutu ne amma kuruwar ta na nan na yawo. Ta kuma lashi takobin hana wannan ahali zaman lafiya. To amma da yake Allah ke yi ba wanin shi ba. Wannan kundi da kuka gani ,kundi ne na k'ona rauhanai. Saboda haka na nayi nasarar k'ona kuruwar wannan baiwar Allah da ke cikin jikin Haajar. Ba'anan matsalar take ba. Wannan ba ita bace asalin ruhin. Kuma muddin ba'a Nema ta asalin an k'ona ta ba ,to fa akwai gagaruwar matsala. Saboda haka na yi mata tambayoyi tun kafin na qona ta. Ta kuma gayamin inda za'a samu wannan babban kundin ,da an d'auko shi aka k'ona komai zai zama tarihi da izinin Allah." Wani irin ajiyar zuciya Hajiya ta sauke tare da cewa "To yanzu a ina za'a samu wannan kundi malam?" Sunan wani daji Dr. Imam ya fad'a mai matuqar hatsarin gaske. Wanda ba lallai ka shiga wannan dajin ka dawo ba ,idan kuwa ka dawo to ba shakka zaka iya tab'uwar hankali. Ya kuma shaida musu akan lallai lallai Haajar d'in ake buqatar da ta je da kanta. "Kai ina!" Inji daddy "bazan tab'a barin Haajar ta je wannan wurin ba". Dr. Imam yace " Wannan itace mafitar mu ta k'arshe ,idan ba haka kuruwar zata dawo ,kuma idan ta dawo to dawowar bazai wa kowa kyau ba". Shiru kowa ya yi yana jimanta al-amarin. Kafin Dr. Imam yaci gaba da cewa "Zan shirya komai a Daren yau insha Allahu rabbi." Daga haka yace a rufe sashen Haajar d'in kowa da kowa ya koma sashen Hajiya. Haka kuwa aka yi.
Misalin k'arfe sha biyu na dare babu Wanda ya iya runtsawa banda suxee da auta da basu San wainar da ake toya wa ba. Wata farar mata ce ta shigo su Dr. Na zaune. Dr.imam yace ta zauna. Bayan ta zauna suka tattauna da shi cikin harshen larabci. Suna gama magana daddy yace wa Haajar "ki yi wa baquwa ta rakiya". Ba musu Haajar ta bi bayan wannan farar mata ,ita kuma Matar ta rik'e hannun Haajar suka fita.
Bayan sun fita daddy ya dubi Dr. Imam tare da cewa "Wannan wacece da suka fita da Haajar?" Gyara zama Dr. Imam ya yi tare da cewa "Wannan da kuke gani ba mutum bace aljana ce, Sunan ta maimunatu. Maimunata aljanar zuri'a ta ce ta amana." Cike da tashin hankali daddy yace "ina kuma zata kai Haajar?" Dr. Imam yace "dajin da fad'a muku za'a d'auko wannan kundin. Da taimakon Allah da taimakon maimunatu Haajar zata kai ga wannan kundi". A gigice daddy ya fita da gudu yana kiran suna Haajar! Dr. Imam yace " da'ace zaka dawo ka kwantar da hankalin ka da ya fiye maka kwanciyar hankali. Dan babu Haajar take so a wurin mu yanzu sama da addu'a." Kuka daddy ya fashe da shi ya na mai ci gaba da kiran sunan Haajar d'in babu qaqqautawa Sai da ya bawa kowa tausayi. Aiki Dr. Imam ya shiga yi tuk'uru. Dan kusan saida ya yi saukar alqur'ani. Su Hajiya kuwa alwala suka yi suka duqufa sallah har garin Allah ya waye. Banda daddy dake zaune cunkus kamar wani Mara lakka ,tun yana kukan mai sauti har ya koma sai dai hawaye kawai ke yi masa zuba.
MUJE ZUWA💃
TAKU HAR KULLUM
SIDIYA...✍️
[8/24, 12:09 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠
*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_*
(On ward together)
*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*
_BABI NA ARBA'IN DA SHIDA_
*____________________________*
Har wuraren shida na safe babu Haajar babu alamar ta. Gaba d'aya ahalin gidan sun shiga damuwa ainun. Shida da rabi, Dr. Imam ya fito wajen sashen da suke ciki. A bakin k'ofa ya ga Haajar d'in a yashe ta yi wani irin baqi ta sauya kala kamar ba ita ba. Koma wa ciki ya yi ya yiwa daddy magana akan yazo ya d'auko matar shi. Da sauri daddy ya miqe yana fad'in "Ina take?" Ganin kwance a qasa a k'ofar shiga ya sa yayo saurin yowa kanta ba shiri ,ya shiga jijjiga ta yana kiran sunan ta. Dr. Imam yace "ka shigo da ita ciki". Daga haka ya yi shigewar shi. Ba shiri daddy ya sunkuci Haajar d'in ya bi bayan Dr. Imam. A tsakar d'aki Dr. Imam yace ya ajiye ta. D'ankwalin dake k'ulle a jikin zanin ta ya kwanto tare da warware k'ullin ya furta " Alhamdulillahi! Wannan shi ne kundin da ake da buqata". K'ok'arin k'ona kundin ya shige yi da ayoyin Allah. Nan take wannan kundin ya ka ma da wuta ,wani bak'in hayak'i na tashi. Sai da ya cinye tas sannan ya yiwa Haajar d'in yayyafin ruwan magani. A zabure ta tashi zata ruga a guje ,ya rik'o ta, Tare da ci gaba da karanto mata ayoyin waraka daga ubangiji. Sambatu Haajar d'in ta shiga yi kamar wata zararriya. Addu'o'i sosai Dr. Imam ya dinga yi mata, daga haka wani irin nannauyan bacci ya yi awon gaba da ita. Ya sake furta "Alhamdulillahi! Sauqi ya samu daga Allah! Yanzu ta samu bacci. Sannan wannan baccin idan zata kai sati d'aya tana yin sa kar a tashe ta ,sai lokacin da ta farka da kanta. Kar kuma Ku damu, babu abunda zai sake faruwa da izinin Allah. Za kuma Ku iya ci gaba da sabgogin ku". Hajiya tace " Insha Allahu za mu yi k'ok'arin kiyaye wa. Sannu da aiki malam, Allah ya saka maka da alkhairi. Da ba Dan kazo ba bansan yadda za mu yi da wannan rikitaccen al-amarin ba mai kama da al-mara. Duk da cewar Haajar 'yar ka ce ,amma mu ka yi wa wannan taimakon, Dan Haajar wata jigo ce daga cikin wannan ahali da ba zamu tab'a qaunatar abunda zai same ta na rashin dad'i ba. Mun gode sosai". Dr. Imam yace "Allah ya tsare gaba".