Sashe 16
Feeryal Part 2 Complete Hausa Novel.t · about 8 min read
Kasancewar tana fashin sallah,
tana fita daga wanka ta saka kaya ta fito parlour.
Aunty taji dad'in ganin yadda ta warware sosai, kamar ba ita ce jiya da d'azu abin tausayin nan ba.
Suna parlour da Aunty na sallar magriba ita kuma tana kwance tana buga game a wayarta.
Miemie ta shigo, ta zauna gefen ta tana fad'in
"Mara lafiyar ke nan d'azu na shigo ai kina bacci Aunty ke ce min baki da lafiya."
murmushi ta yi
"Eh amma naji sauki."
"Ba dai tsoro ne ya saki ciwo ba,ma tsoraciya kawai."
dariya kawai ta yi.
Miemie ta zauna sukayi ta hira har bayan sallar ishe kafin ta koma sashin su.
Siyama ce ta fad'o cikin d'akin Umma Karima, ta cire takalmi mai tsinin da ke kafarta tayi wurgi da shi.
"Ya ya mene ne hakan Siyama?."
"Aunty Karima kiyi wani abu dan Allah, ki duba fa ki gani lokaci kurewa ya ke dad'a yi,
auren nan fa da gaske za'ayi,
gashi duk wata hanyar da zanbi wai dan hankalin sa ya dawo kai na duk a banza,
dubeni ki gani dubi shiga ta ki gani ki ga irin had'ewa ta fa,
a haka yazo ya iske ni a sashin Mommy amma ko kallo ban isheshi ba,
duk yadda zanbi na janyo hankalin sa na bi amma babu wata nasara."
Umma Karima ta mike ta dafa kafad'ar ta ta ce
"Ina so ki kwantar da hankalin ki,
kar ki damu zaki mallaki Abdurrahim zaki same shi a tafin hannunki, boka yabani tabbaci kuma yana kan aiki a kan haka,
na yadda da boka Mali nasan bazai wasa mana kasa a ido ba,
auren nan da ke za'ayi in har ina numfashi."
"Aunty Karima in har abin nan bazai yuwuba kawai ni zan tinkare sa, na fad'a masa ina son sa."
"Dalla matsa can mashirmaciya kawai shi zai zo da kansa yace yana son ki, kuma zaki sha mamaki ki zuba ido kawai ki gani."
Da sauri Umma Karima ta d'aga hannu a kafad'ar ta tana cewa
"Tsaya ma tukun wai nikam kamar naga sonshi da gaske kika fara."
a dibirbirce Siyama ta ce
"Kamar ya Aunty Karima ai ni so nake ayi-ayi musamu abun da muke bukata, naga jinkirin zuwan lokacin ne kawai."
"Ai ho yanzu naji batu
je ki ki cire kayan nan ki huta, ki kwantar da hankalin ki kamar tsumma a randa, kamar yanzu lokaci zaiyi ayi a wuce gurin."
Siyama ta sauke b'oyayyen numfashi kana ta tattari takalmarta ta yi d'akin su.
Feeryal ce kwance a parlour saman doguear kujera rike da waya tana buga game.
Miemie ta shigo ta zauna gefen ta tad'a mata buka acinya tana fad'in
"Yanzu dama wayar tana hannunki nake ta kira kika ki d'aga wa."
"Wash Allah Miemie ta zafi fa."
"Ai dama so nake kiji zafin, ayi ta kiran ki a waya kike d'agawa, tun d'azu na tura miki abu ta Whatsapp baki ma hau online d'in ba bare ki gani,
ke kam ma ba amfanin wayar ki,
kalli kiga ni ashoben da muka cire na kannen ango kala biyar ne, Unaisa da Umaima'n Hajiyan Dubai ne zasu taho mana dashi daga can,
duk kalolin nan ba karamin kyau zasu miki ba."
ta karb'i wayar tana duba wa
"Gaskiya sun yi kyau kam."
ta fad'a tana mika mata wayar.
Miemie ta ce
"Ai sosai ma kuwa idan muka yi waya da su zance a siyo har da ke."
"Da ni kuma to ai ni ba kanwar ango ba ce me zai sa nayi ashoben."
Miemie ta tsare ta da ido.
kai ta gyad'a tana cewa
"Eh ai Mommy ta ce shi ba yaya na ba ne kinga kuwa ni ma ba kanwar sa bace."
"Dan ta fad'a shine me dalla kiyi abin ki, kowa zai sa ke ne bazaki saba."
Feeryal ta d'au wayar ta ta cigaba da buga game d'in ta tana cewa
"Meye a ciki tun da ba tsirara zanyi yawo ba, nifa bazanyi ba karma ki sa su kawo."
Aunty da ta fito daga kitchen tayi shiru tana sauraran su.
Miemie ta mike tana cewa
"To idan an kawo an d'in ka kar ki sa."
"Ki sa a kawo da ita zata saka ma."
cewar Aunty tana karaso wa cikin parlour'n,
Miemie ta ce tom kana ta dubi Feeryal da
ta tab'e fuska.
Tana cewa
"Goben zamuje gyaran gashin kuwa ni fa so nake ma ayi min kitso gashina sai karyewa yake gara naki shi baya komai,
kar gashin yagama gwaguyewa."
"Eh zamuje."
"To Allah ya kaimu."
ta fice ta koma sashin su.
Washegari da wuri Miemie ta gama shiri ta biyo wa Feeryal suka fito bayan Aunty ta gama yi musu kashe din su dawo da wuri.
suna hanyar su na zuwa parking lot Ameerah ta hange su.
murya ta d'aga
"Ke Miemie tsaya-tsaya-tsaya."
Miemie ta juyo tana dalla mata harara dan tasan bai wuci halin nata na rashin mutunci zatayi mata ba.
Ameerah ta karaso in da suke ta harare su sama da kasa sannan ta ce
"Da kika cewa su Unaisa su karo ashobe na mutum d'aya, ke zaki sa kala goma iri d'aya da naki da wanda za'a karon."
"Ina ruwan ki meye damuwar ki idan zan sa duka, idan kuma ma wata zan bawa kina da matsala ne,
ko akwai sisin ki a cikin kud'in siyan kayan,
Daddy ne me bada kud'in ko ke da kika titsiye ni kina tambaya ta."
"Ai nasan bai wuce ma wannan Aljanar kika sa ba, to tunda kud'in bana uban ta bane baza a kawo da ita ba,
ta had'a dangi da Ya Abdurrahim d'in ne da zatayi ashoben bikin sa,
to bama son gayyan sod'i, ta tsaya a matsayin ta dangin sa ne zasuyi ashoben bikin sa ba bare 'ya'yan tsintuwa ba."
Feeryal tayi murmushin takaici taja hannun Miemie ta ce
"Muje Miemie."
Miemie ta fisge hanun tana cewa
"Ke kam kin yi asara Ameerah haka zaki kare da gori, idan kikace zakiyi min ni wlh farfasa miki baki zanyi 'yar rainin wayo."
"Miemie muje dan Allah, ki rabu da ita."
Feeryal ta fad'a tana kuma ruko ta.
Ameerah ta waiga gefe da sauri ta isa bayan mota ta sunkuya ta d'auko magen Hajiya da ke kwance a gindin mota, ta jefawa Feeryal a jiki tana gad'in
"Munafuka idan bata rabu da ni ba ya zatayi da ni."
Wani irin uban ihu Feeryal ta kurma tare da kankame jikinta dake cirawa,
nan da nan kwayar idanunta suka sauya, tayi wani irin yanke jiki ta rid'u a kasa, tare da kuma kwalla kara ta zare gyale da d'ankwalin kanta ta yamusa gashin kanta.
tayi wani irin mikewa ta shako wuyan Ameerah.........!
11
Wani irin damka tayi wa wuyan Ameerah, tana wani irin gurnani.
idon Ameerah ya firfito, ta d'aga hanu kafafaka kamar kaza a cikin ruwa ta rike hanun Feeryal tana ja tayi-tayi ta iya b'anb'are hannunta a wuyan ta ta gagara.
ganin yadda Ameerah ta ke fafutukan niman numfashi, da sauri Miemie ta ce
"Sake ta Feeryal yau kin nuna mata shiru shiru ba tsoro bane gudun magana ne, kyale ta mu tafi wannan ya zame mata darasi in ita mai gane wa ce,
in kuma bata gane ba gaba a kuma ankarar da ita."
da sauri Miemie ta shiga kokarin janye ta, sai ji tayi kamar dusi take tab'awa.
"Feeryal kyale ta sake ta haka."
tafad'a tana jan hannunta dake wuyan Ameerah, amma ko gizau hannun ta baiyi ba.
da sauri ta dube ta cike da mamakin yadda taji takasa iya b'anb'are hannunta dake wuyan Ameerah.
da karfe ta d'ago kanta dake sunkuye gashin kanta ya rufe fuskarta.
a razane Miemie tayi baya ganin kwayar idanunta da suka sauya izuwa na ban tsoro.
Da gudu ta juya tana fad'in
"Me gadi security Feeryal Ameerah kuzo dan Allah wlh ba ita ba ce ba Feeryal ba ce!."
gaba d'aya ta kid'ime, tayi bakin get a guje tana kiran security.
Nabila da Sahla da komai ya faru a kan idon su dan tare suke da Ameerah dama, su suka tsaya jiranta ita kuma ta karaso ciwa su Miemie mutunci.
suka juya da gudu sukayi sashin Mommy suna fad'in
"Wayyo Allah Mommy Feeryal zata kashe Ameerah."
Mommy ta fito a hargitse dai-dai sanda Security suma suke karasowa gurin.
Aunty ma ta iso a bujajan Baba Rabi ta sanar mata da abin da ke faruwa.
Security suka bugawa Feeryal tsawa sukace
ta sake ta.
ganin bata da niyyar sakin ta,
ga yadda numfashin Ameerah ke yi kamar zai bar jikin ta, suka shiga kokarin jan Feeryal da jan hannunta a wuyan ta.
amma ko gizau basu iya ko da jijjigata ba.
Mommy ta ce
"Wayyo Allah shegiya mayya zata kashe min yarinya."
tayi kukan kura
tashiga dukan Feeryal da hanu bibbiyu ta baya tana fad'in
"Mayya sake ta kashe ta zakiyi."
wani irin sa kafa tayi ta baya ta angiza Mommy sai ga Mommy a kasa shirim, ta kawo ihu ta saka, tana dafe bayanta.
security hud'u sukayi kan Feeryal sukayi sukayi su iya kwace Ameerah a hannunta suka kasa.
Aunty da hankalin ta yayi mummunar tashi
ta zo ta gaban Feeryal tana fad'in
"Kuyi hakuri dan girman Allah ku sake ta na gama ku da Allah, kar ku ja mana masifa."
"Ai ita ce masifar babban annoba wayyo Allah mun shiga uku zata kashe 'yar gida, wayyo jama'a ku kawo mana d'auki za'ayi kisa."
Umma Karima da rahoto ya kaimata ta iso yanzu take fad'a.
ta ci gaba da fad'in
"Ku harbeta da bindiga idan bata sake ta ba, kuna gani zata kashe ta, dalla ku kashe mara amfani."
sai kuma ta juya da gudu tayi sashin Daddy tana ihu.
Ta fad'o cikin parlour'n Daddy tana fad'in
"To Alhaji gashi can za'ayi kisa a cikin gidan ka,
ka aje gamasheka ta bunkasa tafara cire wuyan 'yan gida,
ga mayyar Aljanar 'yarnan can ta makure wuyan Ameerah har jini na fita, ko numfashi bata yi wata kila ma ta mutu yanzu,
wani irin bala'i ne wannan ka ajiye mana a cikin gida."
tana fita daga wanka ta saka kaya ta fito parlour.
Aunty taji dad'in ganin yadda ta warware sosai, kamar ba ita ce jiya da d'azu abin tausayin nan ba.
Suna parlour da Aunty na sallar magriba ita kuma tana kwance tana buga game a wayarta.
Miemie ta shigo, ta zauna gefen ta tana fad'in
"Mara lafiyar ke nan d'azu na shigo ai kina bacci Aunty ke ce min baki da lafiya."
murmushi ta yi
"Eh amma naji sauki."
"Ba dai tsoro ne ya saki ciwo ba,ma tsoraciya kawai."
dariya kawai ta yi.
Miemie ta zauna sukayi ta hira har bayan sallar ishe kafin ta koma sashin su.
Siyama ce ta fad'o cikin d'akin Umma Karima, ta cire takalmi mai tsinin da ke kafarta tayi wurgi da shi.
"Ya ya mene ne hakan Siyama?."
"Aunty Karima kiyi wani abu dan Allah, ki duba fa ki gani lokaci kurewa ya ke dad'a yi,
auren nan fa da gaske za'ayi,
gashi duk wata hanyar da zanbi wai dan hankalin sa ya dawo kai na duk a banza,
dubeni ki gani dubi shiga ta ki gani ki ga irin had'ewa ta fa,
a haka yazo ya iske ni a sashin Mommy amma ko kallo ban isheshi ba,
duk yadda zanbi na janyo hankalin sa na bi amma babu wata nasara."
Umma Karima ta mike ta dafa kafad'ar ta ta ce
"Ina so ki kwantar da hankalin ki,
kar ki damu zaki mallaki Abdurrahim zaki same shi a tafin hannunki, boka yabani tabbaci kuma yana kan aiki a kan haka,
na yadda da boka Mali nasan bazai wasa mana kasa a ido ba,
auren nan da ke za'ayi in har ina numfashi."
"Aunty Karima in har abin nan bazai yuwuba kawai ni zan tinkare sa, na fad'a masa ina son sa."
"Dalla matsa can mashirmaciya kawai shi zai zo da kansa yace yana son ki, kuma zaki sha mamaki ki zuba ido kawai ki gani."
Da sauri Umma Karima ta d'aga hannu a kafad'ar ta tana cewa
"Tsaya ma tukun wai nikam kamar naga sonshi da gaske kika fara."
a dibirbirce Siyama ta ce
"Kamar ya Aunty Karima ai ni so nake ayi-ayi musamu abun da muke bukata, naga jinkirin zuwan lokacin ne kawai."
"Ai ho yanzu naji batu
je ki ki cire kayan nan ki huta, ki kwantar da hankalin ki kamar tsumma a randa, kamar yanzu lokaci zaiyi ayi a wuce gurin."
Siyama ta sauke b'oyayyen numfashi kana ta tattari takalmarta ta yi d'akin su.
Feeryal ce kwance a parlour saman doguear kujera rike da waya tana buga game.
Miemie ta shigo ta zauna gefen ta tad'a mata buka acinya tana fad'in
"Yanzu dama wayar tana hannunki nake ta kira kika ki d'aga wa."
"Wash Allah Miemie ta zafi fa."
"Ai dama so nake kiji zafin, ayi ta kiran ki a waya kike d'agawa, tun d'azu na tura miki abu ta Whatsapp baki ma hau online d'in ba bare ki gani,
ke kam ma ba amfanin wayar ki,
kalli kiga ni ashoben da muka cire na kannen ango kala biyar ne, Unaisa da Umaima'n Hajiyan Dubai ne zasu taho mana dashi daga can,
duk kalolin nan ba karamin kyau zasu miki ba."
ta karb'i wayar tana duba wa
"Gaskiya sun yi kyau kam."
ta fad'a tana mika mata wayar.
Miemie ta ce
"Ai sosai ma kuwa idan muka yi waya da su zance a siyo har da ke."
"Da ni kuma to ai ni ba kanwar ango ba ce me zai sa nayi ashoben."
Miemie ta tsare ta da ido.
kai ta gyad'a tana cewa
"Eh ai Mommy ta ce shi ba yaya na ba ne kinga kuwa ni ma ba kanwar sa bace."
"Dan ta fad'a shine me dalla kiyi abin ki, kowa zai sa ke ne bazaki saba."
Feeryal ta d'au wayar ta ta cigaba da buga game d'in ta tana cewa
"Meye a ciki tun da ba tsirara zanyi yawo ba, nifa bazanyi ba karma ki sa su kawo."
Aunty da ta fito daga kitchen tayi shiru tana sauraran su.
Miemie ta mike tana cewa
"To idan an kawo an d'in ka kar ki sa."
"Ki sa a kawo da ita zata saka ma."
cewar Aunty tana karaso wa cikin parlour'n,
Miemie ta ce tom kana ta dubi Feeryal da
ta tab'e fuska.
Tana cewa
"Goben zamuje gyaran gashin kuwa ni fa so nake ma ayi min kitso gashina sai karyewa yake gara naki shi baya komai,
kar gashin yagama gwaguyewa."
"Eh zamuje."
"To Allah ya kaimu."
ta fice ta koma sashin su.
Washegari da wuri Miemie ta gama shiri ta biyo wa Feeryal suka fito bayan Aunty ta gama yi musu kashe din su dawo da wuri.
suna hanyar su na zuwa parking lot Ameerah ta hange su.
murya ta d'aga
"Ke Miemie tsaya-tsaya-tsaya."
Miemie ta juyo tana dalla mata harara dan tasan bai wuci halin nata na rashin mutunci zatayi mata ba.
Ameerah ta karaso in da suke ta harare su sama da kasa sannan ta ce
"Da kika cewa su Unaisa su karo ashobe na mutum d'aya, ke zaki sa kala goma iri d'aya da naki da wanda za'a karon."
"Ina ruwan ki meye damuwar ki idan zan sa duka, idan kuma ma wata zan bawa kina da matsala ne,
ko akwai sisin ki a cikin kud'in siyan kayan,
Daddy ne me bada kud'in ko ke da kika titsiye ni kina tambaya ta."
"Ai nasan bai wuce ma wannan Aljanar kika sa ba, to tunda kud'in bana uban ta bane baza a kawo da ita ba,
ta had'a dangi da Ya Abdurrahim d'in ne da zatayi ashoben bikin sa,
to bama son gayyan sod'i, ta tsaya a matsayin ta dangin sa ne zasuyi ashoben bikin sa ba bare 'ya'yan tsintuwa ba."
Feeryal tayi murmushin takaici taja hannun Miemie ta ce
"Muje Miemie."
Miemie ta fisge hanun tana cewa
"Ke kam kin yi asara Ameerah haka zaki kare da gori, idan kikace zakiyi min ni wlh farfasa miki baki zanyi 'yar rainin wayo."
"Miemie muje dan Allah, ki rabu da ita."
Feeryal ta fad'a tana kuma ruko ta.
Ameerah ta waiga gefe da sauri ta isa bayan mota ta sunkuya ta d'auko magen Hajiya da ke kwance a gindin mota, ta jefawa Feeryal a jiki tana gad'in
"Munafuka idan bata rabu da ni ba ya zatayi da ni."
Wani irin uban ihu Feeryal ta kurma tare da kankame jikinta dake cirawa,
nan da nan kwayar idanunta suka sauya, tayi wani irin yanke jiki ta rid'u a kasa, tare da kuma kwalla kara ta zare gyale da d'ankwalin kanta ta yamusa gashin kanta.
tayi wani irin mikewa ta shako wuyan Ameerah.........!
11
Wani irin damka tayi wa wuyan Ameerah, tana wani irin gurnani.
idon Ameerah ya firfito, ta d'aga hanu kafafaka kamar kaza a cikin ruwa ta rike hanun Feeryal tana ja tayi-tayi ta iya b'anb'are hannunta a wuyan ta ta gagara.
ganin yadda Ameerah ta ke fafutukan niman numfashi, da sauri Miemie ta ce
"Sake ta Feeryal yau kin nuna mata shiru shiru ba tsoro bane gudun magana ne, kyale ta mu tafi wannan ya zame mata darasi in ita mai gane wa ce,
in kuma bata gane ba gaba a kuma ankarar da ita."
da sauri Miemie ta shiga kokarin janye ta, sai ji tayi kamar dusi take tab'awa.
"Feeryal kyale ta sake ta haka."
tafad'a tana jan hannunta dake wuyan Ameerah, amma ko gizau hannun ta baiyi ba.
da sauri ta dube ta cike da mamakin yadda taji takasa iya b'anb'are hannunta dake wuyan Ameerah.
da karfe ta d'ago kanta dake sunkuye gashin kanta ya rufe fuskarta.
a razane Miemie tayi baya ganin kwayar idanunta da suka sauya izuwa na ban tsoro.
Da gudu ta juya tana fad'in
"Me gadi security Feeryal Ameerah kuzo dan Allah wlh ba ita ba ce ba Feeryal ba ce!."
gaba d'aya ta kid'ime, tayi bakin get a guje tana kiran security.
Nabila da Sahla da komai ya faru a kan idon su dan tare suke da Ameerah dama, su suka tsaya jiranta ita kuma ta karaso ciwa su Miemie mutunci.
suka juya da gudu sukayi sashin Mommy suna fad'in
"Wayyo Allah Mommy Feeryal zata kashe Ameerah."
Mommy ta fito a hargitse dai-dai sanda Security suma suke karasowa gurin.
Aunty ma ta iso a bujajan Baba Rabi ta sanar mata da abin da ke faruwa.
Security suka bugawa Feeryal tsawa sukace
ta sake ta.
ganin bata da niyyar sakin ta,
ga yadda numfashin Ameerah ke yi kamar zai bar jikin ta, suka shiga kokarin jan Feeryal da jan hannunta a wuyan ta.
amma ko gizau basu iya ko da jijjigata ba.
Mommy ta ce
"Wayyo Allah shegiya mayya zata kashe min yarinya."
tayi kukan kura
tashiga dukan Feeryal da hanu bibbiyu ta baya tana fad'in
"Mayya sake ta kashe ta zakiyi."
wani irin sa kafa tayi ta baya ta angiza Mommy sai ga Mommy a kasa shirim, ta kawo ihu ta saka, tana dafe bayanta.
security hud'u sukayi kan Feeryal sukayi sukayi su iya kwace Ameerah a hannunta suka kasa.
Aunty da hankalin ta yayi mummunar tashi
ta zo ta gaban Feeryal tana fad'in
"Kuyi hakuri dan girman Allah ku sake ta na gama ku da Allah, kar ku ja mana masifa."
"Ai ita ce masifar babban annoba wayyo Allah mun shiga uku zata kashe 'yar gida, wayyo jama'a ku kawo mana d'auki za'ayi kisa."
Umma Karima da rahoto ya kaimata ta iso yanzu take fad'a.
ta ci gaba da fad'in
"Ku harbeta da bindiga idan bata sake ta ba, kuna gani zata kashe ta, dalla ku kashe mara amfani."
sai kuma ta juya da gudu tayi sashin Daddy tana ihu.
Ta fad'o cikin parlour'n Daddy tana fad'in
"To Alhaji gashi can za'ayi kisa a cikin gidan ka,
ka aje gamasheka ta bunkasa tafara cire wuyan 'yan gida,
ga mayyar Aljanar 'yarnan can ta makure wuyan Ameerah har jini na fita, ko numfashi bata yi wata kila ma ta mutu yanzu,
wani irin bala'i ne wannan ka ajiye mana a cikin gida."