← Book details Feeryal Part 2 Complete Hausa Novel.t Local reading mode
READING PART 7 OF 43

Sashe 7

Feeryal Part 2 Complete Hausa Novel.t · about 8 min read

Zuwa can ya soma magana
"Ina kuka fito har 11 na dare kuna waje?."
Suka had'a baki wajen fad'in
"Munje dinner yayan kawar mu ce."
sai a lokacin ya tsai da abin da yake ya d'ago ya dube su d'aya bayan d'aya sannan ya ce
"Da daddaren nan sabo da rashin mafad'i ko me, ina Miemie ta ke?."
da sauri Ameerah ta ce
"Samarukansu ne suka d'auke su bamusan ina suka je ba."
"What! samarukansu ita da wa?."
ya furta yana duban su, abin ya bala'in bashi mamaki wai wad'an nan 'yan hanci wai su ke da samaruka.
ta ce
"Ita da Feeryal kuma da ganin su 'yan iska ne,
samarukan, sai da na ce su zo muje gida suka ki."
tana rufa baki motar su Miemie yana shigowa gidan.
duk suka bi motar da ido, su Nabila kirjinsu na dukan uku-uku Ameerah tayi karya ta janyo musu.
ya yi shiru idanunsa akan laptop yana tuka maganar cikin ransa.

Kasancewar motar Ammah ce direban ya yi kokarin wucewa sashin ta da su.
da sauri Miemie data hango su Sahla durkushe a gaban yayan nasu ta ce
"Tsaya-tsaya mu sauka anan sai ka wuce,
Feeryal sauko muje ga su Ameerah can gurin Ya Abdurrahim."
suka sauko jiki a sanyaye kar Feeryal uwar 'yan tsoro taji labari.
a hankali suka karaso suka sunkuya kamar yadda su Ameerah sukayi.
a fusace ya d'ago ya ce
"Miemie har kinyi girman da zakibi samari a mota!."
ido ta waro murya na rawa ta ce
"Wlh Ya Abdurrahim babu wanda muka bi direban Ammah ne ya kaimu kuma shi ya dawo da mu."
da sauri Ameerah ta ce
"Bayan muna ganin ku da su har wani ya yi wa Feeryal kiss, daga nan kuma kuka bisu kuka tafi."
da sauri ya kuma d'ago kansa karaf suka had'a ido da Feeryal da tsoro ke kukarin tafiya da numfashin ta.
maganar Ameerah ce ya sashi mai da dubansa gareta
"Na rantse ya mata kiss a gaban jama'a ma kuwa, ai gasu nan."
ta mika masa wayar ta,
hoton Feeryal karara wani yana mata kiss, ga d'ayan fuskarsu daf da juna har suna gogar fuskar juna.
Miemie ta marairaice murya ta ce
"Kai Ameerah kiji tsoron Allah a'ina akayi hakan."
a fusace yad'a go wayar ya nuno musu fuskar wayar.
Feeryal tayi wani irin zabura, jiki na kyarma.........!

Mommyn Twins ce

Wani irin sarawa kanta ya yi da sai da ta kai hannu ta dafe kan, tana girgiza kan cike da matukar tsoro.
hanjin cikin Miemie ya kad'a.
cikin fusatacciyar murya ya nuna Feeryal da hanu ya ce
"Ke tashi kibar nan!."
ya fad'a cikin tsawar da sai da ta zabura ta zube kasa kana ta mike da gudu ta yi hanyar sashin Aunty.
b'acin rai karara ake hangowa kan fuskarsa, ya mike a zafafe tare da d'aukar belt dake ajiye a gefensa.
yashiga nad'e shi a hannunsa yana fad'in
"Wato kun zama 'yan'iska kamar ku d'in nan har kun iya biyewa sa maruka, yaushe ne aka haifeku!."
Ameerah ya damko yana cewa
"Wato ke har kin iya d'aukar hoto ana bad'a la, ga kinan 'yar iska ko."
yashiga shinfid'a mata belt tana ihu sai da ya mata taya-taya kafin ya sake ta, ya bita da naushi,
tana tsalle tana sosa in da aka zuzzuba mata bulala.
su Sahla kam tuni suka fashe da kuka tun kafin a zo kansu.
ya cafko Nabila itama ya birkita ta da duka, yana sakin ta ta zube kasa tana kuka.
haka Sahla ma.
Miemie ce dukan karshe yadda taga yake huci yana dad'a kyara rukon betl d'in tasan yau kam zataci uban ta,
ai kuwa dukanta yafi na kowa, sai da ya mata bulala ashirin da biyar kafin ya kyaleta.
sannan ya nuna su ya ce
"Daga yau wata ta sake sa kafa ta fita a gidan nan ta gani, ku tashi ku bani guri a nan!."
da gudu ko wannen su ya yi hanyar sashinsu.

Ganin yadda Feeryal tashigo a firgice Aunty da tun d'azu hankalinta yake tashe ganin karfe goma yayi basu dawoba.
har 11 tarinka kiran wayar Feeryal d'in saijin ringing d'in sa a d'akinta tayi.
wayar Miemie kuwa yana shiga ba'a dagawa.
tajawota dasauri tana dad'in
"Ke Feeryal lafiya meyasa baku dawo akan lokaci ba sai yanzu, meyasa kuka zauna meyafaru naganki Hak?."

Aunty tana maganan cikin tashin hankali.
Feeryal ta kankameta tana kuka bata b'oyemata komai ba tafad'a mata duk abin da ya faru.
Aunty taja Numfashi cike da fargaba tace
"Yanzu ina su Miemien suke, suna gurin yayansu kenan?."
Feeryal tace Eh.
Aunty tatsaya shiru kana taja hannunta suka shiga d'aki.

Tana fad'in
"Shiyasa tunfarko banso tafiyan nan nakuba,
samari 'yan bana d'ayan nan basu da tabbas,
shiyasa kullum magana ta baiwuce ki kula ba,
Feeryal Allah ya yi miki baiwar zubin halittar da ba kasake za'a barki ki rika yawo ba,
fitar nan sam bana son shi sai ya zama dole."
Aunty ta rika fad'a Feeryal da har lokacin tsoro bai gama sake ta ba,
sai sharar kwalla take.
sai kuma Aunty ta shiga rarrashin ta,
kana ta taimaka mata ta cire kayan jikinta ta shiga bandaki tayi wanka tafito.
tagabarta da sallahn isha tasa kayan bacci ta haye gado takwanta,
tare da sunkulewa guri guda tana rarraba ido cikin tsoro.
har lokacin Aunty nacikin d'a kin tasata tayi addu'ar bacci kafinnan tafita .

Takai zamani guda batayi bacci ba tana sake-sake a ranta sai chan bacci barawo ya sami damar yin awon gaba da ita.

Nabila ta shige sashin su a guje tana mussuke jikin ta inda ta sha bulalu.
Umma Karima ta zabura da sauri tana fad'in
"Ke lafiya yaya haka?."
Nabila ta zube gefen ta tana cewa
"Ya Abdurrahim ne ya bige mu."
"Duka kuma a laifin me?."
Umma Karima tayi tambayar tana yamutsa fuska.

Nabila ta gyara zama ta shiga fesa mata labarin abin da ya faru karya da gaskiya.
Umma Karima ta ware ido tare da buga kirji ta ce
"Ita da laifi ku da duka! jar'uba har ta iya tsotsar bakin namiji a cikin bainin nasi,
baiyi kasa-kasa da ita ya farfasawa shegiya baki, muga bakin da zata tsotsi bakin wani namijin da shi ba,
ai wannan yarinyar tajima tana iskanci tun tana kankanuwar, tafiyarta Abujan da taje ma iskanci take acan ai munsan komai,
gashinan asirinta na kan tonuwa kad'an ma ke nan, in Allah ya yarda asirinta yarika tonuwa ke nan,
sai tabar gidan nan,
ai abin da yasa Abdurrahim ya koreta ba zai iya yiwa kazanta hukunci ba,
ai sai dai ku tsaftatattun kannen sa,
ta ya zaiyi yayiwa 'yar'iska hukunci, hukuncin ta ke nan kora gidan ma gaba d'aya zata bari,
yanzu kam alkadarin ki Fatima ya karye daga zaran Abdurrahim ya ce ta bar gidan nan dole zata bari,
hahahaha."
ta karasa maganar da shekewa da dariya tana tafa cinya.

Washegari kuwa Umma karima har da kiran Ameerah ta zo ta nuna mata hoton.
Umma Karima ta rike baki ta ware ido kan wayar tana fad'in
"Tabd'i jam lallai yarinyar nan cikakkiyar 'yar'iska ce asirinta yarika tonuwa ke nan."

Sai da rana kafin Miemie tashigo sashin su Feeryal.
a falo ta tadda Aunty da Feeryal d'in zaune,
ta zauna tare da gaida Aunty,
ta amsa tana cewa
"Kunyi rashin hankali Miemie da kukakai goma awajen taron nan,
watakilama shiyasa maza suka bibiyeku,
da kundawo kan lokaci da duk hakan bai faruba,
Allah dai yatsare yasa yayanku baimuku komai ba dai?."
Miemie taja rigarta tagwada wa Aunty shatin bulala Aunty tawaro ido tace
"Subhanallah abin da ake guje muku ke nan Miemie yanzu ina amfanin sa, sam fitar dare ba na d'iya mace bace, Allah shikyauta gaskiya ku rika kiyayewa."
Feeryal kaman zatayi kuka ganin shatin bulala a jikin Miemie.
ta ce "Wayyo sannu Miemie dan Allah kiyi hakuri ."

Miemie tayi kwafa ta ce
"Wallahi bazan kyale Ameerah ba,
ba ita ta iya munafurciba dukda tare aka bige mu."
Aunty ta ce
"Kiyi hakuri kar kice zakuyi fad'a da ita tunda itama anbigeta, ki rabu da ita kawai, ku dai kurika kiyaye abin da zai janyo muku laifi."
Miemie sai kwafa take tana cize lips.

Aunty tayi kitchen tana saka lamarin aranta sam bataji dad'i ba da Abdurrahim bai hadasu da Feeryal ya musu hukunci dukan su ba,
tun da in laifin ne tare sukayi,
ya ware kannensa kenan yamusu hukunci?.
ta girgiza kai kawai tana shigewa kitchen.

"Ke Ameerah kada kiyi gigin cewa zaki yad'a hoton nan a Media dan wlh idan kika kuskura Ya Abdurrahim ya ci karo da shi sunan ki sorry, sai ya yi miki kabarin da ba sallah,
jiya ma ke nan ya yi miki dukan d'aukar hoton bare kuma kin yad'a shi wa duniya,
zai ce dama kin saba yad'a hotunan batsa wlh mukam babu ruwan mu."
cewar Sahla da suke tare da su Ameerah a parlour'n Mommy.
Nabila ta ce
"Gaskiya nima dai ban bada goyon baya ba, kibari Ameerah mu aje hoton nan zai zame mana makami nan gaba, ai shegiya banso Ya Abdurrahim ya barta ta ba, da ya mata shegin duka 'yar iska yanzu kam mun gama da ita babu wanda zai zo gurin ta,
in yazo kuwa sai ya gani."
Sumayya ta rike hab'a ta ce
"Hm wlh Ameerah kibi ahankali ku rabu lafiya da Ya Abdurrahim,
ina dukan da ya miki akan d'aukar hoton ne shine zaki ce zaki yad'ashi wa duniya, idan fa kika kuma shiga hannunsa bazaki ga da kyau ba."
Ameerah ta ja tsaki
"Mttss ai na rantse da Allah yadda aka bige ni sai an bige ta, wulakantaccen duka ma kuwa,
da wayarta zanyi sending hoton wa duniya kowa ma yagani ta yadda kowa zai d'auka ita d'in ce ke tallen kanta wa duniya."
Sumayya ta gorgiza kai ta ce
"Ameerah nadai gaya miki kibi a sannu, idan ta kwab'e miki bazakiga da kyau ba."
Ameerah ta mike tana hararar Sumayya ta wuce d'aki,
cike da shan alwashin sai ta aikata.

Bayan kwana uku da faruwar haka da sauri Miemie ta shigo sashin Auny.
Chapter 7 · 0% Book details