Sashe 15
Feeryal Part 2 Complete Hausa Novel.t · about 8 min read
Abdurrahim ta hango yana shigowa da alama daga masallaci ya fito, da sauri ta tare shi tana cewa
"Dan Allah Abdurrahim ka taimake ni Feeryal ba lafiya kaje ka duba ta, kwana tayi bata rumtse ba, jikin ta ya yi zafi sosai,
ina ta kiran Dr tun jiya har yanzu bai zoba, ka tai maka dan Allah."
d'an jim ya yi ganin irin magiyar da take masa ya ginjina kai alamar zai je. da sauri ta juya ta koma ciki,
shi kuma ya wuce side d'in sa yana shiga ya haye gado ya kwanta......!
Mommyn Twins ce
10
Ganin shiru-shiru bai zoba Aunty ta kira sa a waya.
kiran wayar ne ya tashe sa daga baccin da ya fara.
gajeren tsaki yaja, kana ya mike zaune ya yi mika tare da yin salati.
ya zura takalmansa ya mike tsaye ya ja bedside ya d'ibi abubuwan da zai bukata ya zura cikin aljuhun jallabiyar jikin sa, kana ya fita ya nufi sashin Aunty.
a bakin kofar parlour suka had'u ta fita zuwa da kanta ta kira shi.
da sauri Aunty ta juya tana cewa
"Yauwa Abdurrahim dan Allah ka duba min ita."
baiyi magana ba yabi bayanta dan yana mugun jin nauyin ta.
Feeryal na kwance cikin bargo.
Aunty ta hayo gadon tana cewa
"Feeryal ta shi ga shi za'a duba ki,
karaso dan Allah Abdurrahim."
ta janye bargon, idanun ta a lumshe bawai ko dun tana bacci ba sai dan jirin da take ji.
a sannu ya toko d'akin hannayen sa suna nad'e a kirjin sa.
ya karaso bakin gadon,
kallo d'aya ya yi mata ya d'auke idanun sa. a hankali ya sauke hannayen sa da suke nad'e a kirjin sa.
kana a sannu yakai yatsun sa biyu kan goshin ta.
patt!. haka taji kirjinta ya buga san da yatsar sa ya sauka kan goshinta,
da kyarfi ta rumtse idanunta tare da jan numfashi.
Ya janye hannunsa tare da zurashi cikin aljuhu ya zaro allura ya fasa ya zuko shi cikin Syringe.
"Gyara Feeryal ayi miki allura ba sai kin tashi ba a kwancen ma za'a iya yi ko Abdurrahim."
Aunty ta fad'a tana duban shi.
kai ya gyad'a batare da ya yi magana ba.
wani irin zabura tayi jin an ambaci sunan allura.
murya na rawa ta ce
"Aa Ammie ni dai bana so kar ayi min."
had'iye ragowar maganar tayi ganin shi tsaye a gaban ta.
hannu takai ta mussuke idanunta zaton ta gizo ne.
jin Aunty tana cewa
"Ke ki tsaya da'alla abin da ba zafi Abdurrahim yi mata kaji."
huf ta mike tsaye ta tsaya da kafafunta a kan gadon, ta matsa can karshen gado tana yarfe hannu da fad'in
"Wayyo Allah Ammie naji sauki kar a min."
"Ke dalla bana son shiririta kina b'ata masa lokaci fa."
ta janyo ta ta zille tare da fashewa da kuka tana yarfe hannu
"Ammie dan Allah dan Allah Ammie kar a yi min naji sauki ma."
ta rika yarfe hannu tana buga kafa kan katifa.
Aunty ta ruko ta da karfi, ihu ta fasa tana tirjewa.
gajeren tsaki ya ja cike da kosawa ya mika hanu ya fisgo ta ta fad'o kan kafar Aunty, ta rirtike ta, itama ta kankame ta gamgam tare da b'oye fuskarta jikin Aunty.
tsaki ya kuma ja badun nauyin Aunty da yake ji ba da babu abin da zai sa yazo bare har a tsaya ana masa wannan haukar.
kwafa ya yi afili Aunty ta fahimci ransa ya b'aci, ta bugawa Feeryal tsawa
"Idan baki tsaya ba za'a barki da ciwon ki kiyi ta fama, kina hauka ne allura kawai kamar cire ran ki za'ayi haba dan Allah,
yi hakuri Abdurrahim kayi mata."
ta d'an ja sket d'in ta kasa
Baki ya tab'e ya d'an matso ya nitsa allurar ta saman pant d'in ta.
kara ta kurma ta kai hannu ta rike nashi da ke rike da allurar ya bige hannuta bayan ya matse ruwan allurar ya zare shi a jikin ta, yana mai dad'a gimtse fuskarsa, ya cika har wuya.
da kyar ta tsaya a ka kara mata d'aya,
"A sa mata ruwan sanyi a jikin ta."
ya fad'a a takaice.
Aunty ta d'ago ta a jikin ta ta sauka ta shige bayi da sauri.
Feeryal kukan allura har da majina.
ganin Aunty ta shige bayi itama ta mike da sauri ta duro a gadon.
tana d'aga kafa taji abu ya cake ta a bayan hanu.
kara ta kwalla tare da d'ago hannun tana yarfe shi.
wani kallo ya wurga mata sannan ya saki allurar dake hannunsa kasa,
"Stupid girl." ya fad'a kana ya juya ya fice a d'akin
Aunty ta fito da sauri tana fad'in
"Feeryal lafiyar ki tun da an gama ina shike nan ko sai kin tsaya shiririta,
me ya sami hannun naki kike tallafe shi sai kace a hannun aka yi miki allurar."
Aunty ta ruko hannun nata tana cigaba da cewa
"Um kin gani karin gardamar ki har kin ji ciwo a hannu gashi har ya d'an fidda jini, sannu zauna na sa miki towel zaki dad'a jin dad'i, jikin naki ya yi zafi sosai baki ji ya ce asa miki ruwan sanyi ba."
Feeryal bata iya magana ba sai matsar kwalla take.
Aunty ta taimaka mata ta cire kayan jikin ta, ta d'auko mata wani riga bes da wandon sa iya guiwa ta saka, kana ta rika jika towel tana shafa mata a jikin ta.
har sai da taji jikin ya yi sanyi kafin zuwa lokacin kuwa bacci ya d'auke ta.
Aunty ta fita taje ta kama aiki akai-akai take shigowa dubata, sosai jikin ta ya yi sanyi ta jima sosai tana bacci..
"Ya shugaba na akwai tsoron wani mai tsanani a tare da ita, gata a kwance cikin jinya sakamakon tsoron nashi."
waziri Kutup ya yi maganar yana zubewa gaban sarki Aljani Matip tare da d'aura ruwan madubin ganin zahiri daga rayuwar ta bisa kafar sarki Aljani Matip.
kura mata ido ya yi sosai sannan ya ce
"Aje a wanke mata fuskarta da ruwan zuzirr, akwai bak'in yana da magauta masu neman ta sukayi jifa ya fad'o fuskarta,
shi yasa idan tayi duba a gareshi firgici yake dirar mata,
a wancan lokacin malam Buba Mani bai san da ragowa a goshin ta ba, wan da ya gani kawai ya iya cirewa."
kasa waziri Kutup ya yi da kansa yana cewa
"A gafarce ni ya shugaba na amma me yasa sai a kansa take shiga wannan yanayin, ga sauran bil'adam kuma ba haka ba."
murmushi sarki Matip ya yi sannan ya ce
"Magauta bincike suke babu dare babu rana sun watsa taurarin su ta ko ina domin cikar burin su,
tauraru ya fad'a a kansa duk da hasken shi ya disashe taurarun su amma yana tasiri a jikin sa,
shi yasa take jin hakan game da shi,
a wanke mata fuska da ruwan zuzirr na karkashin teku,
ganin da zata kuma yi masa zai kona taurarun su dake razanar da ita,
wanda yake a matsayin tarko gare ta, za'a shafe sammanin su da suke jin sun kusa gado inda take, duk da taurarun nasu baya da kaifin tasiri a kanshi,
har yanzu lalub'e suke cikin duhu."
"Na d'auki umurni ya shugaba na."
Waziri Kutup ya mike domin isar da umurnin da aka masa..
Sai bayan sallar la'asar ta farka.
tana bud'e ido ta saki murmushi ganin Chuchu da Chulu a kusa da ita.
Chuchu na rike da hannunta tana share mata d'an guntun jinin da ya fito kan bayan hannunta.
mikewa ta yi ta zauna tana fad'in
"Laa Chuchu Chulu kunzo ne har kun dawo daga tafiyar?."
suma murmushin suka mayar mata, Chulu ta ce
"Dawowar mu ke nan, muka biyo nan,
baki da lafiya kinji sauki ko mu baki magani."
"Naji sauki kaina ke min ciwo kad'an kad'an yanzu."
wani d'an karamin tandu mai murfi ta ciro, ta kwance marfin ta ce
"Kawo hannun ki na zuba miki ki wanke fuskarki zaki ji kan ya dai na miki ciwo."
ta mika hannu ta tsiya ya mata har sau uku tana wanke fuskarta da shi..
fuska ta yamutsa tana
kallon hannunta dake rike a hannun Chuchu sannan ta ce
"Wannan Sahab d'in nan ne ya caka min allura a gurin."
Chuchu ta ce
"Kina so ki rama?."
ido ta d'an waro ta ce
"Tsoro yake bani kuma duka ya ke yi fa, baku ga yadda ya yi wa su Miemie ba."
"Ki dai na tsoron shi ba ga munan ba zamu taya ki,
idan ya ce zai duke ki zamuyi mishi irin na Mommyn shi,
kin mance tun da data tab'a dukan ki muka rike mata kafa ta kasa iya tafiya, to haka zamuyi masa shima."
Dariya ta fashe da shi tuno da abin da suka tab'a yi wa Mommy tun tana karama.
sai da dariyar ta yi tare da cewa
"To amma ai kunce shi kun kasa iya yi masa komai, shifa mugu ne baku ga yadda ya caka min allura ba."
"Ina abin da muka baki ki sa masa a jikin san nan?."
"Yana can cikin wardrobe nifa tsoro nake ji, a ina ma zan ganshi na saka masan."
"Duk in da kika ganshi ki san yadda zakiyi ya tab'a jikin sa, ta nan ne kad'ai zamu sami damar iya yi masa wani abu,
idan ba haka ba to mu ba zamu iya yi masa ko mai ba ba zamu iya zuwa jikin sa ba,
mun d'au ki wancan a in da kika ajiye,
amma zamu baki wani."
d'an shiru tayi tana tunani ta ya za a yi ta iya hakan.
"Babu abin da zai miki ki daina tsoron sa mu zamu taya ki kinji."
kai ta gyad'a.
Chulu ta mika mata wani jan ganye guda d'aya ta ce
"Idan wannan ya tab'a jikin sa zamu iya zuwa jikin sa, bai isa ya yi miki wani abu ba zamu rama miki."
ta karb'a tana murmushi nan take ta kudiri aniyar saka masa a jiki, duk da bata san ta in da zata fara ba.
Har kusan magariba suna tare sai da Aunty ta shigo tashinta ta tashi magariba yayi tayi wanka,
kafin su Chuchu suka tafi.
"Dan Allah Abdurrahim ka taimake ni Feeryal ba lafiya kaje ka duba ta, kwana tayi bata rumtse ba, jikin ta ya yi zafi sosai,
ina ta kiran Dr tun jiya har yanzu bai zoba, ka tai maka dan Allah."
d'an jim ya yi ganin irin magiyar da take masa ya ginjina kai alamar zai je. da sauri ta juya ta koma ciki,
shi kuma ya wuce side d'in sa yana shiga ya haye gado ya kwanta......!
Mommyn Twins ce
10
Ganin shiru-shiru bai zoba Aunty ta kira sa a waya.
kiran wayar ne ya tashe sa daga baccin da ya fara.
gajeren tsaki yaja, kana ya mike zaune ya yi mika tare da yin salati.
ya zura takalmansa ya mike tsaye ya ja bedside ya d'ibi abubuwan da zai bukata ya zura cikin aljuhun jallabiyar jikin sa, kana ya fita ya nufi sashin Aunty.
a bakin kofar parlour suka had'u ta fita zuwa da kanta ta kira shi.
da sauri Aunty ta juya tana cewa
"Yauwa Abdurrahim dan Allah ka duba min ita."
baiyi magana ba yabi bayanta dan yana mugun jin nauyin ta.
Feeryal na kwance cikin bargo.
Aunty ta hayo gadon tana cewa
"Feeryal ta shi ga shi za'a duba ki,
karaso dan Allah Abdurrahim."
ta janye bargon, idanun ta a lumshe bawai ko dun tana bacci ba sai dan jirin da take ji.
a sannu ya toko d'akin hannayen sa suna nad'e a kirjin sa.
ya karaso bakin gadon,
kallo d'aya ya yi mata ya d'auke idanun sa. a hankali ya sauke hannayen sa da suke nad'e a kirjin sa.
kana a sannu yakai yatsun sa biyu kan goshin ta.
patt!. haka taji kirjinta ya buga san da yatsar sa ya sauka kan goshinta,
da kyarfi ta rumtse idanunta tare da jan numfashi.
Ya janye hannunsa tare da zurashi cikin aljuhu ya zaro allura ya fasa ya zuko shi cikin Syringe.
"Gyara Feeryal ayi miki allura ba sai kin tashi ba a kwancen ma za'a iya yi ko Abdurrahim."
Aunty ta fad'a tana duban shi.
kai ya gyad'a batare da ya yi magana ba.
wani irin zabura tayi jin an ambaci sunan allura.
murya na rawa ta ce
"Aa Ammie ni dai bana so kar ayi min."
had'iye ragowar maganar tayi ganin shi tsaye a gaban ta.
hannu takai ta mussuke idanunta zaton ta gizo ne.
jin Aunty tana cewa
"Ke ki tsaya da'alla abin da ba zafi Abdurrahim yi mata kaji."
huf ta mike tsaye ta tsaya da kafafunta a kan gadon, ta matsa can karshen gado tana yarfe hannu da fad'in
"Wayyo Allah Ammie naji sauki kar a min."
"Ke dalla bana son shiririta kina b'ata masa lokaci fa."
ta janyo ta ta zille tare da fashewa da kuka tana yarfe hannu
"Ammie dan Allah dan Allah Ammie kar a yi min naji sauki ma."
ta rika yarfe hannu tana buga kafa kan katifa.
Aunty ta ruko ta da karfi, ihu ta fasa tana tirjewa.
gajeren tsaki ya ja cike da kosawa ya mika hanu ya fisgo ta ta fad'o kan kafar Aunty, ta rirtike ta, itama ta kankame ta gamgam tare da b'oye fuskarta jikin Aunty.
tsaki ya kuma ja badun nauyin Aunty da yake ji ba da babu abin da zai sa yazo bare har a tsaya ana masa wannan haukar.
kwafa ya yi afili Aunty ta fahimci ransa ya b'aci, ta bugawa Feeryal tsawa
"Idan baki tsaya ba za'a barki da ciwon ki kiyi ta fama, kina hauka ne allura kawai kamar cire ran ki za'ayi haba dan Allah,
yi hakuri Abdurrahim kayi mata."
ta d'an ja sket d'in ta kasa
Baki ya tab'e ya d'an matso ya nitsa allurar ta saman pant d'in ta.
kara ta kurma ta kai hannu ta rike nashi da ke rike da allurar ya bige hannuta bayan ya matse ruwan allurar ya zare shi a jikin ta, yana mai dad'a gimtse fuskarsa, ya cika har wuya.
da kyar ta tsaya a ka kara mata d'aya,
"A sa mata ruwan sanyi a jikin ta."
ya fad'a a takaice.
Aunty ta d'ago ta a jikin ta ta sauka ta shige bayi da sauri.
Feeryal kukan allura har da majina.
ganin Aunty ta shige bayi itama ta mike da sauri ta duro a gadon.
tana d'aga kafa taji abu ya cake ta a bayan hanu.
kara ta kwalla tare da d'ago hannun tana yarfe shi.
wani kallo ya wurga mata sannan ya saki allurar dake hannunsa kasa,
"Stupid girl." ya fad'a kana ya juya ya fice a d'akin
Aunty ta fito da sauri tana fad'in
"Feeryal lafiyar ki tun da an gama ina shike nan ko sai kin tsaya shiririta,
me ya sami hannun naki kike tallafe shi sai kace a hannun aka yi miki allurar."
Aunty ta ruko hannun nata tana cigaba da cewa
"Um kin gani karin gardamar ki har kin ji ciwo a hannu gashi har ya d'an fidda jini, sannu zauna na sa miki towel zaki dad'a jin dad'i, jikin naki ya yi zafi sosai baki ji ya ce asa miki ruwan sanyi ba."
Feeryal bata iya magana ba sai matsar kwalla take.
Aunty ta taimaka mata ta cire kayan jikin ta, ta d'auko mata wani riga bes da wandon sa iya guiwa ta saka, kana ta rika jika towel tana shafa mata a jikin ta.
har sai da taji jikin ya yi sanyi kafin zuwa lokacin kuwa bacci ya d'auke ta.
Aunty ta fita taje ta kama aiki akai-akai take shigowa dubata, sosai jikin ta ya yi sanyi ta jima sosai tana bacci..
"Ya shugaba na akwai tsoron wani mai tsanani a tare da ita, gata a kwance cikin jinya sakamakon tsoron nashi."
waziri Kutup ya yi maganar yana zubewa gaban sarki Aljani Matip tare da d'aura ruwan madubin ganin zahiri daga rayuwar ta bisa kafar sarki Aljani Matip.
kura mata ido ya yi sosai sannan ya ce
"Aje a wanke mata fuskarta da ruwan zuzirr, akwai bak'in yana da magauta masu neman ta sukayi jifa ya fad'o fuskarta,
shi yasa idan tayi duba a gareshi firgici yake dirar mata,
a wancan lokacin malam Buba Mani bai san da ragowa a goshin ta ba, wan da ya gani kawai ya iya cirewa."
kasa waziri Kutup ya yi da kansa yana cewa
"A gafarce ni ya shugaba na amma me yasa sai a kansa take shiga wannan yanayin, ga sauran bil'adam kuma ba haka ba."
murmushi sarki Matip ya yi sannan ya ce
"Magauta bincike suke babu dare babu rana sun watsa taurarin su ta ko ina domin cikar burin su,
tauraru ya fad'a a kansa duk da hasken shi ya disashe taurarun su amma yana tasiri a jikin sa,
shi yasa take jin hakan game da shi,
a wanke mata fuska da ruwan zuzirr na karkashin teku,
ganin da zata kuma yi masa zai kona taurarun su dake razanar da ita,
wanda yake a matsayin tarko gare ta, za'a shafe sammanin su da suke jin sun kusa gado inda take, duk da taurarun nasu baya da kaifin tasiri a kanshi,
har yanzu lalub'e suke cikin duhu."
"Na d'auki umurni ya shugaba na."
Waziri Kutup ya mike domin isar da umurnin da aka masa..
Sai bayan sallar la'asar ta farka.
tana bud'e ido ta saki murmushi ganin Chuchu da Chulu a kusa da ita.
Chuchu na rike da hannunta tana share mata d'an guntun jinin da ya fito kan bayan hannunta.
mikewa ta yi ta zauna tana fad'in
"Laa Chuchu Chulu kunzo ne har kun dawo daga tafiyar?."
suma murmushin suka mayar mata, Chulu ta ce
"Dawowar mu ke nan, muka biyo nan,
baki da lafiya kinji sauki ko mu baki magani."
"Naji sauki kaina ke min ciwo kad'an kad'an yanzu."
wani d'an karamin tandu mai murfi ta ciro, ta kwance marfin ta ce
"Kawo hannun ki na zuba miki ki wanke fuskarki zaki ji kan ya dai na miki ciwo."
ta mika hannu ta tsiya ya mata har sau uku tana wanke fuskarta da shi..
fuska ta yamutsa tana
kallon hannunta dake rike a hannun Chuchu sannan ta ce
"Wannan Sahab d'in nan ne ya caka min allura a gurin."
Chuchu ta ce
"Kina so ki rama?."
ido ta d'an waro ta ce
"Tsoro yake bani kuma duka ya ke yi fa, baku ga yadda ya yi wa su Miemie ba."
"Ki dai na tsoron shi ba ga munan ba zamu taya ki,
idan ya ce zai duke ki zamuyi mishi irin na Mommyn shi,
kin mance tun da data tab'a dukan ki muka rike mata kafa ta kasa iya tafiya, to haka zamuyi masa shima."
Dariya ta fashe da shi tuno da abin da suka tab'a yi wa Mommy tun tana karama.
sai da dariyar ta yi tare da cewa
"To amma ai kunce shi kun kasa iya yi masa komai, shifa mugu ne baku ga yadda ya caka min allura ba."
"Ina abin da muka baki ki sa masa a jikin san nan?."
"Yana can cikin wardrobe nifa tsoro nake ji, a ina ma zan ganshi na saka masan."
"Duk in da kika ganshi ki san yadda zakiyi ya tab'a jikin sa, ta nan ne kad'ai zamu sami damar iya yi masa wani abu,
idan ba haka ba to mu ba zamu iya yi masa ko mai ba ba zamu iya zuwa jikin sa ba,
mun d'au ki wancan a in da kika ajiye,
amma zamu baki wani."
d'an shiru tayi tana tunani ta ya za a yi ta iya hakan.
"Babu abin da zai miki ki daina tsoron sa mu zamu taya ki kinji."
kai ta gyad'a.
Chulu ta mika mata wani jan ganye guda d'aya ta ce
"Idan wannan ya tab'a jikin sa zamu iya zuwa jikin sa, bai isa ya yi miki wani abu ba zamu rama miki."
ta karb'a tana murmushi nan take ta kudiri aniyar saka masa a jiki, duk da bata san ta in da zata fara ba.
Har kusan magariba suna tare sai da Aunty ta shigo tashinta ta tashi magariba yayi tayi wanka,
kafin su Chuchu suka tafi.