Sashe 10
Feeryal Part 2 Complete Hausa Novel.t · about 8 min read
Hajiya bata nan taje ta'aziyya a yelwa, sai da tayi kwana uku kafin ta dawo,
tun bata hutaba labari ya isar mata.
ta ce wa Ajmal da ya shigo yi mata sannu da dawowa ya kira mata Daddy.
shiko ya mike ya nufi kofar fita yana fad'in
"Kijira ya dawo mana."
"Kai Ajimi iya shege zaka kawo min, ka kira min uban ka ka ce na jira shi, gaka min iya shegen banza,
ban san me Abubakar yake nufi ba,
daga ce ta d'an zauna na wani lokaci kafin a gama bincike,
shike nan sai ta shari gindi ta zauna har malikiyaumiddini, to bari ya dawo ya same ni zaman nata ya isa haka ta kara gaba,
nagaji da gayyar tsiya arna gun idi."
Da daddre Daddy da ya shigo gaishe ta ko zama baiyi ba ta taresa da maganar.
ta ce gobe gobe yasata a mota ta koma inda ta fito.
da kyar Daddy ya samu ya lallab'a ta ya ce saura kiris a gama binciken ana gamawa zata koma, Hajiya ta rika bala'i haka dai ya tashi ya barta
★★�
Yau Feeryal tun da yamma take side d'in su Miemie,
har bayan sallar isha, tun kan magriba taso komawa b'angaren su Miemie ta ki barinta.
har dai da sukayi sallar isha kafin suka fito ta rako ta.
suna tafe suna d'an hirar su, suka taho ta kofar b'angaren su Ajmal.
Zaraddin da tun fito warsu a kan idon sa yana hango su ta saman bene, kafin su karaso ya yi saurin sauko wa.
suna isowa ya fito yana wage baki.
Miemie ta ce
"La Ya Zaraddin ashe kana nan, kwna biyu ina ka shiga ne bana ganin ka."
kirjinsa ya shafa yana bin Feeryal da wani irin mayataccen kallo ya ce
"Tafiya nayi d'azu na dawo."
murmushi Feeryal tayi tana janye idanunta daga kallon da ya ke mata cikin siririyar muryarta mai kama da mai yin shagwab'a ta ce
"Sannu da dawowa Ya Zaraddin ka dawo lafiya."
wani irin lumshe ido ya yi ya wani rungume hannunsa a kirjinsa da ke ji ina ma ace ta fad'o cikin sa,
komai na yarinyar ya had'u babu makusa ko kad'an.
ya karkace kai yana cigaba da aika mata irin kallon nan nasa sannan ya ce
"Daku na fara had'uwa da na shigo ku yakamata ku fara kunce jaka ku kwashi tsaraba,
musamman ke da kikayi min barka da dawowa lafiya."
ya yi maganar idanunsa akan Feeryal.
"Oh lallai ma Ya Zaraddin d'in nan amma ai ni na fara tambayar ka banganka ba kwana biyu."
Miemie tayi maganar tana d'aga kiran Ammah da ya shigo wayarta.
"To Ammah."
ta fad'a tana sauke wayar.
ta dubi Feeryal tana fad'in
"Ki karasa bari naje na bawa Ammah ATM d'in ta zata aiki direba kuma ni na aje mata shi wai bata gani ba, ina zuwa yanzu."
Feeryal ta gyad'a kai.
Miemie ta juya da sauri.
Feeryal ta d'aga kafa tana kokarin barin gurin,
da sauri Zaraddin ya ce
"Ah ina kuma zakije tun baki karb'i tsarabar ki ba,
ai kin cancanci tsaraba mai tsoka ke da kikayi min fatan na dawo lafiya ai dole na saka miki, taho muje ki karb'i tsaraba sai kinso ki samma Miemie."
ya juya ya shige kofar dide d'in su, sannan ya juyo ya ce
"Zo mana zo muje ki karb'a."
ya yi maganar yana gwada mata hanya.
a hankali ta d'aga kafarta da zummar biyo shi.
wata mota da ta shigo gidan yanzu fitilar motar ta hasko mata ido.
da sauri ta kai hannunta biyu ta kare fuskata,dan har jijiyar idanunta sai da ya amsa sakamakon hasken nan.
Tsawon sakanni 20 wutar motar bata janye a kanta ba.
da sauri ta matsa gefe tare da janye hannayen ta kan fuskarta, sai a sannan ta sami damar iya bud'e idanunta.
abin da ya bata mamaki motar tana tsaye batayi gaba ba ba'a kuma kashe wutar motar ba.
maganar Miemie ta juyo a bayan ta
"Feeryal muje gashi har na dawo."
Miemie tayi gaba Feeryal ta biyo ta, da sauri Miemie ta d'an dawo da baya ta ruko hannun Feeryal ta ce "Motar Ya Abdurrahim ce wannan zo mubi ta can.......!
*Babu editing a karanta da hakuri*
Miemie ta janyo hannunta suka bi gefe.
yana zaune cikin motar ya jingina bayan sa jikin sit idanunsa akan waya yana latsawa.
kallo d'aya tayi masa tayi saurin janye idanunta sakamakon jin wani irin mummumar fad'uwar gaba,
sau uku ke nan tun da take gidan ta tab'a ganin sa, had'uwarsu ta farko a sashin Hajiya da yake tambayar ta wai ita aljana ce ko,
sai kuma ranar da sukaje dinner sukayi dare, sai kuma yau.
ganin da tayi masa sau uku duk abu guda take ji mummynar fad'uwar gaba mai had'e da tsoro.
duk da ba su yake kallo ba idanunsa na kan wayar hannunsa, amma gaba d'aya ta rud'e ganin irin dukan da ya yi wa su Miemie ya dad'a kara mata tsoron sa.
da karfi ta damke hannun Miemie ta kara saurin ta.
Suna shiga parlour Aunty ta wani sauke numfashi mai sauti.
Miemie ta dube ta ta ce
"Ya dai Feeryal?."
kai ta girgiza tare da kakalo murmushi.
A parlour suka tadda Aunty da Daddy zaune suna kallo tare da d'an tab'a hira.
suka karaso suka gaishe su, Daddy ya dubi Miemie ya ce
"Mamana mutumiyar taki taci abinci kuwa?."
Aunty ta ce
"Wani abincin cake da yogurt ba tana da abincin da ya wuce su ne."
kai Feeryal ta langwab'e ta ce
"Naci tuwo fa Daddy ko Miemie."
Miemie tayi murmushi ta ce
"Taci Daddy tare ma muka ci."
"Yauwa ko ke fa gara dai a rika had'awa da mai nauyin, idan iska ya taso kinyi nauyi bazai iya kada ke ba."
cewar Daddy cikin zolaya.
dariya duk sukayi.
Daddy ya mike ya nufi bedroom ya na cewa
"To sai da safen ku."
zama sukayi suka bud'e sabon hira, har wajen karfe goma kafin Miemie ta yi musu sallama ta tafi.
Feeryal ma ta mike dan bacci ne cike a idanunta ta shige bedroom d'in ta.
Aunty ta je ta kulle kofar parlour kana ta dawo ta kashe TV sannan ta rage wutan parlour ta shige d'aki.
Ta taras da Daddy ya yi nisa a baccin sa, ta rage kayan jikinta ta sa na bacci kana ta shige bayi ta d'auri al'wala ta fito ta haye gadon itama ta kwanta gefen sa bayan tayi addu'a.
wani irin zabura Daddy ya yi ya mike zaune tare da fad'in
"Innailaihirraji'un!."
ya dafe kirjinsa jikinsa na cirawa.
a razane Aunty ta mike ta ruko shi tana fad'in
"Subhanallahi ya ya dai Daddy me ya faru bakayi addu'a bane ka kwanta."
kai ya girguza mata yana sauke numfarfashi tare da share gumin da ya karyo masa.
gaba d'aya Aunty ta rud'e a 'yan kwanakin nan ta lura a duk sanda ya kwanta haka zai farka a birkice.
tsawon shekaru ashirin da d'ori bayan auren su ya yi ta fama da irin wannan matsalar wacce damuwar haka takai ga tab'a masa lafiyar zuciya,
a wancan lokacin bayan auren su da wata biyar yasoma irin wannan mummunar mafarkin,
sai da ya shari shekaru goma yana fama da matsalar,
da taimakon Allah da taimakon addu'o'in da Aunty take tayashi yasami sassaucin lamarin,
damuwa da irin wahalar da yake sha idan ya kwanta bacci,
ta kai ga tab'a masa lafiyar zuciya, da har gobe yake shan magani.
sai gashiga a 'yan kwanakin nan abun ya dawo yanzu ba bu dare babu rana daga zaran ya kwanta bacci zai farka a firgice.
Ganin yadda gaba d'aya hankalin Aunty ya tashi, a hankali ya kwantar da kansa jikin kafad'ar ta yana sauke numfashi.
cikin shiga damuwa sosai Aunty ta ce
"Daddy tashi kayi al'wala muyi sallah babu abin da yafi karfin Allah babu abin da zai faru da yardar Allah."
Tarika karfafashi har ya mike yaje ya d'auro al'wala,
yafito ya taras har ta shinfid'a musu sallaya ta sa hijabi tana tsaye tana jiran sa.
shi ya jasu sallar suna idarwa taje ta d'auko musu Alkur'ani.
sun jima sosai suna karatu cikin suratul BAQARA, sai da ta tabbatar da nusuwa tare da shi,
har yana karatun yana gyangyad'i,
ta gyara ta mike kafafunta ta ce
"Kwanta Daddy."
ya mike kan sallayar yayi pillow da kafarta.
a hankali take karatun cikin kasa da murya tana yi tana shafa kansa, nan da nan bacci ya yi gaba da shi.
ya yi bacci abadan kafin itama ta soma lumshe ido. ta rufe kur'anin kana ta jingina bayan da jikin gado a haka bacci ya d'auketa a zaune.
Har sai kusan asuba ya farka ya ganta zaune tana bacci.
kauna da tausayin ta suka dad'a shigarsa, ya mike ya ciccib'eta ya d'aurata a kan gado,
yana ajeta ta bud'e ido.
murmushi tayi masa cikin muryar bacci ta ce
"Daddy ashe da sauran ka har yanzu tun da ka iya d'aukata."
kumatun ta ya ja ya na fad'in
"Tun da ina da ke kam tsufa bata isa ta matso ni ba."
murmushi tayi masa ta gyara kwanciyar ta.
shiko ya shige bayi ya d'auro al'wala,
yafito ya haye sallaya yasoma gudanar da nafilfili.
sai da aka kira sallar asuba kafin ya tashe ta shikuma ya wuce masallaci.
Aunty na idar da sallah ta je ta tada Feeryal kafin ta koma tacigaba da adhkar.
Feeryal ko bayan ta idar da salla da karatun alkur'ani tayi kamar yanda kullum Aunty ke umurtar ta da tayi, tana shafa addu'a ta haye gado ta koma baccin ta.
ba ita ta farka ba sai wuraren karfe 11 da rabi.
Bayan tayi wanka ta shirya cikin doguwar rigar atamfa da ta amshi jikin ta.
ta fito ta wuce dinning ta tarar da Aunty a gun ta tanadar mata abin kaunar ta wato cake da yogurt.
ta bayan kujerar Aunty ta zo ta kwantar da kanta gefen kafad'ar ta cikin siririyar muryarta ta ce
"Ina kwana Ammie na."
Aunty ta shafa gefen fuskarta ta ce
"Lafiya lau 'yammatan Ammie antashi lafiya ya lalaci,
a rage lalacin nan gobe ke zakiyi mana breakfast idan Allah ya kaimu, yau ma tare zamu shiga kitchen anjima."
"To Ammie."
ta fad'a tana mikewa a jikin ta taja kujera ta zauna.
tun bata hutaba labari ya isar mata.
ta ce wa Ajmal da ya shigo yi mata sannu da dawowa ya kira mata Daddy.
shiko ya mike ya nufi kofar fita yana fad'in
"Kijira ya dawo mana."
"Kai Ajimi iya shege zaka kawo min, ka kira min uban ka ka ce na jira shi, gaka min iya shegen banza,
ban san me Abubakar yake nufi ba,
daga ce ta d'an zauna na wani lokaci kafin a gama bincike,
shike nan sai ta shari gindi ta zauna har malikiyaumiddini, to bari ya dawo ya same ni zaman nata ya isa haka ta kara gaba,
nagaji da gayyar tsiya arna gun idi."
Da daddre Daddy da ya shigo gaishe ta ko zama baiyi ba ta taresa da maganar.
ta ce gobe gobe yasata a mota ta koma inda ta fito.
da kyar Daddy ya samu ya lallab'a ta ya ce saura kiris a gama binciken ana gamawa zata koma, Hajiya ta rika bala'i haka dai ya tashi ya barta
★★�
Yau Feeryal tun da yamma take side d'in su Miemie,
har bayan sallar isha, tun kan magriba taso komawa b'angaren su Miemie ta ki barinta.
har dai da sukayi sallar isha kafin suka fito ta rako ta.
suna tafe suna d'an hirar su, suka taho ta kofar b'angaren su Ajmal.
Zaraddin da tun fito warsu a kan idon sa yana hango su ta saman bene, kafin su karaso ya yi saurin sauko wa.
suna isowa ya fito yana wage baki.
Miemie ta ce
"La Ya Zaraddin ashe kana nan, kwna biyu ina ka shiga ne bana ganin ka."
kirjinsa ya shafa yana bin Feeryal da wani irin mayataccen kallo ya ce
"Tafiya nayi d'azu na dawo."
murmushi Feeryal tayi tana janye idanunta daga kallon da ya ke mata cikin siririyar muryarta mai kama da mai yin shagwab'a ta ce
"Sannu da dawowa Ya Zaraddin ka dawo lafiya."
wani irin lumshe ido ya yi ya wani rungume hannunsa a kirjinsa da ke ji ina ma ace ta fad'o cikin sa,
komai na yarinyar ya had'u babu makusa ko kad'an.
ya karkace kai yana cigaba da aika mata irin kallon nan nasa sannan ya ce
"Daku na fara had'uwa da na shigo ku yakamata ku fara kunce jaka ku kwashi tsaraba,
musamman ke da kikayi min barka da dawowa lafiya."
ya yi maganar idanunsa akan Feeryal.
"Oh lallai ma Ya Zaraddin d'in nan amma ai ni na fara tambayar ka banganka ba kwana biyu."
Miemie tayi maganar tana d'aga kiran Ammah da ya shigo wayarta.
"To Ammah."
ta fad'a tana sauke wayar.
ta dubi Feeryal tana fad'in
"Ki karasa bari naje na bawa Ammah ATM d'in ta zata aiki direba kuma ni na aje mata shi wai bata gani ba, ina zuwa yanzu."
Feeryal ta gyad'a kai.
Miemie ta juya da sauri.
Feeryal ta d'aga kafa tana kokarin barin gurin,
da sauri Zaraddin ya ce
"Ah ina kuma zakije tun baki karb'i tsarabar ki ba,
ai kin cancanci tsaraba mai tsoka ke da kikayi min fatan na dawo lafiya ai dole na saka miki, taho muje ki karb'i tsaraba sai kinso ki samma Miemie."
ya juya ya shige kofar dide d'in su, sannan ya juyo ya ce
"Zo mana zo muje ki karb'a."
ya yi maganar yana gwada mata hanya.
a hankali ta d'aga kafarta da zummar biyo shi.
wata mota da ta shigo gidan yanzu fitilar motar ta hasko mata ido.
da sauri ta kai hannunta biyu ta kare fuskata,dan har jijiyar idanunta sai da ya amsa sakamakon hasken nan.
Tsawon sakanni 20 wutar motar bata janye a kanta ba.
da sauri ta matsa gefe tare da janye hannayen ta kan fuskarta, sai a sannan ta sami damar iya bud'e idanunta.
abin da ya bata mamaki motar tana tsaye batayi gaba ba ba'a kuma kashe wutar motar ba.
maganar Miemie ta juyo a bayan ta
"Feeryal muje gashi har na dawo."
Miemie tayi gaba Feeryal ta biyo ta, da sauri Miemie ta d'an dawo da baya ta ruko hannun Feeryal ta ce "Motar Ya Abdurrahim ce wannan zo mubi ta can.......!
*Babu editing a karanta da hakuri*
Miemie ta janyo hannunta suka bi gefe.
yana zaune cikin motar ya jingina bayan sa jikin sit idanunsa akan waya yana latsawa.
kallo d'aya tayi masa tayi saurin janye idanunta sakamakon jin wani irin mummumar fad'uwar gaba,
sau uku ke nan tun da take gidan ta tab'a ganin sa, had'uwarsu ta farko a sashin Hajiya da yake tambayar ta wai ita aljana ce ko,
sai kuma ranar da sukaje dinner sukayi dare, sai kuma yau.
ganin da tayi masa sau uku duk abu guda take ji mummynar fad'uwar gaba mai had'e da tsoro.
duk da ba su yake kallo ba idanunsa na kan wayar hannunsa, amma gaba d'aya ta rud'e ganin irin dukan da ya yi wa su Miemie ya dad'a kara mata tsoron sa.
da karfi ta damke hannun Miemie ta kara saurin ta.
Suna shiga parlour Aunty ta wani sauke numfashi mai sauti.
Miemie ta dube ta ta ce
"Ya dai Feeryal?."
kai ta girgiza tare da kakalo murmushi.
A parlour suka tadda Aunty da Daddy zaune suna kallo tare da d'an tab'a hira.
suka karaso suka gaishe su, Daddy ya dubi Miemie ya ce
"Mamana mutumiyar taki taci abinci kuwa?."
Aunty ta ce
"Wani abincin cake da yogurt ba tana da abincin da ya wuce su ne."
kai Feeryal ta langwab'e ta ce
"Naci tuwo fa Daddy ko Miemie."
Miemie tayi murmushi ta ce
"Taci Daddy tare ma muka ci."
"Yauwa ko ke fa gara dai a rika had'awa da mai nauyin, idan iska ya taso kinyi nauyi bazai iya kada ke ba."
cewar Daddy cikin zolaya.
dariya duk sukayi.
Daddy ya mike ya nufi bedroom ya na cewa
"To sai da safen ku."
zama sukayi suka bud'e sabon hira, har wajen karfe goma kafin Miemie ta yi musu sallama ta tafi.
Feeryal ma ta mike dan bacci ne cike a idanunta ta shige bedroom d'in ta.
Aunty ta je ta kulle kofar parlour kana ta dawo ta kashe TV sannan ta rage wutan parlour ta shige d'aki.
Ta taras da Daddy ya yi nisa a baccin sa, ta rage kayan jikinta ta sa na bacci kana ta shige bayi ta d'auri al'wala ta fito ta haye gadon itama ta kwanta gefen sa bayan tayi addu'a.
wani irin zabura Daddy ya yi ya mike zaune tare da fad'in
"Innailaihirraji'un!."
ya dafe kirjinsa jikinsa na cirawa.
a razane Aunty ta mike ta ruko shi tana fad'in
"Subhanallahi ya ya dai Daddy me ya faru bakayi addu'a bane ka kwanta."
kai ya girguza mata yana sauke numfarfashi tare da share gumin da ya karyo masa.
gaba d'aya Aunty ta rud'e a 'yan kwanakin nan ta lura a duk sanda ya kwanta haka zai farka a birkice.
tsawon shekaru ashirin da d'ori bayan auren su ya yi ta fama da irin wannan matsalar wacce damuwar haka takai ga tab'a masa lafiyar zuciya,
a wancan lokacin bayan auren su da wata biyar yasoma irin wannan mummunar mafarkin,
sai da ya shari shekaru goma yana fama da matsalar,
da taimakon Allah da taimakon addu'o'in da Aunty take tayashi yasami sassaucin lamarin,
damuwa da irin wahalar da yake sha idan ya kwanta bacci,
ta kai ga tab'a masa lafiyar zuciya, da har gobe yake shan magani.
sai gashiga a 'yan kwanakin nan abun ya dawo yanzu ba bu dare babu rana daga zaran ya kwanta bacci zai farka a firgice.
Ganin yadda gaba d'aya hankalin Aunty ya tashi, a hankali ya kwantar da kansa jikin kafad'ar ta yana sauke numfashi.
cikin shiga damuwa sosai Aunty ta ce
"Daddy tashi kayi al'wala muyi sallah babu abin da yafi karfin Allah babu abin da zai faru da yardar Allah."
Tarika karfafashi har ya mike yaje ya d'auro al'wala,
yafito ya taras har ta shinfid'a musu sallaya ta sa hijabi tana tsaye tana jiran sa.
shi ya jasu sallar suna idarwa taje ta d'auko musu Alkur'ani.
sun jima sosai suna karatu cikin suratul BAQARA, sai da ta tabbatar da nusuwa tare da shi,
har yana karatun yana gyangyad'i,
ta gyara ta mike kafafunta ta ce
"Kwanta Daddy."
ya mike kan sallayar yayi pillow da kafarta.
a hankali take karatun cikin kasa da murya tana yi tana shafa kansa, nan da nan bacci ya yi gaba da shi.
ya yi bacci abadan kafin itama ta soma lumshe ido. ta rufe kur'anin kana ta jingina bayan da jikin gado a haka bacci ya d'auketa a zaune.
Har sai kusan asuba ya farka ya ganta zaune tana bacci.
kauna da tausayin ta suka dad'a shigarsa, ya mike ya ciccib'eta ya d'aurata a kan gado,
yana ajeta ta bud'e ido.
murmushi tayi masa cikin muryar bacci ta ce
"Daddy ashe da sauran ka har yanzu tun da ka iya d'aukata."
kumatun ta ya ja ya na fad'in
"Tun da ina da ke kam tsufa bata isa ta matso ni ba."
murmushi tayi masa ta gyara kwanciyar ta.
shiko ya shige bayi ya d'auro al'wala,
yafito ya haye sallaya yasoma gudanar da nafilfili.
sai da aka kira sallar asuba kafin ya tashe ta shikuma ya wuce masallaci.
Aunty na idar da sallah ta je ta tada Feeryal kafin ta koma tacigaba da adhkar.
Feeryal ko bayan ta idar da salla da karatun alkur'ani tayi kamar yanda kullum Aunty ke umurtar ta da tayi, tana shafa addu'a ta haye gado ta koma baccin ta.
ba ita ta farka ba sai wuraren karfe 11 da rabi.
Bayan tayi wanka ta shirya cikin doguwar rigar atamfa da ta amshi jikin ta.
ta fito ta wuce dinning ta tarar da Aunty a gun ta tanadar mata abin kaunar ta wato cake da yogurt.
ta bayan kujerar Aunty ta zo ta kwantar da kanta gefen kafad'ar ta cikin siririyar muryarta ta ce
"Ina kwana Ammie na."
Aunty ta shafa gefen fuskarta ta ce
"Lafiya lau 'yammatan Ammie antashi lafiya ya lalaci,
a rage lalacin nan gobe ke zakiyi mana breakfast idan Allah ya kaimu, yau ma tare zamu shiga kitchen anjima."
"To Ammie."
ta fad'a tana mikewa a jikin ta taja kujera ta zauna.