Sashe 2
Fini A Uba In Fiki A Miji Complete Hausa Novel · about 8 min read
PAGE 2
Tun da Allah ya dawo da Zainab gidan nan bata kara sanin menene farin ciki ba.
Da babanta ya je dauko ta daga hannun mahaifiyarta da cin hancin karatu mai nagarta ya rarrashe ta ya kuma dakko ta da alkawarin haka. Amma ga shi nan a sati da kyar take samu ta je sau biyu ko sau uku. Saboda Mammy ta kafa mata dokar ita zata dinga gyara dakinsu bayan sun tashi san nan ta jira kowa yayi wanka ta wanke bandakin su.
Hakan ya sanya ta ke zama ta karshe wajen shiryawa. Kuma da Abbansu zai fara fada a kan cewa me ya hana ta shirwaya da wuri kafin ta bashi amsa , Mummyn zata yi saurin cafewa da fadin "Daddyn Farida kayi hakuri ka san kowa da irin yanayinsa. To ita haka Allah yayi ta bata da hanzari ko kadan".
Yadda take kama da mahaifiyar ta haka halinsu yake iri daya. Ita maba mai azarbabin magana ba ce. Hakan ke bawa Mummy danar cin galaba a kanta.
Bata taba ba ta damar magana da mahaifinta direct ba. Da ya yi yunkurin tambayarta wani abu ko kuma yana niyyar yi mata fada to kuwa caraf zata amshe zancen.
Hakan ya sanya mahaifinta bai san komai dangane da halin da take ciki ba.
A cikn sauran 'yan uwanta Farida duk tafi su kirki. Ita ke kokarin janta a jiki. Amma su anti Sakina sun fi kowa takura mata. Bata da wata daraja sama da wacce za su bawa 'yar aiki.
Ga shi dai itace 'yar gida ,amma ba wata alama da zata nuna maka hakan.
Tun farko da ta zo double bunk biyu ne a dakin. Su anti Sakina na kwana a kasan kowanne yayin da Farida da Farisa suke saman su.
Saboda haka ita bata da makwanci. A kan kafet take kwana. Tun bata fi wata biyu da zuwa gidan ba taji gidan ya gundureta saboda rashin kula da take samu daga wajen mazauna gidan baki daya.
Ita in ba sanda ta zo gidan ba ina ta san wani kula da kanta ko kayanta. Amma yanzu idan tayi wanka ruwanta idan taga dama tayi sallah ita ta sani. Idan ta alkinta kayanta kanta ta yiwa. In ba haka tana ji tana kallo su Farisa zasu mai da mata kaya duster.
Ranan farko da hakan ta faru. Farisa ta zo ta samu ta dauki dankwalin rigarta ta wan nan sallar da aka yi musu tana goge takalmin ta da shi.
Tun ranar salla da ta saka atamfar bata sake sata ba. Haushi ya kamata ta fisge dankwalin tana fadin "saboda wulakanci da kayana zaki yi duster".
"An yi duster da shi. Banza 'yar kauye". Farisa ta amsa cikin rashin kunya. Wai ita takamarta itace babba sai ta dauka tana da 'yancin hukunta kannenta idan sun mata laifi. Saboda haka tana daga hannu ta wankawa Farisa mari. Duka dan hannunta nama guda nawa yake. Marin ma dan kada ne ya samu Farisa.
Amma wai yarinyarnan bata fi shekaru biyar ba amma ta iya kazafi. Sai da ta juta ta kalleta tace "la la la laa! Ni kika mara. Yau kuwa zaki sha mari".
"An mare ki din". Inji Zainab. Nan Farisa ta tafi ta barta tana kunkuni bata mata kaya masu daraja da akayi.
Allah yarinyar nan ba ta fasa kuka ba sai da ta kusa isa dakin Mummy. Ta kuwa dage ta faskara wani irin ihu. Irin wanda baka jinsa sai in tafasasshen mangyada ya zubo a jikin yaro. Da sauri mummy ta fito tana fadin "ke meye ya same ki"?
Ba ta bata amsa ba sai ma wani kukan da ta tsiri yi. Sai da mummy tayi rarrashi sannan ta tsagaita cikin shesshekar kuka tace "ba Zainab ce ba abin da nayi mata ta kamani ta dinga marina. Har taji min targade a kunne....,."
Ai bata jira jin karashen magana ba ta fizge ta suka nufi dakin yaran. Zainab na kokarin ninke kayanta ba zato ba tsammani taji saukar mari zafafa guda hudu biyu ta kowanne bari.
Nan take farar fuskarta ta koma ja.
"Muguwa mai hali irin na uwarta. Dama turo ki tayi ki zo ki nakasta min 'ya'ya. To ki koma ki sanar da ita ni nafi karfin ku daga ke har ita. Annamimiya". Ta fada tana me sake kai mata rankwashi aka.
Saboda azaba kasa kuka tayi yayin da daga gefe Farisa take mata gwalo.
Nan dai Mummy ta kari masifarta ta ja 'yarta suka fice daga dakin.
Sai da suka fita san nAn hawaye ya zubo mata. Nan ta kwanta a tsakiyar daki tana faman kukan ciwon da idonta da kuma kanta ke yi. Ba kuwa ita ta samu relief ba sai da Allah ya dawo da Farida daga lesson ta zo ta tarar da ita a haka.
Falon babansu ta ruga da gudu tana fadin "Abba Mummy ku zo ku ga Zainab ta na kuka bata da lafiya".
Da hanzari duk su biyun suks nufi inda take. Suna zuwa Mummy Rumaisa ta daga ta ta rungume a jikinta tana fadin "ke kuma baki da lafiya ba zakiyi magana a baki magani ba. Yi sauri Farida duba drwaer a dakina ki dauko min panadol".
Tana dago ta da niyyar bata maganin ya hankalta da jinin da ya kwanta a gefen idonta. Cike da tsoro ya tambaya. "Zainab meye haka ma ya samu idonnki"?
Kafin tace komai Mummyn tayi sauri tayi chipping in. "A garin wasan banzan su ta je ta bige. Zainab ki dinga kula. Maza hanzarta Farida akwai chloramphenicol a cupboard din bandaki na ki dauka ki kawo min".
Haka kuwa wan nan zance ya wuce ba tare da Abbansu ya san me ke faruwa ba.
Sa ar Rumaisa Daya ce Abban nasu ya kasance irin mazan wan nan zamani wanda ba ruwansu da sa ido a harkar iyali. Wadanda suka dauka nauyi daya ne a kansu. Su fita su nemo su kawo domin wadata iyali.
To itama wan nan damar ta samu take amfani da ita.
Ba ta fi shekara biyu a gidan ba kuwa Mummy ta sake haihuwa inda ta samu Khalil. Kaf renon Khalifa kan Zainab ya koma.
Hakan ya sa karatun ta ya dada ja baya. Ga mahaifinsu Allazi boko. Shi in ba jarrabawa kaci ba ba abin da zaka yi ka birgeshi.
Na islamiyya ne Allah yasa tana da rabo.
Saboda ana musu shi ne a gida bayan la'asar. Sai tayi sa'a kusan duk fitar Mummy tafi yinta da la'asar din hakan yasa take samun sukunin daukarsa.
Malam Usman shine sunan mijin da mahaifiyarta ta aura. Mutum ne mai yakana da sanin ya kamata. Ga shi dai bata daura super da cotton lace balle getzner, amma kwanciyar hankali ta sanya Khadija ta murmure tayi kyau. Kamar matar wani babban mutum.
Shi tsohon mijinta yana mata dariyar daga England ta koma Garko. Bai san ita kuwa a rayuwar da ta samu kanta, Mecca kawai ta fiye mata zama da malamin mijinta a garkon ba.
Shi ya takura akan tazo taga 'yarta. Ta so taki zuwa saboda sanin halin mutanen gidan data baro,amma sam yaki karbar uzirinta da kokarin nuna mata ba zai yiwu ta fita sabgar 'yarta ba saboda bata tare da mahaifinta. Tun da ai shi kam ya so riketa , suka hana shi.
Sai da ya bari anyi albashi ya hada mata tsaraba rankacakaf ya kuma roki abokinsa mai motar haya golf daya sauke ta. Idan yaso idan ta yini in yayo lodi zai dawo sai ya biya ya dauketa su dawo tare.
[8/6, 23:11] +234 814 948 5104: FINI A UBA 👨👧👧IN FIKI A MIJI💑
PAGE 3
BY HANNE ADO ABDULLAHI
Hajiya Khadija ta sauka kofar gidan su Zainab watau gidan tsohon mijinta domin ziyarar 'yar ta wacce ta haura shekara biyu rabo da suga juna.
Ta fito da abincin maigadi za ta kai masa ta hango maigadin yana yiwa tsohuwar uwardakinsa rakiya.
Dauke yake da katon kwando cike da albasa. Yayin da ita kuma ta dauko jarkoki guda biyu irin rabin poster nan.
Dukkansu cike suke da lafiyayyen kindirmo. Ai tana ganinta ta saki flask din abincin maigadin ta ruga a guje ta rungume ta tana fadin "ga ummana ! Ga ummana".
"To sakeni kar ki kada dani " itama ta fada cikin murnar ganin 'yarta ta fari. In ban da tsawo ba abin da ta kara. Sai ma duhu da rama da ta lura ta dan yi.
Ta ki sakin nata saboda gani take idan ta sake ta guduwa zata yi.
Zainab rike da hannun mahaifiyarta suka dumfari kofar shiga gidan.
"Ke dakata. Ina zaki"?
Mamaki wan nan tsawa da ta daka musu ya sanya khadijan tsayawa cikin mamaki.
Ita bata ga lokacin da ta fito zuwa inda suke ba. Saboda ta shagalta da surutun da Zainab ke rangada mata. Bata san cewa karadin murnar ganinta ya fito da Rumaisa ba. Wadda ita kuma mamakin tashin muryar Zainab din ne ya sata fitowa saboda bata taba jin sautin muryarta irin haka ba.
"Uban me kika zo yi. Wacce irin marar zuciya ce ke. Miji ya koreki amma kin nace masa sai bibiyar sa kike".
"Kwantar da hankalinki. Ba wajen Yaya Abdullahi nazo ba. Zainabu na zo gani".
"Zainab kika ce kin zo gani. To itama na haramta miki ita". Rumaisa ta fada tana mai fizgo Zainab da ta makale jikin mahaifiyarta. Bata kuwa tsaya ba sai da ta kaita har cikin dakin ta wurgar da ita. San nan tace "bari in gama da uwarki san nan in dawo kanki". Ta rufe kofar da karfi sannan ta koma tsakar gida inda ta baro Khadija tsaye cikin mamaki.
Tana karasowa tace da ita cike da masifa "ke kuma na dawo gareki. Idan don wan nan jajakuwar 'yar taki kike shigo min gida. To ina son ki sani ke da ita sai dai a lahira idan kuna da rabon ganawa. Kumanayi miki alkawarin wan nan 'yar da kike takama da ita sai na daidaita ta sai na tarwatsa rayuwarta. Sai na maida miki ita abar kwatance saboda munanan halayen da zan tabbatar ta horu da su. Sai kin dawo kina jin kunyar nuna ta a matsayin diyar da kika haifa".
"Allah ya fiki" shine kawai abin da Khadija ta fada ta juya tana kokarin fita daga gidan.
"Dawo ina zaki ban gama magana dake ba".
"Ni ai na gama magana dake" ta fada tana mai kokarin fita daga gidan.
Tun da Allah ya dawo da Zainab gidan nan bata kara sanin menene farin ciki ba.
Da babanta ya je dauko ta daga hannun mahaifiyarta da cin hancin karatu mai nagarta ya rarrashe ta ya kuma dakko ta da alkawarin haka. Amma ga shi nan a sati da kyar take samu ta je sau biyu ko sau uku. Saboda Mammy ta kafa mata dokar ita zata dinga gyara dakinsu bayan sun tashi san nan ta jira kowa yayi wanka ta wanke bandakin su.
Hakan ya sanya ta ke zama ta karshe wajen shiryawa. Kuma da Abbansu zai fara fada a kan cewa me ya hana ta shirwaya da wuri kafin ta bashi amsa , Mummyn zata yi saurin cafewa da fadin "Daddyn Farida kayi hakuri ka san kowa da irin yanayinsa. To ita haka Allah yayi ta bata da hanzari ko kadan".
Yadda take kama da mahaifiyar ta haka halinsu yake iri daya. Ita maba mai azarbabin magana ba ce. Hakan ke bawa Mummy danar cin galaba a kanta.
Bata taba ba ta damar magana da mahaifinta direct ba. Da ya yi yunkurin tambayarta wani abu ko kuma yana niyyar yi mata fada to kuwa caraf zata amshe zancen.
Hakan ya sanya mahaifinta bai san komai dangane da halin da take ciki ba.
A cikn sauran 'yan uwanta Farida duk tafi su kirki. Ita ke kokarin janta a jiki. Amma su anti Sakina sun fi kowa takura mata. Bata da wata daraja sama da wacce za su bawa 'yar aiki.
Ga shi dai itace 'yar gida ,amma ba wata alama da zata nuna maka hakan.
Tun farko da ta zo double bunk biyu ne a dakin. Su anti Sakina na kwana a kasan kowanne yayin da Farida da Farisa suke saman su.
Saboda haka ita bata da makwanci. A kan kafet take kwana. Tun bata fi wata biyu da zuwa gidan ba taji gidan ya gundureta saboda rashin kula da take samu daga wajen mazauna gidan baki daya.
Ita in ba sanda ta zo gidan ba ina ta san wani kula da kanta ko kayanta. Amma yanzu idan tayi wanka ruwanta idan taga dama tayi sallah ita ta sani. Idan ta alkinta kayanta kanta ta yiwa. In ba haka tana ji tana kallo su Farisa zasu mai da mata kaya duster.
Ranan farko da hakan ta faru. Farisa ta zo ta samu ta dauki dankwalin rigarta ta wan nan sallar da aka yi musu tana goge takalmin ta da shi.
Tun ranar salla da ta saka atamfar bata sake sata ba. Haushi ya kamata ta fisge dankwalin tana fadin "saboda wulakanci da kayana zaki yi duster".
"An yi duster da shi. Banza 'yar kauye". Farisa ta amsa cikin rashin kunya. Wai ita takamarta itace babba sai ta dauka tana da 'yancin hukunta kannenta idan sun mata laifi. Saboda haka tana daga hannu ta wankawa Farisa mari. Duka dan hannunta nama guda nawa yake. Marin ma dan kada ne ya samu Farisa.
Amma wai yarinyarnan bata fi shekaru biyar ba amma ta iya kazafi. Sai da ta juta ta kalleta tace "la la la laa! Ni kika mara. Yau kuwa zaki sha mari".
"An mare ki din". Inji Zainab. Nan Farisa ta tafi ta barta tana kunkuni bata mata kaya masu daraja da akayi.
Allah yarinyar nan ba ta fasa kuka ba sai da ta kusa isa dakin Mummy. Ta kuwa dage ta faskara wani irin ihu. Irin wanda baka jinsa sai in tafasasshen mangyada ya zubo a jikin yaro. Da sauri mummy ta fito tana fadin "ke meye ya same ki"?
Ba ta bata amsa ba sai ma wani kukan da ta tsiri yi. Sai da mummy tayi rarrashi sannan ta tsagaita cikin shesshekar kuka tace "ba Zainab ce ba abin da nayi mata ta kamani ta dinga marina. Har taji min targade a kunne....,."
Ai bata jira jin karashen magana ba ta fizge ta suka nufi dakin yaran. Zainab na kokarin ninke kayanta ba zato ba tsammani taji saukar mari zafafa guda hudu biyu ta kowanne bari.
Nan take farar fuskarta ta koma ja.
"Muguwa mai hali irin na uwarta. Dama turo ki tayi ki zo ki nakasta min 'ya'ya. To ki koma ki sanar da ita ni nafi karfin ku daga ke har ita. Annamimiya". Ta fada tana me sake kai mata rankwashi aka.
Saboda azaba kasa kuka tayi yayin da daga gefe Farisa take mata gwalo.
Nan dai Mummy ta kari masifarta ta ja 'yarta suka fice daga dakin.
Sai da suka fita san nAn hawaye ya zubo mata. Nan ta kwanta a tsakiyar daki tana faman kukan ciwon da idonta da kuma kanta ke yi. Ba kuwa ita ta samu relief ba sai da Allah ya dawo da Farida daga lesson ta zo ta tarar da ita a haka.
Falon babansu ta ruga da gudu tana fadin "Abba Mummy ku zo ku ga Zainab ta na kuka bata da lafiya".
Da hanzari duk su biyun suks nufi inda take. Suna zuwa Mummy Rumaisa ta daga ta ta rungume a jikinta tana fadin "ke kuma baki da lafiya ba zakiyi magana a baki magani ba. Yi sauri Farida duba drwaer a dakina ki dauko min panadol".
Tana dago ta da niyyar bata maganin ya hankalta da jinin da ya kwanta a gefen idonta. Cike da tsoro ya tambaya. "Zainab meye haka ma ya samu idonnki"?
Kafin tace komai Mummyn tayi sauri tayi chipping in. "A garin wasan banzan su ta je ta bige. Zainab ki dinga kula. Maza hanzarta Farida akwai chloramphenicol a cupboard din bandaki na ki dauka ki kawo min".
Haka kuwa wan nan zance ya wuce ba tare da Abbansu ya san me ke faruwa ba.
Sa ar Rumaisa Daya ce Abban nasu ya kasance irin mazan wan nan zamani wanda ba ruwansu da sa ido a harkar iyali. Wadanda suka dauka nauyi daya ne a kansu. Su fita su nemo su kawo domin wadata iyali.
To itama wan nan damar ta samu take amfani da ita.
Ba ta fi shekara biyu a gidan ba kuwa Mummy ta sake haihuwa inda ta samu Khalil. Kaf renon Khalifa kan Zainab ya koma.
Hakan ya sa karatun ta ya dada ja baya. Ga mahaifinsu Allazi boko. Shi in ba jarrabawa kaci ba ba abin da zaka yi ka birgeshi.
Na islamiyya ne Allah yasa tana da rabo.
Saboda ana musu shi ne a gida bayan la'asar. Sai tayi sa'a kusan duk fitar Mummy tafi yinta da la'asar din hakan yasa take samun sukunin daukarsa.
Malam Usman shine sunan mijin da mahaifiyarta ta aura. Mutum ne mai yakana da sanin ya kamata. Ga shi dai bata daura super da cotton lace balle getzner, amma kwanciyar hankali ta sanya Khadija ta murmure tayi kyau. Kamar matar wani babban mutum.
Shi tsohon mijinta yana mata dariyar daga England ta koma Garko. Bai san ita kuwa a rayuwar da ta samu kanta, Mecca kawai ta fiye mata zama da malamin mijinta a garkon ba.
Shi ya takura akan tazo taga 'yarta. Ta so taki zuwa saboda sanin halin mutanen gidan data baro,amma sam yaki karbar uzirinta da kokarin nuna mata ba zai yiwu ta fita sabgar 'yarta ba saboda bata tare da mahaifinta. Tun da ai shi kam ya so riketa , suka hana shi.
Sai da ya bari anyi albashi ya hada mata tsaraba rankacakaf ya kuma roki abokinsa mai motar haya golf daya sauke ta. Idan yaso idan ta yini in yayo lodi zai dawo sai ya biya ya dauketa su dawo tare.
[8/6, 23:11] +234 814 948 5104: FINI A UBA 👨👧👧IN FIKI A MIJI💑
PAGE 3
BY HANNE ADO ABDULLAHI
Hajiya Khadija ta sauka kofar gidan su Zainab watau gidan tsohon mijinta domin ziyarar 'yar ta wacce ta haura shekara biyu rabo da suga juna.
Ta fito da abincin maigadi za ta kai masa ta hango maigadin yana yiwa tsohuwar uwardakinsa rakiya.
Dauke yake da katon kwando cike da albasa. Yayin da ita kuma ta dauko jarkoki guda biyu irin rabin poster nan.
Dukkansu cike suke da lafiyayyen kindirmo. Ai tana ganinta ta saki flask din abincin maigadin ta ruga a guje ta rungume ta tana fadin "ga ummana ! Ga ummana".
"To sakeni kar ki kada dani " itama ta fada cikin murnar ganin 'yarta ta fari. In ban da tsawo ba abin da ta kara. Sai ma duhu da rama da ta lura ta dan yi.
Ta ki sakin nata saboda gani take idan ta sake ta guduwa zata yi.
Zainab rike da hannun mahaifiyarta suka dumfari kofar shiga gidan.
"Ke dakata. Ina zaki"?
Mamaki wan nan tsawa da ta daka musu ya sanya khadijan tsayawa cikin mamaki.
Ita bata ga lokacin da ta fito zuwa inda suke ba. Saboda ta shagalta da surutun da Zainab ke rangada mata. Bata san cewa karadin murnar ganinta ya fito da Rumaisa ba. Wadda ita kuma mamakin tashin muryar Zainab din ne ya sata fitowa saboda bata taba jin sautin muryarta irin haka ba.
"Uban me kika zo yi. Wacce irin marar zuciya ce ke. Miji ya koreki amma kin nace masa sai bibiyar sa kike".
"Kwantar da hankalinki. Ba wajen Yaya Abdullahi nazo ba. Zainabu na zo gani".
"Zainab kika ce kin zo gani. To itama na haramta miki ita". Rumaisa ta fada tana mai fizgo Zainab da ta makale jikin mahaifiyarta. Bata kuwa tsaya ba sai da ta kaita har cikin dakin ta wurgar da ita. San nan tace "bari in gama da uwarki san nan in dawo kanki". Ta rufe kofar da karfi sannan ta koma tsakar gida inda ta baro Khadija tsaye cikin mamaki.
Tana karasowa tace da ita cike da masifa "ke kuma na dawo gareki. Idan don wan nan jajakuwar 'yar taki kike shigo min gida. To ina son ki sani ke da ita sai dai a lahira idan kuna da rabon ganawa. Kumanayi miki alkawarin wan nan 'yar da kike takama da ita sai na daidaita ta sai na tarwatsa rayuwarta. Sai na maida miki ita abar kwatance saboda munanan halayen da zan tabbatar ta horu da su. Sai kin dawo kina jin kunyar nuna ta a matsayin diyar da kika haifa".
"Allah ya fiki" shine kawai abin da Khadija ta fada ta juya tana kokarin fita daga gidan.
"Dawo ina zaki ban gama magana dake ba".
"Ni ai na gama magana dake" ta fada tana mai kokarin fita daga gidan.